Hausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 71

Sponsored Links

71
Saida Umme ta warware sosai ta fara komawa daidai suka koma zuwa office daga Bena har
Zeenah Kuma har lokacin Safnah Bata dawo ba tana gidansu dad dinta ya koma duniyarsu ta dawo sabuwa a gidan ba hajiya yanzu sune komai da kowa tareda iKon dukiyarsa ta Nan da kadarorinsa na Nan Dan haka tini burinsu da zuciyarsu ta gara qarfafa a yanzu dukkanin shirinsu akan Dawood yake dawowarsa kawai suke bugata.
Bayan hankula sun kwanta sati biyu cif da rasuwar hajiyan daga Umme,dad kaante da dd babba har Safnah da Bena suna tsammanin dawowar D Amma shiru taflyan tasa ta gara kwanaki Amma tinda ana jinsa kalau sai kowa
Bai damu ba sai Safnah data matsu ya dawon sbd abubuwan dasuka haukace tanasha baji ba Gani.

Bena itace wadda tafi kowa kewansa haka
Kuma itace wadda tafi kowa boye hakan,
Kullum kusan a office take wuni sai yamma ta dawo tana dawowa Bata Wani zama sosai da dare yayi ya kwantawa bacci da wuri.
Wasu lokutan Kuma gurin Annenta take zuwa ta wuni ta dawo Saida Kuma a hankali hakurin Ababa ya fara qarewa sbd gabaki
Daya ya dawo Ababansa kullum Rena masa hankali kaantes keyi da cewan ya jira Bena ta karatu ta fara Aiki zaa yanka masa kudin albashin da duk wata zaa ringa Basa gashi ta gama karatun kusan tun shekaru Amma babu
Abinda yaji ko ya Gani,
Annenta Dayake ragawa sbd kada ya Bata rawarsa da tsalle a gaban kaantes din tini ya dawo da dokokinsa a cikin haukanta ma aikin gidan ake sakata tuquru. Duk Abinda Bena ta Tara nata na kanta ta tattara ta Basa kudi masu yawan gaske Dan ya Bata Anne ta nema mata lafiya Amma ya hanata Kuma ya karbe kudin.
***Abubuwan da Safnah takesha sukai mata yawa tareda sakar mata ciwon ciki me tsanani da Amai Dan haka Koda tai wunin ranar da zazzabi da ciwon cikin ta wuni me Dan tsanani.
Su Umme na ji Umme taje ta dubota lokacin su Bena na office Dan haka da duka dawo da dare Umme ta fada musu sbd Zeenah ta samu taie ta dubota.
Yau da safe very late ta iso office sbd sai data aje Zeenah gidan Alh basheer bulama din kafin ta wuce office da niyar idan ta tashi zata biya ta dauketa su wuce gida sbd yau bazata lega office ba zata Dan wuni gidansu Safnah din.
tana zaunawa ta dauko wayarta zata saka silent kira ya shigo wayar ta duba a hankali sai taga sunan Ababa.
Faduwa gabanta yayi hannuwanta na Neman daukan rawa ahankali sbd har gobe babu ranar da zasu hadu da Ababa Basu shiga wannan halinba,
Tsoransa Daya dasa musu a cikin jininsu yake har abada bazasu Dena ba idan ba Wani miracle din ya suka ba duk Abinda zasu zama kuwa.
Daga wayar tayi bugun zuciyarta na qaruwa cikin tsoro da fargaba.
A natse ta gaidasa kafin ta garasa baya bugatan gaisuwar yace “Kizo da motarki yanzu a nemi uwarki haukarta ta tashi tabi hanya.”
Yana gama fadan Hakan ya kashe wayarsa zuciyarsa na tafasa sbd ba garamin azaba zaiwa Annen ba idan ya kamata wannan
Karan,
Haukarta ta ishesa.
Gaba Daya ita kanta ta zamar masa lalurar da kashinsa yafi masa daraja akanta,
Barin da yayi mata a gidansu da Bai saketa yakaita bola da Kansaba sbd idan tana hannunsa ne zai juya Bena yanda yakeso tayi duk Abinda yace babu haufi.
Amma ko yanzu zai nuna musu su dukan
Yana Nan Ababansa babu Abinda ya sauya.
Bena cikin tsananin damuwa da tsoro ta miqe ta dauki wayarta takira Zeenah tace bazata samu zuwa daukanta ba gidansu zata
Annenta ba lafiya sosai
Bata Jira amsan Zeenah dinba ta kashe wayarta tana kokarin barin office din.
