Hausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 32

Sponsored Links

32
Tsit palon ya dauka kusan kowanne tsakanin dd babba da Bilal sun dauke wuta da mamaki tareda firgicin zancen da Ababan ya zaro,

Bilal Kansa ya sauke cikin baqin ciki da damuwa Mai tsananin gaske tareda sanyin jiki sbd tin zuwansa duniya ko dd babba Bai taba fitowa Kai tsaye ya tinatar dashi ko shi din wayeba,
Iyayensa da suka haifesa dinma daga ranar da aka daura musu aure ko a tsakaninsu Basu sake tayar da zancen ba sbd umarni da qaqqafar rantsuwar da dd babba yayi Akai Amma ayau Rana tsaka Kai tsaye a gaban idon dd babban ga Wani Yana fadan maganar Kai tsaye batareda mutunta shi Bilal din ba.

Dd babba kuwa shiru yayi batareda iya cewa komaiba tsawon mintina kafin ya dago ya sakewa Ababa kallan tsaf na mintina,

Ayau Rana ta farko da Wani yake zaune gabansa ya fada maganar da zata iya sakawa yasa a batar dashi da labarinsa,
Ko a cikin familyn kaantes ba kowa ne ba yasan asalin Tayaya aka haifi Bilal din ba bayan shi da Kansa sai Mahaifin Bilal da mahaifiyarsa sai Dawood da Kuma kanin dadynsu Bilal din da matarsa.,

Bayan wainnan babu Wanda ya sani a familyn sai dangin mahaifiyar Bilal Suma kawunta da matarsa ne kawai suka sani Kuma kawun ya rasu matarsa da yayanta Kuma sun koma asalin garinsu sunbar Nan din gabaki Daya Wanda dd babba da Kansa ya Bata Abinda zatayi nesa dasu kada ta dawo har abada saidai Fatima takai musu ziyara sbd kawai kada ma zancen ya iya fita wataran ta hanyar matar kawun.

Tabbas Ababa yazo da zance Mai girma,
Idan ya fahimci zancensa da yanayin yanda ya isar da zancen cikeda sakon nufin
“Ko a karba yarsa da cikin itama ko ya fallasa zancen cikinta Dana uban cikinta.”

Kan Bilal ya Maida kallansa sbd a yanzu kam ya sake tabbatarda illar zamtowar Bilal cikin ahalin kaantes.

Basai dd ya fada ba Bilal da Kansa yasan wannan tinanin ne acikin zuciyar dd babba yanzu akansa Daman Kuma tin ba yanzu ba yasan da Hakan.

A Karo na farko bayan zancen dd babba ya Bude baki yacewa Ababa

“Yama kace sunanka na gaskia malam Ababa?

“Abubakar nake” Ababa ya fada Kai tsaye.

“Malam abubakar a ringa kulawa sosai da aibin harshe,
Maganar ‘yar ka Kuma kaje kawai zan sake nemanka.

Magana Ababa zaiyi ddn ya kira Abbakar Sam ko kalma Daya baa bari ya furta ba aka fice da dashi Yana waiwaye sbd Bai fahimci me Hakan ke nufi ba.

Ana fitowa dashi Abbakar ya sallamesa har gate din waje ya koma.

Gida ya nufa Yana shiga nazari saidai Kuma bazaiyi qasa a gwiwa ba zai tsaya tsayin Daka a maganarsa kokuma a mutu har liman.

Bilal kaante ranar yau na cikin ranakun dasuka wuce masa a baya na radadin zuciya sbd maganar Ababa ta sosa masa tabon Daya jima cikin rayuwarsa Yana dannewa,
Bayan tafiyar Ababa shi Kansa ya sosa masa maganar data sakasa rufe Kansa a part dinsa ya zubar da hawayen da suka dawo masa da ciwo da radadin zuciyar Daya jima da dannewa.

Haka damuwarsa tin ta yarinta Mikn ya dawo masa sabo fil baida Mai zaunawa kusa dashi ya sanyaya masa kaman baya da mahaifiyarsa da DD ke zaunawa gefensa su rungumesa.

Kaf ahalin gidan babu Wanda ya asan meyake faruwa sbd gargadin dd babba na kada ya sake kowa yasan da zancen.

Dad dinsa baisan Abinda yake faruwaba tsakanin dd babban da Bilal sbd ko a fuska baka Isa ka Gane akwai Wani abin ba a qasa.

A tinani da hukuncin dd babba so yke ya dakile zancen ya rufe batareda kowa ma ya san da wannan qaddarar ba Amma Kuma da alama Ababa bazai lanqwasu da sauki ba.

Ta bangare Daya Abbakar ya saka yayi masa bincike Mai zurfi akan Ababan da duka huldodinsa.

Karan farko ana gama sanar dashi waye Ababan ya fahimci Yana Hana Ababan Abinda yakeso zai Bata musu sunan Daya debo shekaru masu tsayin gaske Yana ginawa.

Yanada plans me kyau akan rayuwar jikokinsa Dan haka bayajin zai iya hada iri ko zuria da Ababa sbd a halayensa babu na gari to Amma idan har karban yarsa shine maslahar Hana fidda sirrin A kaantes suna yayan gaban fatiha zai sake dubawa ya Gani.

