Hausa NovelsNi da Patient Dina Hausa Novel

Ni da Patient Dina Book 1 Page 18

Sponsored Links

Page 1️⃣8️⃣

 

 

“Gaskiya nikam yau senayi jinyar kafata ” FANAN tagama magana tana mamatsa kafanta din datakeji Yana mata zugi tsabar gudun dasu kasha, uhmmm Amira ce tamike tana fadin “gwara daku nide bari inkoma gida kar hajiya taga na Dade tayi tunanin Kona tafine” saka hijab dinta tayi tamusu sallama ta tafi sukuma suka cigaba da hiransu.

 

Driving yakeyi Yana Dan duba agogon Rolex Dake hannunshi ganin dayayi 11:00 saura ne yasa yadanyi tsaki ya tsani bata lokaci saboda komai nasa akan time yakeyi kowani lokaci Yana basa mahimmancisa , gashi meeting zetafi haduwan dayayi da FANAN ne tabata mishi lokaci. Abakin gate din Government house yatsaya Yana horn ga sojoji awaje suna aikinsu sanin sunsan shidin wayene shisa Basuyi gigin tareshi ba cikin sauri gate man yabude yashiga packing space yaje yayi packing yafito Yana sanye da suit ruwan toka ga bakin glass manne a face dinshi fuskan nan a murtuke kamar Wanda aka aikowa da sakon mutuwa Yana tunkaro bakin meeting room din me gadin wajan yabude mishi yashiga , samunsu yayi gaba Daya sungama hallara shi kadai suke Jira ko kallonsu beyiba yasamu waje yazauna kallon me girma gomna yayi ciki ciki yace ” barka da warhaka excellency” fuska asake yace ” barka de my son ” be amsa Shiba yaci gaba da danna wayarsa cikin bacin Rai alhaji lamido yace ” lallai yaro ka girma tabbas kayi girman da bazaka iya gaidamu ba saboda karenamu kana ganin tsayinka yazo Dede da namu” kallonsa azaad yayi kafin yayi killer smile dinshi Wanda aduk lokacin dayayi irin wannan murmushin bakin ciki ne yake kamasu suji kamar su shakeshi yamutu kowama yahuta. Harzuka alhaji lamido yayi zesake magana alhaji sambo daurayi yayi saurin rikeshi Yana fadin ” kaikuwa mezesa katsaya kana kula Dan cikinka” dukansu kallonshi sukeyi shikuma ko ajikinshi duba time yayi kafin yadago calmly cikin kwanciyar hankali yafara magana” kunci 40mint acikin 2hours din da kuka bukata awajena nazo Kuma naga kamar you have nothing to say idan babu nizan wuce yanzu saboda inada Abubuwa masu mahimmanci dazanyi ” yagama maganar sa Yana cigaba da danna wayarsa gyaran murya me girma gomna yayi kafin yabude taro da adduah yamaida kallonsa kan AZAAD dayayi relax yana pressing phone dinshi sannan yace “AZAAD MUHAMMAD MAINASARA Ina bukatar hankalinka anan ” yayi maganar Yana zuba mishi ido ajiye wayar yayi yadaura Daya kan Daya yazuba musu ido. Sauran kuwa zuciyarsu ne take tafarfasa tsananin tsanan azaad ne yabayyana afuskansu , excellency ne ya gyara mic din gabanshi yacigaba da magana” wato dalilin da yasa aka hada wannan Taron shine asamo masalaha tsakaninka da Yan uwanka Yan kasuwa domin kuwa sunkawo kararka kan cewa kana son tarwatsa musu kasuwancin su ta hanyar sassauto da farashin kayan company ka komai karage masa kudi tayanda ake kokarin Dena siyan kaya a company’s su saboda arhan da naka yayi ko zaka iya mana dalilin dayasa kake haka azaad Muhammad ”

