Hausa NovelsYar Zaman Wanka Hausa Novel

Yar Zaman Wanka 16

Sponsored Links

.

“Lallai Inna kin yi ƙoƙari” Ya faɗa had lokacin ya kasa tsaida dariyarsa, Ashrof ma sai tayashi take duk da Sadiya ta bata labari amma sai ta ji kamar yanzu ne ake farkon jin labarin.

“Kai Abida baka cin ribar zance ne, ka tsaya ka ji yadda ta kaya mana tsakanin ni da Imirana ai bai fa ci bulus ba, mutuminka na sanya Sadiya ta ƙwala masa kira lokacin ya sha dariyarsa ya more, a raina na ce bakin dariya shi ne na kuka, ai yana shiga ɗakin na shammacesa a janyo Halima muka fito na bankeshi a ɗakin, kira yake Inna ki buɗe dan Allah, aikuwa na yi kunne uwar shegu na ce sai na rama sai da ya horu sosai a ɗakin na buɗe, ka san ya na ga Imirana” Ta faɗa tana dariya, su ma dariyar suke har Sadiya da ta kasa riƙe tata dariyar, hakan ya sanya Imran ya shigo yana ta sallama basu ji ba da yake bai wani ɓuga maganar ba dama jikinsa ya bashi ana cin namansa a gidan tun da ya ga motar Abid a waje ya san Inna tana nan tana bada labarinsa.

“Yana laɓe a jikin bango yadda ka san ƙadangare ya rakuɓe a waje ɗaya sai maƙyarƙyata yake kamar kazar da bazai ya kamata” Ai gabaɗaya suka ɗauki dariya har Inna a dai dai nan Imran ya shigo falon sai haɗe rai yake kamar zai kai musu duka.Ɗif suka daina dariyar sai Abid da ke ƙoƙarin danne dariyar taƙi tsayawa har ruwa idanunsa suka kawo saboda dariya sosai yake hango yadda abokin nasa ya yi, a rakuɓe a ɗakin ga kuma miciji a gefe, tsaf Inna ta iya bada labari yadda mai sauraro zai ji kamar a gabansa ake yi.

“Abokina ka dawo? Ka ganni kamar an jefoni daga sama ko ban maka waya ba” Cewar Abid yana goge ƙwallar idonsa da dariya ta sa ta taru. Wani mugun kallo Imran ya masa wanda ya sanya wata dariya ta ƙwacewa Abid aikuwa ya sakikayarsa dan ya kasa riƙeta.

“Ai abin akwai abin dariya Abida dan ma ba a gabanka aka yi ba” Inna ta faɗa tana dariyar dan ganin Imran ma sai ta sake ƙara ƙarfin dariyarta dan ta ƙular dashi tun da shi bai san abin arziƙi ba.

“Yo da kana siyo min ɗan goro da turmin zane, ai da na ɗan rangwanta maka ka san zuciya tana son a kyautata mata” Cewar Inna a zuciyarta a fili kuma ta ce.

“Kallai abin arziƙin da abokinka ya kawo min, wancan na gaban Asharofa kuma ya ƴaƴanka ne da matarka”

“Ta faɗa tana kallon Imran da ke ƙoƙarin ajiye ledojin da ya shigo da su.

“An gode” Kawai ya ce tare da juyawa zai fita.

“Amma kuwa yau nan tabbatar ta mugun halin ka Imirana ace a kawo wannan uban kayan kuɗi amma ka yi godiya ƴar mitsitsiya, ina laifin ma ka ce an gode madalla Allah amfana Allah saka da alkairi ya bar zumunci, ka ƙara da cewa kai amma kayan sun yi kyau sosai har da Inna ma aka kawo wa to madalla, amma dan baƙinciki kake min kuma da baƙin halinka Imirana shi ne ka ce an gode a takaice” Cewar Inna tana gatsinen gefen hanci.

“Haba Inna ai tsakaninmu ba godiya” Cewar Abid a fili yana ƙara maƙe dariyarsa. A zuciyarsa kuma ya ce na tabbata Imran ya ji Inna tana bada labari amma babu yadda zai yi da ita, kuma gashi magana take faɗa masa a kan ƙin doguwar godiya kuma ba yadda zai yi da ita lallai Inna ita ce maganin Imran.

