Hausa NovelsYar Aikin Karuwai Book 2 Hausa Novel

Yar Aikin Karuwai Book 2 Page 76-80

Sponsored Links

Zuwa Yamma Ahsan ya dira a Nigeria ta Lagos ya sauka,Cele bata San shirinsa ba ma,yana zuwa motoci aka kawo Wanda ya siya a nan sababbin gadal masu kyau da tsadar gaske guda uku guda biyu na securities daya tasa,komai nasa aka zuba a booth ya shiga mota suka wuce garin da Cele ta masa address,Hammad ne dai driver da shi suka zo tare,Cele kuwa suna Shan kida ta sa Omaira ta hada mata zobo me sanyi a ciki zata ebi nata na sha zata zubawa Salma magani ita da Auta,Omaira ta wuce kitchen ta dafa zobo da kayan kamshin da abarba a ciki ta barshi ya huce, ni dai miracle Nawwar ya kirani naje wajen baso na iske Auta,Nawwar,Mami,Baffa a ciki na mikawa Baso jaririna ya Ganshi ya mini barka ya zaro kudi sun Kai dubu goma sha biyar ya dora akan kayan dake jikin Jaririn ya Miko min na karba nayi godiya na zauna tare da mikawa Nawwar Baby Abdullah,ya karbi abinsa,kudin na kwashe abina na zuba a Jakata.
Auta ne ya Kira Salma a waya yace tazo,Salma ta tafi inda yake,tana zuwa ta koma ta zauna a gefen Auta tace Yaya sannu da zuwa Ina yini? Yaushe kazo? Su Mami muna zaune Yace ke karki min ae yane ko baki gane bane dama zuwa nayi na fada Miki mahaukaci dai ya warke,Salma ta bude baki tace Allah? Yace dama hatsari yayi kwakwalwarsa ta tabu rannan ya fita mota ta sake bigeshi Allah yasa baiji ciwo ba sai ya dawo hayyacinsa.

Ashe mahaukaci dai hamshakin attajiri ne,shine Kuma sanadin shiriyata,bayan aurenki da sati daya ya warke,sunansa ma Engnr Alhaji Mukhtar Dan asalin Adamawa ne amma a Kano suke zaune,a hanyar kano zuwa Adamawa yayi hatsari ba Wanda ya sani a danginsa ya haukace haka har ya fada gari gari har Yazo layinmu a cikin Kano,Yan uwansa sunyi cigiyar duniya ba a Ganshi ba,an zaci sace shi aka yi,yana da matarsa da yaransa biyu,yace a gaishe ki ma yace a bashi number dinki Kuma watarana zaizo,shine ya bude min shago na gaske a Kasuwar Kwari,ya siya min gida na million goma,mota ma shi ya siya min ita da kika ganta sannan ya kaini gidansa can dake Abuja a can nayi sati uku,duk zuwan nan da nakeyi nan Ina Abuja,ya dorani a hanya ya dinga min fada da nasiha har Allah yasa na Daina Shan komai,naga Shaye Shaye baida amfani a rayuwa face ya haukata mutum ya lalace ya zama dan Iska,Kalli yanda na dawo mutum kuma dake me kudi ne sai naji fadansa da wani talaka ne ko gaskiya ce bazan bita ba sabo da bashi da abin bani, kai duniya amma haka ya dinga zare min Ido yana fada yana min masifa Baso naki Salma shuru ban iya cewa komai ba,da ya warke fa a kan titi sai da Yan unguwa matasa suka bashi labarin abinda nayi masa amma shi bai iya tuna komai ba,Matarsa da Yan uwansa baki gansu ba Salma sai kin wanke hannu kafin ki tabasu.