Bayan yagama Jin bayanin da gomna yayi ne yasa yayi yar murmushi dama yasan zaa rina domin kuwa wannan shine karo na 7 sunasanyi zama dashi Amma yanuna musu bayida lokacin haka shisaka suka kawo karanshi wajan excellency, zamanshi yagyara kafin ya seta mic din da kyau yafara magana cikin Isa da mulki ” da farko de danasan akan haka aka kirani nan wajan Dan abatamin lokaci to bazanzo ba, na biyu Kuma karata da kuka kawo Kuma akan yanda nake gudanar da kasuwancina wannan bekamata yazama matsalarku ba yanda nagadama nayi niyya haka zansiyarda kayana Kuma kuje kusiyar danaku aduk farashin dakukeso , na uku ko kyauta naraba kayan banida matsala da hakan saboda riba sam baya gabana ni inada kudaden dazan iya barin kayan company na ata rabawa talakawa har natsawon shekara 10 ko fiyeda hakan” yagama maganarshi Yana gyara necktie din wuyanshi kafin yaci gaba da danna wayarsa. Tunda yafara magana alhaji Ibrahim tijjani (mahaifi agun aneesa) ya kafeshi da ido Yana aiyana ta idan ze bullo mishi .
Excellency ya jinjina da taurin Kai dakuma ranshin tsoro na azaad saboda yasan irin hatsarin dasu alhaji Ibrahim tijjani da alhaji sambo daurayi suke dashi Amma shi kwata kwata bayajin tsoron haka, ajiyar zuciya yayi kafin yace ” azaad baka mana kwakwaran bayanin dazamu gamsu dashi ba” cikin kakkausar murya yace” babu wani bayanin dazanwa wani anan saboda you don’t owe me any explanation” afusace alhaji sambo yamike yabugi table din yace ” kai karamin kwaro kayi kadan katsaya kana juyamu yaushe kazo duniyar to wallahi tallahi kabi asannu karkasa rayuwarka ahadari domin bakasan dasuwa kake jaba ” yagama magana Yana diri kafin alh lamido yace” ku kyaleshi de mugani ko tusa ze hura wuta ” dukansu dasuke magana beko dago kansa ba balle susa ran zetanka musu ba, girgiza Kai alh Ibrahim tijjani yayi yace” azaad yata tana matukar sanka bazanyi abinda itama zatasha wahala ba Amma kasani kayi adduah allah yasa kana Daya daga cikin masu tsawon Rai sirkina” dariya meyar sauti yayi Wanda yakara masa matukar kyau mikewa yayi yayi da murmushi akan fuskanshi yadauki wayarsa kafin yace” meyi baya fada ai zanfijin dadin ku aiwatar da abinda kuke fada Amma kuntsaya kunata haushi kamar wasu kana nan karnuka zanso kununamin ku Yan halak ne ” yakarasa Yana tafiya alh lamido ne cikin daga murya yace “Kai azaaaaaaaad dawani irin action azaad yajuya yadaura yatsanshi Daya akan libs dinsa shhhhhhhhhhhhhhh sannan yace ” idan Ina waje baa daga murya ko kuma dass ya kyasta yatsunshi guda biyu suka bada sauti” gaba Dayansu shuru sukayi kamar wayanda ruwa yashanye su, fita yayi daga meeting room din ya fisgi motar shi Yana driving Yana murmushin da shikadai yasan maanarshi , kamar ance yakalli mirror motar yaga katuwar trailer tabiyoshi da mugun gudu shafa sajen fuskanshi yayi yasake wata kayittaciyar murmushi Kara speed yayi Yana gudu kamar Wanda zefire sama drivers din trailer ganin dasukayi yabacewa ganinsu yasa suka packer suna tunanin ta Ina zasu samoshi fitowa sukayi daga motar suna Kunna sigari kamar daga sama dayan yaji anyi sama dashi anbugashi dakasa taka ruwan cikinsa azaad yayi dakarfasa dayan da gudu yazo yacakumeshi tabaya juyawa yayi yakai mishi kyakyawar naushi afuska nan take yafadi kasa hancinshi da bakinsa na zubar da jini komawa kan na farkon yayi yamishi mugun duka kafin yakarya mishi kafan hagu da hannun dama Shima dayan hakan ya mishi Sannan yazauna akan wata dutse yadauki wayarsa acikin aljihu yakira police station sukazo suka kwashesu shikuma yakoma gida,. Yanda abun yafaru bayan yakara gudun speed din seda yatabbatar da yamusu Nisan dabazasuyi tunanin binshi ba shikuma yayi xagaye yakoma bayansu can nesa ya hangosu suna busa sigari anan yayi packing motar shi yakaraso gunsu batare dasun sani ba.