Zeenah dake tareda Safnah da momy duk sunji Abinda ta fada Dan haka Safnah taji ta warware sbd tafi kowa sanin Anne itace weakness din Bena me qarfin gaske.
Daki momy ta wuce tana Amsa wayan da babu kira bayan tashige ta qwalo Kiran Safnah wadda itama Abinda momyn ke tinani itama shi take tinani wato samun Saar Bena a daidai wannan gabar.
Zeenah data kasa nutsuwa sod sanin yanda duniyar Bena takeso takeji dashi kaman
Annenta Dan haka key din motar Safnah ta karba ta kama hanyar office Dan cimma Bena su tafi tare.
Tana ficewa Safnah ta karbi key din motar momy suka fito tareda momyn sbd hanyar gidansu zuwa gidan Ababa zasu Riga Bena da zata fito daga office Isa express titin na bavan gari Wanda babu mutane kwata kwata yanda ya kamata sbd dama tin farko kaman daji ne haka Ababa ya zabi zama gurin sukai rayuwa anan.
Yanda Safnah ke tuqi kaman hannuwanta na rawa da qafafunta sbd titin zuwa gidan Ababa. da suka kama Wanda shekarun baya suka ringa dawowa mata zuciyarta na bugawa kaman zata fado.
Dishi dishi take Gani a idanuwanta sbd mummunan tsoron Dayake cikin jininta Daya taso na Ababa.
Fuskan Ababan take Gani akan duka titin
Datake tafiyan
Rawa motan ta faravi dasu sbd hayyacinta
Datake Neman
Bata ankaraba tayi sama da Anne data hawo titin Kai tsaye tana kalle kalle da Kiran sunan Benazir data kusa kawowa tana hango
Annenta tana qara gudun motarta ta kawo gurinta akan idonta motar tayi sama da Annen ta watsar gefen titin
Take Wani duhu ya mamaye idanuwanta ta saki tata motar itama tana kokarin Yi daji
Momy na ganin haka ta jijiga Safnah da batasan waye ta Kade ba sukai kan motar
Bena da tasu motar suka daka da qarfi suka qarasa tura dajin da gudu sosai yanda abin zaiyi munin da wuya a rayu.
Basu bi takan Anne ba Safnah da kanta ke juyawa sosai da abubuwa da yawa kaman zata haukace take ji ita bayan motar Bena tabi da gudu sbd tabbatarda ta tafi kada su bar baya da qura.
Momy kuwa kan Anne tayi ta Gani ko ta mutu ko tana Raye ga mamakinta sai taga matar ta tashi gefen kanta na jini tana kokarin tafiyarta. Baya momy tayi da sauri sbd Gane mahaukaciya ce suka kade sbd alamunta sun nuna.
Safnah kuwa kan motar Bena dake tsananin hayaqi ta nufa ta ta fara kokarin Bude motar
Dan dubawa.
Sama sama Bena ke Jin iska da motsin abubuwan duniya ta Bude idanuwanta daqyar ahankali tana ganin dishi dishi duhu duhu jini na fita hancinta da fuskarta duk Daya Bata jinin.
Murfin kofar motar da aka Bude ya saka haske shiga cikin idanuwanta tafara ganin fuskar
Safnah ahankali tana bayyanar mata. Cikin mummunan hali take kanta na juyawa
Amma Kuma idanuwanta dasuka nuna mata Safnah sake shigar da ita mawuyacin hali sukai motsawa takeson Yi ta kira sunan
Safnah Amma ta kasa.
Safnah na ganinta cikin wannan halin taji toro da bugawan zuciyarta na tsananta ta juya da sauri zata gudu takira momy sbd ita bazata iya garasa Bena din da hannuwanta ba saidai momy ta qarasata.
Tana juyawa Bena tayi Wani garfin halin rigo hannunta Daya da hannunta dakeda jini sosai a wahale ta kira sunanta tana cewa
“Safnah kece???
Safnah, Safnah kece safnan Anne??
Wasu hawaye masu tsananin zafi ne suka gangarowa safnan ta kasa juyowa ta Kalli
Bena din.
Sake Kiran sunanta Bena tayi tana cewa
“Safnah ki taimaki Anne,
Ki taimaketa ki duba Wani ya kadeta Dan Allah idan kece kiyi magana naji”
Juyowa Safnah tayi hawayen da yamutsin zuciyarta na qaruwa ta kasa magana sai hawaye ta gyada Kai ahankali tace
“Nice Safnah Amma ba safnan Anne ba”