“Ka ji ɗan arziƙi irin albarka, wallahi kana birgeni Abida…

“Idan ka gama neman maganar ka same ni a waje” Imran ya katsewa Inna maganarta yana kallon Abid tare da ficewa cikin ɓacin rai.

“To ina fitowa ” Cewar Abid yana bin bayan Imran da kallo dariya na cinsa.

“Kai rabu da shi yana ta ƙuncin rai ka yi zamanka a nan mu sha hira in maka abin ban faɗa maka ba” Cewar Inna tana kallon Abid.

“To Inna”

“Ashrof miƙa masa yaran ya gan su” Sadiya ta faɗa cikin sanyin murya dan yadda ta ga Imran na harararta da ya shigo hakan ya sanya ta gane bata kyauta ba da aka zauna da ita ana bada labarinsa suna dariya.

“Lah ta barsu ma tun da bacci suke kar a tashe su, ai ni nan tunda gidan zuwa na ne na gansu wata rana”

“Kana ji ko Abida jiya kurman abokin nan naka ya kawo abokinsa Sojojo”

“Inna meye kuma Sojojo ko suna ne?”

“Ina kai ka, baka cin ribar zance”

“To ina jinki Inna”

“Nake faɗa maka Sojojo ne dan bana kirashi Soja ba saboda ragwantarsa”

“Ragwanta kuma Inna”

“I mana” Inna ta faɗa tana kwashe duk yadda aka yi da Abdallah da ya zo barka da matarsa.

“Inna haka aka yi ashe haɗe su kika yi, kai abokina ba dama” Ya faɗa yana dariya

“Kai dai bari yo shi ma Imiranan ranar nan fa suma ya yi saboda Hassan ya sawaya ya zama miciji a jikinsa” Ta faɗa tana dariya. Haka suka sha ta dariyarsu har cikin Abid yana ƙullewa dan ya ma manta Imran na jiransa a waje. Sai can ua tuna ya musu sallama ya sanya hannu a aljihu ya ɗakko dubu ɗaya ya miƙawa Inna. Hannu ta sanya ta karɓa tana washe baki.

“Haba Abid ai da ka barshi hidimar ai ta yi yawa ” Cewar Sadiya cikin jin nauyin Abid.

“Lah ba kamai ai…

“Rabu da ita kawai in banda baƙinciki meye wata dubu ɗaya dan ya bani kyauta zaki wani haƙiƙice kina cewa ya yi hidima ai dama kowa ya san ya yi hidima musamman da ya fi mijinki da bai san ya siye zuciyar mutane da kyauta ba sai baƙin hali da na zuciya fal ransa” Ta faɗa tana sanya dubun a cikin ƴar pos ɗinta.

Dariya Abid ya yi jin abin da Inna ta ce haka kawai shi ds a ce za a barshi da Inna da ya huta d shiga damuwa ko ɓacin rai, saboda ita bakinta ba ya shiru kuma bata gajiya da abin dariya duk da ita tana yin komai dan raha ne.

“To Inna sai kwana biyu”

“Kwana biyu fa Abida sai ka ce an maka baki, yanzu sai ka iya kwana biyu baka zo mun gaisa ba, ai baka ji daɗin da na ji ba da ka bani bugun Abujar nan”

” To Inna idan na samu dama da lokaci zan ke leƙowa ”

“To nagaode sosai” Ta faɗa lokacin da ta fito har ƙofar falon Abid ya sanya takalminsa ya fita.

“Oh ɗan nan da kirki yake Sa’adiyya ya fi min mijinki Imirana sau miliyan ma” Cewar Inna lokacin da ta zauna a kan kujera tana ƙara ganin atamfarta.

“Inna dan Allah kike iya bakin ki idan abokan Imran sun zo kin ga ko a fuska ya nuna ba ya so kina shiga shirginsu” Cewar Sadiya cikin lallaɓawa dan ta san Inna hukuma ce sai da lallashi.

