Hausa NovelsYarima Suhail Hausa Novel

Yarima Suhail 60

Sponsored Links

AGE* 6⃣0⃣

Ummi cigaba tayi da cewa Zarah za6ina ce ni da mahaifinku mu mukasa yarima ya aureta saboda tunda sukayi aure da sumayya baida kwanciyar hankali, bai ta6a zuwa yakawo min k’orafiba koda sau d’aya, gudun kar d’anmu yashiga cikin wani yanayi yasa ni da mahaifinku muka had’asa aure da zarah batare da kowa ya san mune silar aurenba sai yanzu da ku kukasani.

Su rahma ido suka zuba ma mahaifiyar tasu suna kallonta cike da mamaki,
Nan ummi tacigaba da cewa kuma zarah tana zaune da yarima tsakani ga Allah na yarda da tarbiyarta kuma da kuke maganar ko magani tayi masa, ko d’aya ba haka bane.
mace zata iya mallakar namiji ta hanyar kulawa da yi masa duk abinda kikasan yana so dan haka nima nafi tunani ta haka zarah tasamu fada sosai a wajen suhail.
Hawayene yacigaba da fita daga idanun ummi girgiza kai ummi tayi tace burina duk inda d’ana yake sukasance suna cikin k’oshin lafiya shi da matarsa.

Su Husna jikin ummi suka fad’a suna kuka cike da tausayin d’an uwan nasu.

 

Sultan Ahmad koda suka fito daga fada kallon d’an uwan nasa yayi cike da jin kunyan abinda yarima ya aikata ma d’iyarsa, cike da damuwa yabud’e baki zaiyi magana nan sultan abbas yatari numfashinsa yace kar kace komai yaya indai akan mutuwar auren sumayya ne nasan wani abu tayi ma d’ana saisa ya yanke mata wannan hukuncin kuma dan memartaba yana cikin 6acin rai bai tsaya yasaurari ta bakinsaba saisa abun yakasance haka yanzu dai addu’a zamu cigaba da yi masa duk inda yakasance Allah yatsare mana shi, kar kasa komai a ranka yayana zumuncin mu mai d’aurewane har k’arshen rayuwarmu tun bamu mallaki ‘ya’ya da mataba muke tare taya zasuzo a yanzu kayi tunanin zasu shiga tsakaninmu?

Sultan Ahmad jinjina kai yayi cike da jin dad’in kalaman d’an uwan nasa yace nagode sosai abbas samun d’an uwa irinka sai antona a fad’in duniyarnan
Murmushi sultan Abbas yayi yace kar kadamu ai duk a wajenka nakoyi wannan halayyar.

Haka suka rabu kowa yanufi part d’insa cike da k’aunar d’an uwansa.

Sultan Ahmad koda yashiga yatarar da su sultana bilkisu zaune suna kuka, tsayawa yayi daga bakin k’ofa yana kallonsu yana jin wani irin k’unci a ransa, ganinsa yasa ummi tataso cikin kuka tafad’a jikinsa tace dadyn suhail yanzu shikenan na rasa d’ana bana k’ara ganinsa?

Sultan Ahmad janyeta yayi daga jikinsa yaje yazaunar da ita sannan shima yazauna a gefenta, cike da k’warin gwiwa yace bilkisu ke kanki kinsan abinda suhail ya aikata bai kyautaba kiduba kiga d’iyar d’an uwana jininsa yayi ma saki d’aid’aya har ukku, har yana ik’irarin cewa ta haramta ma kansa sumayya, na d’auka yarima yana da tunani koma me sumayya ta aikata masa ai baidace yaimata saki ukku ba, toh taya kike tunanin abinda ya aikata bazai 6ata mana rai ba?

Sultana bilkisu tsagaitawa tayi daga kukan da take tace nasan haka ranka yadad’e ammah hukuncin da aka yanke ma suhail ya yi masa tsauri dayawa yanzu bamusan yanayin da zai shigaba ga matarsa da ciki ina zasuje wa suka sani?

Rik’o hannunta sultan Ahmad yayi yace bilkisu kikwantar da hankalinki suhail fa ba yaro bane insha Allahu duk inda zasu kasance suna cikin k’oshin lafiya addu’a kawai zamucigaba da yi har Allah yataimakemu memartaba yasafko daga fushin da yake insha Allahu suhail zai dawo yayi rayuwa cikin danginsa.

Murmushin jin dad’i ummi tayi tace hakane ranka yadad’e Allah yakawo mana ranar da hakan zai kasance da nafi kowa farin ciki,

Su rahma da suke gefe suna sauraren iyayen nasu cike da jin dad’in maganar da mahaifinsu yayi sukace Allah dai yatsare mana su.