Wasu hawayen azaba da Fita hayyaci masu zafi suka gangarowa Bena ta Bude baki tace “Ni kadai na ragewa Anne Dan Allah idan Wani
Abu ya sameni Safnah ki kula da Anne tana
bugatan taimako da kulawa..
Jin Hakan ya saka Safnah kallan Bena din da
mamaki ta dawo da sauri tareda tarota jikinta
tana girgizata tace
“Ina sumayyah?
Ta rasu gurin haihuwan Amnah…
Wani irin zufa ne ya karyowa Safnah tana
kallan Bena hankalinta na Neman kasa
fahimta Amma Kuma tana bugatan fahimtar
komai kafin Bena din ta mutu,
Meya hada haihuwan Amnah da sumayyah
Kuma. “Ni kadai na ragewa Anne Dan Allah idan Wani
Abu ya sameni Safnah ki kula da Anne tana
bugatan taimako da kulawa..
Jin Hakan ya saka Safnah kallan Bena din da
mamaki ta dawo da sauri tareda tarota jikinta
tana girgizata tace
“Ina sumayyah?
Ta rasu gurin haihuwan Amnah…
Wani irin zufa ne ya karyowa Safnah tana
kallan Bena hankalinta na Neman kasa
fahimta Amma Kuma tana bugatan fahimtar
komai kafin Bena din ta mutu,
Meya hada haihuwan Amnah da sumayyah
Kuma. “Ni kadai na ragewa Anne Dan Allah idan Wani
Abu ya sameni Safnah ki kula da Anne tana
bugatan taimako da kulawa..
Jin Hakan ya saka Safnah kallan Bena din da
mamaki ta dawo da sauri tareda tarota jikinta
tana girgizata tace
“Ina sumayyah?
Ta rasu gurin haihuwan Amnah…
Wani irin zufa ne ya karyowa Safnah tana
kallan Bena hankalinta na Neman kasa
fahimta Amma Kuma tana bugatan fahimtar
komai kafin Bena din ta mutu,
Meya hada haihuwan Amnah da sumayyah
Kuma. Kuka ta fasa Mai taba zuciya da bayyanarda kewa da kaunarsu me tsanani ta rungume
Bena din tana cewa
“Bena karki tafi Dan Allah kibarni da Anne tinda kince sumayyan ta mutu,
Na dawo gareku yanzu bayan gwagwarmayar danasha Dan Tara Abinda zanzo na fansheku na tararda wannan mugun ganin”
Kuka Bena ke son Yi Amma azabar datakeji ta hanata cikin wahala.
Kaman daga sama aka jeho Anne gurin tana ganinsu ta qaraso gurin Benazir da gudu saidai kafin ta tabbata tayi Ido biyu da Safnah wadda itama ita take Kallo jikinta na wata irin rawa. Cikinta Anne tayi ta qanqameta tana Kiran sunanta Dana sumayyah Dana samirah duk lokaci Daya sbd ta manta waye acikinsu take gabanta.
Safnah na ganin haka ta janye da gudu zata bar gurin Anne ta bita lokacin tini Bena ta
Sume a gurin.
Cakumota Anne tayi tana Kiran sunayensu su ukun Banda Bena.
Momy dataga Annen zata saka a cimmusu gurin Jan Safnah da Annen taqi saki tayi dukkaninsu ta tura mota suka bar gurin sbd hayaqin motar Bena Daya fara yawa.
Suna barin gurin Zeenah na isowa da motarta kaman ance ta duba gefen hanya ta hango mota na hayaqi da sauri tayi parking tana yiwa wata motan data kawo hannnu suka tsaye ana gangarowa aka duba taga motan Bena da ita
Ciki
Hankali tashe aka fidda Bena din mutane tini hayaqi yayi alerting nasu suka taru.
Ana cire Bena motan tafara kamawa Dan haka jikin Zeenah har Wani mazari yake da jüjiga sbd tashin hankali.
Momy da Safnah kuwa Nisa sukai sosai da gurin Safnah ta Kalli Anne tana kokarin
Kwantar mata da hankali cikin dubara har
Annen ta sauko ta nutsu tana kallan Safnah din ahankali kaman yarinya qarama.
Numfashi Safnah ta sauke hannuwanta na rawa bakinta ma Yana rawa tace
“Anne samirah ce ni ba sumayyah ba ba
Safnah ba.

Gyada Kai Anne tayi ahankali.
Cikin kokarin sake Hana rawar jikinta bayyana tace
“Anne Ina sumayyah?
Meva sameta?
Waye ya haifi Amnah tsakanin sumayyah da
Bena?
Ya Akai Bena ta hadu da Bilal tayi aure a
Kaantes??”
##MAMUH#
#DBENA
#KAANTES
#SAFNAH
#ABABA

Back to top button