 

Adamawa Yola

 

Alhaji badamasi me ruwa ne zaune shida ahalinshi afalo suna hira lura yayi da nusaiba dataketa bata fuska yasan abinda yasata hakan Dan taba Madina yayi yace kalli yarki tabe Baki tayi kafin tace ” to alhaji aikasan abinda kakeso Amma kahanata yazatayi to ” takarasa magana tana hada fuska Kiran sunanta alhaji badamasi yayi my nusy tashi kizo tasowa tayi tazo tazauna akan kujeran dayake kafin yafara magana ” nusaiba meyasa kikeson wahalar dakanki akan Wanda bemasan kinayi ba kindauki son azaad kin kwallafawa ranki bayan kinsan ko kallo Baki isheshi ba” dago Kai tayi dad ni ahaka nakesonshi Kuma nasan zan aureshi SE yanzuma na kare mata kallo fara ce soll doguwa batada wani shape irin na mata tana da dogon fuska da ido madedeta se hanci dakuma Bakinta Yana da Dan tudu ataikaice de bawata kyakyawar azo agani bace kawai de farin ne yaceceta tunda dama maza sunce( fara doguwa ko maiyace suna so) haidar dakejinsu yadoka uban tsaki wlh nusaiba Bakida hankali azaad din da wacce aka musu baiko ma be kulata ba seke toseki bar garin mugani ai , “Kai Dallah rufewa mutane Baki ina ruwanka da abinda takeso kabi kasa mata ido kahana yarinya sakatt to bari kaji inde gombe ne gobe goben nan zata tafi ” Madina tagama magana tana hura hanci hajiya Hussaina de bata tanka musu ba fruit dinta kawai takesha

Ahalin alhaji badamasi me ruwa kenan matanshi biyu hajiya Hussaina itace uwargidanshi SE Madina tabiyu sunkasance masu Hali mabanbanta hajiya Hussaina bata da damuwa ko kadan hasalima batason yawan rigima akasin Madina da takasance masifaffiya ta gidan gaba ko alhaji badamasi kanshi be tsiraba, haidar 27yrs,hibba 20yrs SE autansu Sadiq 16yrs sune wayan nan sune yaran hajiya Hussaina, nusaiba 19yrs SE kaninta Abdul 12yrs su biyu Madina tahaifa

“Shikenan nusaiba kishirya gobe zakibi flight ✈️ din safe” cewar alhaji badamasi rungumeshi tayi tana murna thank you dad .

 

 