Ameen sultan Ahmad yace tare da mik’ewa yawuce part d’insa.

 

A 6angaren su sumayya koda suka isa 6angaren iyayenta tusa sultana sadiya tayi a gaba tana kuka har da mirgina lallashinta sultana sadiya take ammah kamar k’ara tunzurata take, sumayya kuka take sosai tana cewa dole sai ta koma d’akinta wlh bazata ta6a yadda ba zarah asiri tayi tarabasu da yarima.

Daga k’arshe jugum sultana sadiya tayi tana sauraren d’iyartata, suna cikin haka sai ga sultan abbas ya shigo ganin sumayya kwance k’asa tana mirgina yasa yadaka mata tsawa yace ke menene haka kikeyi?

Sumayya tashi tayi a zaune tana cigaba da kukanta.
Sultana sadiya ce tayi k’arfin halin cewa yauwa gama kanan dan Allah kazo kataimaka asan yadda za’ayi sumayya takoma d’akinta wlh tana son mijinta sosai.

Murmushi sultan abbas yayi wanda yafi kuka ciwo sannan yace sadiya kenan ai ban d’auka zaki mance da saki nawa bane suhail yayi mata,

Ke kuma,,yanuna sumayya da yatsa yace garin haukanki kinje kin kashe aurenki na tabbata suhail ba zai ta6a yimiki saki ukku ba batare da wani k’wak’waran daliliba, toh yanzu wa gari yawaya? Sai kizo kujera da mahaifiyartaki kiyi ta zaman gida, babban bak’in cikina ma da kikayi silar raba yarima da family d’insa.

Cikin 6acin rai sultana sadiya tace haba Alhaji wannan wane irin cin mutuncine tun a gaban memartaba kake ta kware ma d’iyarka baya toh inaso kasani hannunka baya ru6ewa kacire kayar kuma ni nasan sumayya ba abinda zatayi ma yarima wanda zaisa yaimata wannan saki haka saidai idan wacchan munafukar matsiyaciyar yarinyarce tashiga tsakaninsu.

Dakata ke banson shashanci nalura kamar ke kike goya ma yarinyar nan baya tana yadda takeso dan haka kukiyayeni ko gabad’ayanku insa6a muku, wlh kikiyayi lokacin da zakiji kunya dan naga kina d’orema k’arya gindi, ni a wajena da yarima da sumayya duk d’ayane dan dukansu ‘ya’yanane bana goyon bayan kowa sai gaskiya dan haka gatanan tayi ta zaman gidan zata gane ai idan iyaye da miji d’ayane, duk dai inda mace takasance komai gatanta toh gidan miji shine kwanciyar hankalinta,
Sannan ke sumayya ina k’ara tunatar da ke saki ukku ne yarima yaimiki bakida ko sauran igiya d’aya dan haka dole yanzu kicire tunanin komawa gidansa dan yariga da yayi miki nisa,,,,sultan abbas yana kaiwa nan a zancensa yawuce yashige part d’insa cike da 6acin rai.

Sultana sadiya da kallo tabisa dan gabad’aya ya kashe mata baki ga takaici da yacikata, cikin kuka sumayya tace ummah yanzu shikenan na rasa yarima ya zanyi da rayuwata.

Cikin 6acin rai sultana sadiya tace ai ga irintanan ke kibar ganin ina goyon bayanki kema ai kina da naki laifin a ciki yanzu gashinan kinja mijina nima yad’au fushi da ni yadda kika kaso aurenki toh nima bazakiyi silar mutuwar nawaba dan haka dole kihak’ura kicire suhail a ranki tunda bashikad’ai bane namiji a duniyar mutumin ma da baya k’aunarki baisan darajarkiba toh miye amfanin zama da shi hak’urin dai zakiyi Allah yamusanya miki da mafi alkhairi.

Sumayya ganin mahaifiyarta kamar itama tana nema takware mata baya dan haka tamik’e tawuce tashige room d’inta tana kuka.

________________

Yarima koda yafarka baccin da suka koma bayan sallar asuba kallon agogo yayi ganin har 11 ta yi yasa yajanye zarah daga jikinsa, zaune yayi yana k’arema fuskarta kallo cike da sonta dan yanzu ya tabbatar ma kansa yana son zarah, janye gashin da yasafko wajen idonta yayi nan yaduk’a yakai mata peck a goshi, ahankali zarah take bud’e idanunta nan tasafkesu akan fuskar yarima, murmushi tasakar masa tare da rik’o hannunsa d’aya.