Yace Kuma abinda kika masa kema har gida zaizo da iyalansa da Yayansa da Kaninsa,Salma tace Masha Allah Yaya na maka murna,yace iceko kin saita halinki? tace ae wallahi,wallahi Allah Yaya na canja Karka sa a bani wani aikin,murmushi yayi yace ai bazan sa ba Salma,ban zaci zan shiryu da wuri ba sabo da kar na aureki na cutar dake shi yasa na bawa Auta ke badan kudinsa ba ni Kam haduwata dashi naji ya kwanta min a rai kawai shine dalilin da yasa na dage sai ya aureki, ba wai dan bana sonki ba Babu Wanda zai ce bai sonki,yanzu Yaya dama kana so na? ya furta na dai soki ba Ina sonki ba,ki gyara zancenki ya soki a da banda yanzu ya daina babu ya kare cewar Auta yana gefe kishi kamar ya kashe shi, Baso yaci gaba yanzu sai dai Yan uwantaka tunda ni a tunanina na cire rai da zan shiryu ma amma wani ikon Allah Ina aurar dake sai Mahaukacin ya warke ba dadewa kuma Allah ya shiryar dani ta sanadinsa,amma bayan na aurawa Auta ke na dawo gida Salma naci Dadi na more kudin da Auta ya bani akan zai aureki Million daya Banda sauran hidima da ya min iri iri,nace sai ya bani million daya zan bashi ke na siyar masa ke tunda kin san lokacin kwakwalwar bata nan ni iya tunanina siyar dake nayi,Auta yace ai dan Adam yatsansa daya ma ko duk abinda ke duniya za a hada baza a iya siyansa ba sabo da Babu me yin wannan abin sai Allah,yace shi dai ba siyenki yayi ba aurenki yayi kudi kawai ya bani ne,bayan Kuma naci kudin nan a cikina nida mahaukacin nan nazo na dinga tunaninki kamar zanyi hauka duk karfin zuciyata sai da nayi kuka duk kayan gidan nan sai da na farfasa komai na gidan ba abinda na bari,har gado sai da babbala su,na fara cuta kamar zan mutu da kyar Allah ya taimakeni Kuma ban dawo nace Auta ya bani ke ba na Riga na aura masa tsakanina da Allah,na sawa zuciyata ko mene Dan Adam ya rasa to ya hakura ya barwa Allah tunda nayi tsakani da Allah Kuma Allah yasan dan shi nayi to nasan zai min canjin Alkhairi inshallah, haka Allah yaso dama,dama Yaya baka yi auren ba? Ba Aure nayi ba ni kawai Dan ki cireni a ranki na samo kanwar Saminu abokina Sayyada ai kin Santa to Sayyada ce ta Miki magana a waya ba Matata ba,ni kin san ban taba kula mace da sunan so ba kawai dai barni da Shaye Shaye na Kuma yanzu Alhmdllh ko taba sigari karya take ta sake shiga bakina Wanda ya kirkireta ma ubansa,ubansa ma ubansa,muka yi dariya muna jin Baso abin alkhairinsa ya taba mana zuciya, Auta ma yayi dariya wannan zagin ai sai Wanda ya taba Shaye shayen,Salma tace Yaya Allah ya baka ta gari,yace kin hakura da Baso kenan? Salma tace uhm Auta yace kiyi magana sai ki zauna gulma,Salma da karfi tace aeeeeeee….na hakura ni Kam tuni ni zan iya tayashi zaben mata ma,Baso yace ni na gani ma da idona wata ce me hankali ta nutsuwa a jikin bango,Baffa da Mami suka yiwa Baso godiya sosai suka ce gaskiya Idan kaga mutum a wani Hali Karka zage shi ko ka tsane shi,Baso yace Almajiranta ce ta jawo min nima Wanda sai kayi bara zaka ci ka koshi yunwa ba abinda bata sawa,wahala ba wacce Almajirai basa sha a duniya dole su dinga lalacewa a maimakon Karatu,a addini ba inda akace sai ka tura yaro Almajiranta sannan zai samu ilimi ,Iyaye mussamman na kauyuka wasu yaran marayu ne,wasu basu da Uwa sai matar Uba,wani Yan uwa ne zasu kasa rike shi su turashi Almajiranta da sunan Karatu gasu nan dai Wanda sai dai Idan ba Allah ne ya tsare ba duk kusan lalacewa suke musamman na yanzu in Banda siyan waya da jin wake wake ba abinda suka iya,Blue films a wayar Almajirai baza su irgu ba Yara kanana,su kunna kida suna yawo da speakers suna chashewa rawa iri iri,Shaye Shaye,sata, iskanci iri iri akan kawai a rike yaro a gida a bashi ilimi da tarbiyya baza a iya ba duk islmiyyoyi da makarantun allo na gida da sauran makarantun dare duk basu Isa mutane su Kai yaransu ba sai dai a dinga tura Yara bara wannan zubar da kimar addini ce,Baso baya jin hanya shi Kam ko tsoro ya mike yace tafiya zaiyi daga Abuja yake ya biyo ta nan sabo da yaji ya ake ciki.