Abangaren FANAN kuwa suna zaune a compound din gida suhaima na saman plastic chair zatama FANAN kitso ” Dan Allah suhaima karkimin da zafi Dan nasan hannunki ” naji kicire hulan nikam mufara cire hulan kanta FANAN tayi gashin data cukuikuyeshi tasa ahulan dakyar, suka zubo binsu da kallo suhaima tayi tarike ahannunta duk yinta takasa hadasu waje daya “Tabb wlh FANAN wannan gashin naki dakyar yakitso kiga gashi kamar Wanda ake bawa abinci nide innayi iyayina nagaji sede kisan yanda Zakiyi da sauran ” harara FANAN tawurga mata ” aikuwa Baki Isa ba inde kinsan zamu fara kibarmin Kaina kamar wata mahaukaciya gwarama karmu fara yawwa ” dariya suhaima tayi “to shikenan naji zanyi kokari mukarasa” kede kikasani yanzu kam cum ta dauka tafara taje mata gashin dakyar ta tajesu duka kalaba takeyi mata manya_manya saboda susamu sugama da wuri, SE kan mangrib suka karasa bakaramin kyau kitson yayi ba gashi yasauko har kugunta jelar gashin shafa kanta tayi tace ” yauwa koke fa Amma kya wani cemin rabi da rabi tom yanzu de taimaka ki min fakin dinsu sekimin donot dashi” bayan tamata dinne suka koma falo sukayi sallah suka fito. Zama tayi tana kokarin sawa su ya Usman abinci wayarta yafara ringing dagawa tayi” assalamualaikum besty ykk” abangaren Amira ta amsa tana tambayarta besty kinga salary kine ?? ” Ah ah ni wallahi nama manta dabatun shi ” to kidan Jira zeshigo okay sukayi sallama tana ajiye wayar text yashigo batabi takan wayar ba seda tagama sawa kowa abinci taduba taga Ashe alert ne shiga tayi tana dubawa zaro manyan idonta waje tayi “tofa” tayi maganar da Dan karfi tambayarta sukayi meyafaru batace musu komai ba tamikawa baba wayan yakalla yace kiramin layin doctor ammar din kira tayi aikuwa tayi saa yadaga maidawa baba wayar tayi, sallama baba yamishi Jin muryan sane doctor ammar yagaishesa (dama yasan zaayi haka inde sukaga canjin salary FANAN ) “mahaifin Fatima ne ke magana tambayarka nakesonyi” abangaren doctor ammar yace ” inajinka baba” naga salary Fatima ko wani wata 50k ne wannan Karon semuka ga sabanin haka yanzu tamikomin wayar naga 200000k (dubu Dari biyu) gyaran murya doctor ammar yayi yace ” baba kasan tunda Azaad yafara jinya itace take bashi special care so dama hakane inde nurses suna kula da patient masu fama da coma,mania, schizophrenia, paranoid etc duk salary su daban ne ” okay nagane allah yayi albarka cewar baba sannan sukayi sallama yakashe wayar yamika mata sannan yamusu bayani FANAN transfer kudin tayiwa baba duka dama haka takeyi ko biyar bata tabawa a salary ta zata mishi transfer ganin kudi yashigo ta account din dinshi da sunan Fatima yasa yagirgiza Kai FANAN bazata taba canzawa ba ” nikam fanan banace miki kidena turomin da salary kiba kidinga daukan rabi kina bawa mamanki Rabin saboda bazaku rasa wata bukata dazakuyi dashi ba ” ah ah baba nide babu abinda zanyi dashi saboda babu abinda na nema narasa to mexanyi da kudi awajena ni, mama ma Dana fada mata yanda mukayi tace kawai indinga tura maka itama babu abinda zatayi dasu ” tagama magana tana sunkuyar da kanta kasa baba yace “to shikenan allah yamiki albarka Ameen aka amsa sannan kuma magana akan aikinki Zaki cigaba da zuwa gobe in sha Allah seki kiyaye ” in sha Allah baba zan kiyaye yauwa. Autace “tace anty zankimin homework Dina Tana tambayar fanan? Ah ah auta bazanmiki ba sede in nuna miki yanda Zakiyi anjuma inmun koma daki kikawo SE in miki ” cewar FANAN tom anty,

 

 

Semun hadu gobe

 

via- https://play.google.com/store/apps/details?id=com.happyverse.diarywithlock&referrer=utm_source%3DD

‍⚕️‍⚕️ NIDA PATIENT DINA

Story Written by (MRS ISHAM )

 

Da sunan Allah me rahama mejinkai Ina fatan kamar yanda nafara rubuta wannan littafin lfy yabani iKon gamawa lfy ameen

 

 

Wannan littafin sadaukarwa ne gareku fans Dina allah yabar zumunci

 

 

 

 

____________________________________________

Back to top button