Shima murmushin yamaida mata yace baby kin tashi?
Mik’a zarah tayi tace jikina ciwo yakemin, jan d’an k’aramin bakinta yarima yayi yace toh muje inmiki wanka.

Turo baki zarah tayi tace saidai kad’aukeni dan ban iya tashi.

Hmm shikenan yadda kikeso haka za’ayi ai nasan nine nagajiyar da ke d’in,,yafad’i hakan tare da d’aura hannunsa saman cikinta yana shafa.

Ido zarah tazuba ma kyakkyawar fuskarsa bata ko kyaftawa, hura mata ido yarima yayi nan talumshe idanunta cike da jin kunya.

Murmushi yayi tare da d’aura kansa saman k’irjinta yace baby kallon fa?

Zarah batare da ta bud’e idanuntaba tace ni ba kai nake kallo ba,

Bakinsa yakai yad’an ciji le6enta har saida tad’anyi k’ara sannan yace toh wa kike kallo.

Rik’e le6enta tayi kamar zatayi kuka Sannan tace ni mijina na kallah ko laifine dan na kallesa?

Batare da ya bata amsaba yad’auketa yanufi toilet da ita atare sukayi wanka sannan suka fito suna rungume da juna, tana tsaye gaban dreesing mirror tana kwalliya nan yarima yai mata tsaye yana kallon kwalliyarta kashe mashi ido tayi tace nayi kyau?
Ta6e baki yarima yayi yace ko d’aya bakiyi kyauba,
Haushine yakama zarah nan ta6ata fuska tace Allah a’a
K’unshe dariyarsa yayi yace ammah ai kinsan nafiki kyau ko?
Harararsa tayi cikin wasa sannan tace saidai muzo d’aya ammah bakafiniba.

Murmushi yarima yayi tare da rungumota jikinsa yace ban yardaba nan yajanyo wayarsa yai musu selfie.

Zarah zame jikinta tayi tanufi wajen wardrobe nan tad’auko wata gown cikin kayan da yarima yasiyo mata tasaka nan tanad’e gashinta kamar gammo sannan tayi rolling d’in d’an k’aramin veil d’in kayan nan tayi gwanin kyau, juyowa tayi takalli yarima da yatsareta da ido tace toh yanzu ya kaganni?

Murmushi yayi yace har yanzu dai ina akan bakana, dariya tayi nan tamatso yacigaba da yi musu pic’s saida sukayi kusan kala ashirin ganin baida niyar dainawa yasa tajasa suka fito main parlour nan suka tarar da mu’az da matarsa nan suka zauna suka gaisa daganan suka wuce dining gabad’ayansu suna breakfast.
Zarah da yarima saidai kallon love suke aika ma junansu mu’az da jamila suna lura da su saidai suyi murmushi ahaka har suka gama breakfast d’in nan suka hau yin hira, yarima kallon mu’az yayi yace abokina inaso insamu gida insiya dan gaskiya ba zan iya cigaba da zama a nan ba saboda da takura muzauna muku nan zamu d’aura muku nauyi nikuma banason hakan indai kana ganin ba matsala toh kasanya min cigiyar gida.

Cike da damuwa Dr mu’az yace ranka yadad’e banta6a tunanin jin haka daga garekaba da kai da kaya ai duk mallakar wuyane, idan har kai ka mance abinda kayimin toh ni ban manceba kuma bana iya mancewa, wlh yarima zan iya sadaukar da duk abinda namallaka a gareka dan ka fiye min komai dan Allah kataimaka kucigaba da zama da mu Indai akwai abinda mukeyi muku wanda bakuso kusanar da mu insha Allahu zamu daina, gyad’a kai jamila tayi tace eh wlh zamu daina dan muna jin dad’in zamanku a tare da mu.

Yarima murmushi yayi yace kar kudamu ba wai saboda wani abu nakeson barin gidanba kawai dai dan kar mushiga hak’inku ne.

Girgiza kai mu’az yayi yace kar Allah yakawo ranar da zanji wani abu game da zamanmu tare nidai ka amince mucigaba da zama wlh munajin dad’in zama tare da ku.

Yarima kallon zarah yayi nan tasakar mashi murmushi, kallonsa yamaida ga mu’az yace shikenan na amince ammah ban d’aukar maka alk’awaliba.
Murmushin jin dad’i mu’az da matarsa sukayi nan sukaima yarima godia daganan suka cigaba da hira koda rabin hirar mu’az da matarsa sai zarah ne sukeyi dan shi yarima da ido yake binsu saidai yayi murmushinsa mai tsada.