Su Mami suka yi suka yi ya kwana yace shi sai dai ya kwana a hanya suka masa Allah ya tsare,muka koma wajen kida,Nawwar yace to ko wa ya gani yake so Auta Idan ka raka shi kaji,yace ae zanga wace me hankalin nan suka fito suna hira da Baso sai Star ta wuce yace yawwa gata nan ita na gani,Auta ya dinga kyalkyala dariya harda rike ciki yace wannan tana da aure baka ga cikinta ba karami Kai baka gane ba,Baso Bai San Star rawa tayi taji Dan cikinta yana juya ta fita ta tsaya a jikin bango ta makale ta nutsu ta koma Yar kallo wai a haka shine yace nutsatsiya ce,Auta ya nuna masa Omaira dake tsaye a gefen Cele yace na zaci waccen ma ka gani,Baso yace naga kamar zata yi wulakanci ni Kuma ban son yanga da Iyayi yaran nan,Auta yace Allah tana da hankali ka aureta, Baso yace ba ruwana waccen matar manya ce Idan mutum zaiyi aure an Fi so ya auri dai dai shi amma Idan ka auri mace take ganin kamar alfarma ta maka to ka shiga uku ni ba yaro bane irinka,Auta ya dinga cusa masa Omaira Baso yace Kai rabu da ni da fetsararrun yaran nan,Auta yace inshallah sai ka aureta wallahi Kun dace itama a chake take Baso Hamra ya gani yace ga wata me kama da Kai can,yace Yaya ta ce yace ahh to wannan ma tayi amma waccen da ganinta Omaira kace ko to baza tayi mutunci ba,Auta yace Hamra yayata ai tana da Mijin aure itama ta kusa aure,Baso yace to bani da sa’a a gidan nan amma waccen omaira Idan na kalleta ma nasan ba sauki, yace bada ni ba ya bude mota ya shiga yace Allah ya hada kowa da rabonsa ba ruwana,Auta yace to shike nan tunda Kaki Omaira ta shiga uku tayi bakin jini,Wanda ma take so an hanashi aurenta,Baso har yaja mota ya tsaya ya Kira Salma tazo ya bata kudi dubu ashirin yace gashi nan Idan kina son wani abu ki fada min a waya zan tura miki,Salma tace to Yaya na gode ka gaida gida Allah ya tsare,yaushe Yan uwanmu zasu zo? Yace sai kin haihu,tace Allah ya kiyaye hanya yace Ameen.

Cele zobonta ta hada tasa a fridge,wuraren Nagriba duk kowa ya tafi gida sai iya su Cele da yan gidan kawai Yan aiki sun gyara ko Ina dake bai baci ba tunda ba wani taro akayi me yawa ba,ni me jego wanka nayi dake an gyara ko Ina gadona cike yake da gift na jariri Jakata ta cika da kudi gasu nan dai kyaututtuka daban daban gasu nan,Jaririn Cele tazo ta dauka nace wallahi bani abina,wanka zan masa ko ya huta nace bana so ki karya min yaro bada ni ba,fushi tayi ta bani abina,nace zo ki kwashe kudin nan ki gyara bed din Nawwar zai zo mu gaisa,Cele tace baza a gyara ba ta fice,nayi dariya na Kira Omaira nace gyara gadon nan ki kwashe kayan ki zuba a can ma’adanar kaya inda Babu kaya a ciki duk ki shiryasu a ciki,Omaira tace Aunty nima Allah ya bani Miji na gari nayi aure na huta,Na kalleta nace Ameen Omaira kema auren kike so kenan? tace ae wlh Aunty kina ganin Salma sai cikinku take shiga mu ana korar mu, Cele fa cewa tayi idan na shigar muku rawa sai taci ubana Ina son rawar na hakura sabo da nasan halinta,kiyi hakuri to ku dinga hakuri da Cele, Omaira tace jaraba ai gara ma tayi auren ta tafi mu huta,bari tazo na fada mata,Omaira ta hau magiya kar na fadawa Cele,nace to Allah kika Kara gulmarta sai na fada mata.