“Ikon Allah, lallai Halima wuyanki ya fara isa yanka sauran kuma a gwada wuƙa a tabbatar, yanzu sabibi da Allah ni kike faɗawa wannan maganar to ni da banda ma gaisawa da muke a ɗan taɓa hira ina ni ina su, ni fa kawai dan na ɗaukesu ɗaya da ku ne tamakar jikokina in ba haka ba me ma zai haɗa ni da su, in kuma baƙincikin ɗan abin da zan ke samu kike yi to duk da babu wanda ya taɓa bani wani abin arziƙi in ba Abida ba”

“Abid Inna” Cewar Ashrof.

“Ke ki kiyaye ni, in ma Abu zan kirashi ina ruwanki”

“Ki yi haƙuri Inna” Cewar Sadiya.

“Da haƙurin ta mutu sadakar nawa kika bani?”

“Allah baki haƙuri”

“Haƙuri kaya ne naɗa gammo ki ɗauka”

Bayan fitar Abid Inna ta ce ta gaji da zaman cikin gidan fita za ta yi ta zagaya ƙafadunta dan ciwo suke mata, gidan Hajiya Amina za ta je. Haka ta musu sallama ta fita ta sha wata atamfarta mae kyau, ta saka ɗan madinanta ta kama hanya ta fita, har Sadiya ta bata kuɗi ta hau ɗan sahu amma ta ƙi karɓa wai ita ta fi son tafiya a ƙasa saboda kalle -kalle.

Hanyar gidan Hajiya Amina ta kama, har sai da ta je gidan bayan ta gama kalle -kalle da ratse -ratse. Haka ta je gidan Hajiya Amina suka gaisa ta ɗan jima sai kuma ta kamo hanya ta taho gida dan Hajiyar ma sai da ta yi ta yi da ita a kan ta zauna idan aka yi sallar magariba ta yi sallar sai ta tafi, amma Inna fafur taƙi zama dan ta fi so ta taho ido na ganin ido. Saboda ta fi so ta taho ido na ganin ido dan ta ga gari gari ma ya gan ta.

dan haka ta kamo hanyarta ta taho riƙe da ledar da Hajiya Amina ta zuba mata bakilawa. Tana tafe tana kalle-kallenta tana ƴar waƙarta a hankali, tana cewa.

“Carman dudu carman duduwa , carmagade, akwai wani baƙo a gidan mai gari, carmagade, ba duka ba ya lakuci, carmagade, in duka wa zai bashi ne, carmagade, aradu ta Allah ba zan bashi ba” Tana cikin yin waƙar ne ta hango wani ƙerarran gida mai shegen kyau tun daga nesa gidan ya birgeta. Dan dama ba ta hanyar ta bi ba a tafiya yanzu kuma sai ta canja hanya dan ta sake ganin wasu sabbbin abubuwa ba irin wanda ta gani a tafiya ba.

“Ikon Allah masu gidan nan kuwa sun san ana wahalar kuɗi kuwa a duniya, an ya kuww sun san sunan wani abu wai babu, ace wannan gida kamar ba a duniya ba” Ta faɗa tana tsaye tana ƙarewa gidan kallo.

“Oh ni Azumi ina can a ƙauye ina fama da ɗaki ɗaya a gidan Malam kullum ana bala’i da Tasalla to ina kuma ga na ganni a gidan nan ina ga kuma sai an mana tsakani da Tasalla dan kar take faɗawa mutane ita kaɗai ce matar gidan” Ta faɗa tana ƙarasawa ƙofar tangamemen get ɗin da ke buɗe, sai da ta tabbatar babu kowa mai gadin ma ba ya nan…

Masu son a tallata musu hajarsu MMN AFRAH 09030283375
[24/03, 5:13 AM] Mom Mashkur First class: Wannan littafin kuɗi ne 300
Za a tura ta wannan accaunt ɗin Fa’iza Abubakar 0020281885 Unity bank shaidar biya ta wannan no 09030283375 idan katin waya ne mtn Ƴan Niger su tuntuɓi wannan no +22785885134

Back to top button