Sun dad’e suna hirar sannan Dr mu’az da yarima suka tashi suka fita inda zarah da jamila suka shiga kitchen dan suhad’a musu lunch, a tare sukayi komai duk yadda jamila taso zarah tabarta tayi ita kad’ai ammah zarah k’iyawa tayi saida aka gama komai tare da ita sannan suka kai saman dining suka jera daga nan kowa yawuce part d’insa dan yashirya jikinsa.

Koda yarima yadawo Zarah taimaka masa tayi yai wanka yashirya bayan sungama cin abinci part d’insu suka dawo nan tayi d’aid’aya saman cinyarsa tana zuba masa shagwa6a yana biye mata a ranar haka suka kasance takasa tatsare indai ba masallaci yarima zaijeba toh suna manne har dare yayi, taje tahad’o musu coffee a one cup a tare sukasha sannan sukaje sukayi wanka suka kwanta saida sukayi ‘yan wasanni batare da sunyi making sex ba sannan sukayi bacci kowa yana jin d’an uwansa sosai a cikin ransa.

 

*BAYAN SATI ‘DAYA*

Dr mu’az ne da yarima zaune a parlour suna hira, kallon yarima yayi yace yauwa prince ina zuwa,
d’aga masa kai kawai yarima yayi batare da yayi magana ba nan Dr mu’az yamik’e yanufi part d’insu,

Bayan minti biyu yafito rik’e da wasu files, kujerar da yarima yake zaune yaje yazauna, kallon yarima yayi suka fuskanci juna sannan yace prince dan Allah wani taimako ne nakeso kayi min.

Kallonsa yarima yayi yace ina jinka Indai baifi k’arfinaba toh insha Allahu zanyi maka.

Murmushi Dr mu’az yayi yace tabbas baifi k’arfinkaba, nan yafiddo files d’in yamik’a ma yarima yace gashi ammah kayi hak’uri da karambanin da nayi maka muna buk’atarkane a hospital d’inmu.

Yarima dubawa yayi yaga upper ce ta aiki aka basa har da babban matsayi an nad’asa head of department d’in surgeon.

Girgiza kai yarima yayi yace gaskiya kayi hak’uri ba zan iyaba kaima sanin kankane ina da hospital d’ina.

Marairaicewa Dr mu’az yayi yace nasan da haka ammah dan Allah kataimaka ka amince ko yayane kasa albarka a cikin aikin nan kar kak’i amincewa dan muna buk’atar babban surgeon kamarka.

yarima shuru yayi kamar yana nazari sannan yace shikenan zanyi tunani akai.

Cikin jin dad’i Dr mu’az yace Allah yasa inji alkhairi.

Bayan yarima yadawo part d’insu kwance yake saman 3 seater ya yi matashin kai da hannuwansa kansa yana kallon ceiling,

Fitowar zarah kenan daga bedroom rik’e da apple tana ci, tsaye tayi tana kallon yarima da kwata-kwata batama san lokacin da yashigoba dan duk atunaninta bai dawoba.

Takowa tayi ta iso inda yake janye kansa tayi tazauna sannan tamaida kan nasa saman cinyarta, yarima lumshe idanunsa yayi.

shafa sumar kansa tayi tace ashe ka dawo ban saniba.

Murmushi yarima yayi yace uhm ban dad’e da dawowaba,
duk’o da kanta tayi takaimashi peck a saman idonsa da yake lumshe, ahankali yabud’e idanunsa nan suka sakar ma juna murmushi, d’age rigarta yayi yayi kissing d’in cikinta sannan yace ina fatana kuna lafiya keda babyna.

Cike da tsokana zarah tace lafiya lou muke prince saidai missing d’inka da mukeyi.

Shafa cikinta yashiga yi yace nima nayi missing d’inku sosai yanzu muje ciki inga in dagaske kunyi missing d’ina.

Dariya zarah tayi tace nak’i wayon naka babu inda zanje.

Mik’ewa yarima yayi yad’auketa yanufi bedroom da ita tana wuntsila k’afa bai direta a ko’inaba sai saman gado, zarah shirin safka take nan yarima yarik’ota yace toh sarkin tsoro ni ba abinda zanyi miki magana ce nakeso muyi.

gyara zamanta tayi tafuskacesa tana jira taji abinda zaice mata.

Yarima janye idanunsa yayi daga kallonta yayi shuru har na kusan minti ukku sannan yakwashe yadda sukayi da Dr mu’az yafad’a mata.

Zarah kasa 6oye farin cikinta tayi nan tashiga washe baki, kallonta yarima yayi yace toh ya kike gani?