Shiryawa nayi cikin kayan baccinta Riga me siririn hannu da dogon wando blue da su,Mami ce tazo ta dauki yaron ta masa wanka ta kawo shi na shirya shi tsaf da pampers dinsa,nono na bashi ya sha duk yasha wahala sai bacci na kwantar da shi,Omaira duk suka tafi masaukinsu sun gaji suma Banda Cele tare muke kwana da ita,Mami ma tana part din Baffa. Nawwar sai waya ya min yace yana gida shi bacci yake ji da safe zaizo nace Allah ya kaimu yace ki gaida min Baby na,nace zai ji.

Cele ta hada zobonta tsaf ta fita ta samowa Ahsan take away yace ya shugo garin shi yasa ta samo masa kalar abincinsu da suka Saba ko zai iya ci, nace ta kaishi part din da Auta yake ta sa an Kara gyara ko Ina amma sabo da ta shiryawa Auta da Salma mugunta sai tace Salma Dan Allah muje can room din ki kwana a wajen Auta Ahsan zaizo sai mu dauki daya bedroom din Kuma ku dauki daya kunga shike nan bana so naje ni kadai kar yace zaiyi min wani abu nafi so sai an kaini dakinsa kinga Idan yasan a gidan wasu yake dole ya hakura,Salma tace to,Cele tace yawwa tayani Kai abincin can,Salma ta tayata komai suka gama shiryawa a bedroom din da Ahsan zai kwana,suka dawo part din Mami Cele ta shiga kitchen ragowar zobon ta tsiyayi nata me kyau ragowar ta zuba masa maganin sha’awa kadan yanda Mandula tace bata wuce ka’ida ba,ai kuwa Salma ta dakko nata a glass cup ta kurba sau uku sai na Salma yafi nata yawa tazo ta zauna a Palo ta kwalawa Salma Kira zo,Salma tazo tace ga zobo ki shi Salma tace na gode ta dauka tana faman chat da Auta suna soyayya,Zobo na Hannun Salma bata sha ba,Cele tana sha Ahsan ya kirata akan ta fada musu gidan Ina yake, sabo da tasan nata yafi kadan sai ta mike ta ajiye a saman center table ta tafi wajena na fada mata address na gidan,bata San Salma da kwaikwayo ba,ita Salma tunaninta na Cele yafi dadi sabo da haka ita nata zata sha,Cele tana tashi Salma ta shiga kitchen ta rage nata a sink kadan ya zama Kai Daya Dana Cele sai ta fito ta canja kofi tace naki zansha Nima watakil yafi dadi ta ajiyewa Cele nata ta dauke na Cele ta shanye tas,Cele tana dawowa ta gama waya murna ta kamata Salma ta sha masifa, taje kitchen ta dakko ragowar me maganin a glass cup tace ki kaiwa Auta Shima yasha,Salma tace kamar kin sani bana so naci Abu bai ci ba ta mike tana murna ta fita,Cele tace Yar banza taki ta Kare ta dauke zobon Salma ta shanye tas a cikinta,Salma ta taho da cup zata kaiwa Auta sai Auta yace ya fita Nawwar ya aike shi,ta juyo zata koma sai zobo ya subuce ya fadi cup din ya tarwatse,Salma tazo ta share glass din ta kwara ruwa a wajen yabi ruwa tace kar mutum ya maka kyauta ka kifar aga kamar wulakanci ne gwara nace mata ya sha,Salma ta koma tace Aunty ya sha baki ji yanda yaji dadinsa ba an gode sosai,Cele taji Dadi tace ba komai ai an zama Daya ta mike ta koma dakin Miracle.