Sake kiran Ababa yayi wannan Karan dukiyar da yayi masa alqawarin Basa harta fita lissafi Amma Sam Ababan ya tsaya akan sai Bilal ya auri yarsa tinda idan an barsu da ‘yar baisan yanda zaiyi da ita ba.

Wannan Karan ran dd babban ya tsananta Baci Dan haka ya sauke fushinsa a sirrance kan Bilal ya dakatar dashi daga wasu hildodin ya hanasa ko fita daga kaantes din sbd lura da Bilal din zai iya sallamawa ya zabi yarinyar da ake maganar Wanda Hakan zai iya kawo tonan asirin maganar ga family dama duniya gabaki Daya.

Iyakance Bilal daga komai yasa Ababa qara kafewa sbd da alama dai waton ko Bilal din ya zabi sumayyah ba wasu dalolin arzkin zai samu daga gunsa ba tinda zaa iya dakatar dashi daga komai na dukiyar kaantes Dan haka ya sake tsayuwa akan raayin sai Bilal ya auri ‘yarsa kokuma yayi qara.

Akwai matakai da hanyoyin daukan mataki me kyau da sabaninsa da suke dashi akan irinsu Ababa Amma a zuciya da halin dd babban Yana dakatarwa ne sbd duba da yarinyar dake dauke da juna Biyun Wanda rayuwarta tabbas an Riga an lalata mata,
Sunada ‘yaya mata da jikoki Wanda ya tabbatarda idan aka cutatar da wannan yarinyar Allah zai iya jarabtarsu tinda ba kudi ko dubarar bace zasu tsare Maka yayanka daga Hakan,
Shi kuwa a duniyarsa da irin qaddarar Hakan ta samu ‘yayansa ko jikokinsa koma ahalinsa gaba Daya mata gwara Allah ya dauki ransa ya bar duniyar.

Ta bangare Daya Bilal ya qasqantar da Kansa a gaban dd babba ya rokesa akan yabarsa ya auri sumayyahn sbd Yana kaunarta har lokacin harma da duk Abinda zata haifa,

Yayi alqawarin zaiyi nesa da ita inda zasu Rena Abinda zata haifa batareda kowa yasan Tayaya suka haifesa ba,
Bazai taba barin sunan zuriarsa ta lalace ba sbd shi.

Da fari dd babba kasa karban wannan rokon yayi Amma ganin yanda Bilal yake qasqantar da Kai akan Hakan dakuma zaunawa da yayi ya duba tafiyar Bilal din zata ankarar da mutane a iya sani hakama Ababan Nan ba abin yarda bane matiqar suka barsa a Raye to zaa iya sanin gaskia Dan haka zai amince da auran yarinyar ta yanda zasu batar da zancen su Hana a fahimci ansamu wata qaruwar Bata hanyar aure ba daga baya zaisan yanda zaiyi da Ababa.
Saidai ya gindaya manyan sharuddan da daga Ababa har Bilal jiki na rawa suka amince aka bar maganar a rufe akan ana haihuwa zaa daura musu aure a rufe maganar haihuwar ta dawo kaantes.

******Amincewar dd babba yasa Ababa Jin duniyarsa gabaki Daya ta dawo sabuwa sbd farin ciki da samun biyan buqata cikin sauki,

Bilal ma samun Kansa yayi cikin samun kwanciyar hankali da nutsuwar zuciya duk da Sam dd babba ya hanasa zuwa ganinta sbd kada aga Yana zuwa gidan Amma suna magana a waya duk bayan kwana biyu Shima da wayar Ababa sbd Ababan ya mayar masa da tasa wayar Daya bata.

Ta bangare Daya Kuma bakin aljihun kaantes aka budewa Ababan na kulawa da sumayyah wadda basusan meyake faruwa ba Dan kuwa wahalarsu sai Abinda ya qaru ba sauki.

*****Zuwa yanzu rayuwa ta sake yiwa su benazir wahala sbd rashin isashen hutu da yunwa harma da karatun benazir din Dan ita sumayyah tini aka watsar da nata karatun.

Gabaki dayansu sun bushe sun koma kaman wainda ke rayuwa a cikin Sahara sbd daidaicewar yunwa da wahala,

Sumayyah kuwa a yanzu cikinta ne kawai mai tsoka a jikinta,

Komai na masu ciki Tin daga cima har hutu da magani Bata taba samun ko Daya ba tinda ta baro asibiti.

Hande a yanzu tafi koyaushe tsangwamarsu sbd ita kam har lokacin tsanar cikin takeyi harma dasu gabaki Daya Dan ganin takeyi sun haukatar mata da Ababa sbd yanzu duk ya sauya babu Wanda yake Gane Kansa.

***A haka suka ringa gangarawa har cikin ya shiga wata Tara Wanda shigarsa ya saka rayuka da dama shiga tashin hankali da fargaba,

Ababa hankalinsa a yanzu data shiga wata Tara ya tashi cikin fargaban me zaa haifa hakama da fargaba Mai tsanani kan a haihu lafiya ba tareda matsalar komaiba Dan a yanzu haihuwar itace zata tabbatarda hayewarsa zuwa Ababansa ko faduwarsa zuwa Nobaba.
AFUWAN BA YAWA.
##MAMUH#
#AMNAH
#BENAZIR KAANTE
#DD KAANTE
#ABABA
#ZAFIN KAI
#MAMUHGEE

*_Arewabooks@Mamuhgee_*

Back to top button