Cikin jin dad’i tace wlh nima na goyi bayan hakan kaga kaima zaka ji dad’i kuma taimakone Allah zai baka lada dan irin wannan aikin naku duk abinda za’a ba mutum baza’a ta6a biyansaba ladarku tana wajen Allah.

Murmushi yarima yayi yace hakane shikenan tunda kin amince toh nima na amince.

cikin jin dad’i tarungumesa tace nagode sosai my soulmate Allah yabarmin kai ni kad’ai.

Dariya yarima yayi yace toh Allah yasa,

‘Dago kai zarah tayi takallesa tace ashe ka iya dariya haka gaskiya tana yi maka kyau saidai kai bakacika yin dariyaba murmushinma kafin kayi sai ansha wuya.

Jan hancinta yarima yayi yace yau kuma tsokanata akeji?

Murmushi zarah tayi tace ba tsokana bace gaskiya ce nafad’a dan ranar da nafara ganinka lokacin da kukazo islamiyarmu ranar da muke walima saida nakusan rikicewa dan ka burgeni sosai saidai a lokacin fuskarka a d’aure take.

Murmushi yarima yayi yace kedai kin cika tsokana nidai yanzu tashi muje muyi wanka mukwanta dan ni yau agajiye nake ga bacci da nakeji.

Mik’ewa zarah tayi tace angama ranka yadad’e, nan suka cire kayansu sukaje sukayi wanka bayan sun fito shiryawa sukayi cikin kayan baccinsu sannan sukabi lafiyar gado suka kwanta.

 

Wanshe kare koda yarima yaje ma mu’az da batun amincewarsa sosai mu’az yai murna,

bayan kwana biyu yarima motarsa yasiya maikyau da tsada sannan yafara zuwa wajen aikin.

Sosai ma’aikatan asibitin suke girmamasa musamman ma da sukasan matsayinsa da kuma matakin karatunsa, kamar dai yadda yake baya shiga harkar kowa toh nan ma haka hidimar gabansa kawai yakeyi.

Sosai sukejin dad’in aiki da shi musamman ma da sukaga k’wararrene sosai a 6angaren theatre.

 

Bayan kwana biyu
Zarah kwance take saman gadonsu tunanin ‘yan gidansu kawai take dan tasan dole sai sun nemi wayarta, tana cikin tunanin batasan lokacin da yarima yashigoba saidai jin mutum tayi gefenta, murmushi tasakar masa tare da cewa sannu da zuwa ashe ka dawo.

Shima murmushin yayi sannan yace ai daman bazakiji dawowataba tunda kin tsunduma kogon tunani wai ma tunanin me kikeyi haka?

Ajiyar zuciya Zarah tasafke sannan tace tunanin su mama nake nasan zasuyita neman layina bazasu samuba,,,tak’arashe maganar kamar zatayi kuka,

Yarima kallonta yayi yace kar kidamu ai sunsan dai kina cikin k’oshin lafiya zan kira miki su wani lokacin kugaisa.

‘Daga kai Zarah tayi cike da gamsuwa da maganar yarima, jikinta yarima yakwanta tare da tura hannuwansa cikin rigarta yana cakud’ata
Ganin yana shirin nemanta yasa tazame jikinta takoma parlour dan yanzu gabad’aya ji take batason yarima yana kusantarta saboda sai takwana jikinta yana ciwo ga yawan amai da tashin zuciya musamman yanzu da cikinta yafara yi mata nauyi, ammah indai wassani zaiyi da ita bata damuwa saidai tasan halin gogan nata dawuya ya iya tsayawa iya romancing.
Ganin ta gudu yasa yarima yashareta yai kwanciyarsa dan ya lura kwana biyu haka take masa Indai zai nemeta toh sai tasan hanyar da tabi takubce masa.

 

 

_Comment_
*nd*
_Share_

 

 

_Sis Nerja’art✍_[5/3, 9:51 PM] Sis Naj Atu:

_*YARIMA SUHAIL*_

 

_*Written By~Sis Nerja’art*_

 

_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_

https://m.facebook.com/Intelligent-Writes-ASSO-294634797868361/

*INTELLIGENT WRITER’S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS CURDLES GIGGLES AND MARRIEGE THINK
*JUST GIVE US FOLLOW….*✔

_Aunty Aliyah Sharif bazan iya mancewa da ke ba akodayaushe kina raina dan haka kimatso kusa yau page nakine big Aunty, sai wanda kikaso zai karanta, jinjinar bangirma agareki _

 

Back to top button