Tana shigowa nace Cele shirya kudin nan mu irga Cele ta zauna a kasa ta baje kudi tana irgawa Salma tana tayata sabo da tana jiran Auta ya dawo,Can Cele sai muka ga tana motsa cinya,tace wash…taci gaba da irga kudi,,gashinta ta Sosa,sai ta cire dankwali ta ajiye gefe,ta tale kafa ta tsuke bata magana irgan kudin ma ta kasa,dubu ashirin,ashirin da Daya,da gudu,sittin,tsaki ta ja ta dawo baya da irga daya,biyu,uku, takwas sai taja tsaki ta dawo baya, na kalleta duk ta rasa sukuni ta hada zufa sosai,nace Cele kalau kuwa? Cele tace Ina fa lafiya, Salma ajiye kudin nan ki Dan bamu waje,Salma ta ajiye kudi ta fita,Cele tace yarinyar nan na sawa maganin sha’awa a zobo sabo da Auta yayi maganinta amma kinga zobon Dana bata daban Wanda na sha daban amma ita gata lafiya ni Kuma yanzu wallahi Sha’awa nake ji ta bala’i,da Ahsan dinma zai zo shike nan, Rabin kauye yau zan iya yiwa mutum fyade,Nace kin tashi da kika bata lemon? Ae da ya kirani na kawo miki waya kin masa kwatancen,nace kinga kaikayi koma kan mashekiya Kai Cele da mugunta kike ashe Yara Zaki cuta ki sawa mutum maganin sha’awa Idan yayiwa yarinya Illa fa lallai Cele baki San Antena da azababa a farko wallahi da baki sawa yarinya karama irin Salma ba Kuma wai kika sake bata ta kaiwa Auta Kuma tace Auta ya sha lallai to Allah ya Ceci Salma kuma dan baki San Salma bane shegen rashin ji ne da ita da kwaikwayon tsiya yanzu haka naki ta gani kin sha tace itama shi zata sha ai haka take da kwaikwayo Idan wani yayi Abu tace zata yi saukinta ma bata kwaikwayon Halin banza sai na shirme ko gayu ko abinci ko wani abu dai na shiririta shi take kwaikwayo wlh ko raba Daya biyu karki yi naki ta gani ta shanye,Cele tace wash ta baje ta kwanta a kasa ku kunna min ac,idon Cele yayi kwal kwal kamar zata yi kuka,murya a sanyaye tace ni ki koya min soyayya ki Daina damuna da Surutu wlh yau abin kunya zanyi a nan gidan zanyi first night,Naci dariya nace wayyo Allah Cele zata mutu Ahsan maza ka karaso,Cele ta Miko min wayarta tace ungo Idan ya Kira ki daga Shima da shegen iyayinsa yaki ya karaso tun dazu a Ina ya tsaya ne oho,nace Cele tashi na koya Miki love,Cele ta mike zaune tana fifita local government da hannu tace inda kisan nayi Zigidir Rabi,Allah wadaran Halin su Star Yan bariki banza Yan barikin wofi ai sai su fada min Illarsa mugayen banza shegiyar Mandula tana tafiya kamar tsohon kunkuru duk sai naci ubansu daya bayan daya,Allah ya tsine musu mutanen banza mutanen wofi,dariya nake Cele tace harda ke Yan iska kwartaye ba abinda kuka iya sai iskanci,waccen kinibabbiyar Star harda da wani cewa suna sha ita da Abhulkhairi,Ita Kuma Wise tana make murya yana da kyau ai hakane kyan maganin ya Isa wlh in aka Saba akwai dadi sai ayi ta soyewa shegiyar murya kamar ta tsakuwa,ita Kuma Sera ko ba maganin nan ba ai Sabeer yana matukar sonsa,Yar Zabil nawa mijin dake yare ne ai bama free da shi, shegiya da murya kamar ta Devido,Kwartayayen banza wannan Mandula ta Daina ciniki daga yau Babu me sake siya zata gani,dauke biro da takarda ki zana local government din nan da Antena ki bani hadda bazan iya ba yau wlh abin kunya zanyi,mikewa Cele tayi tana Jan skert tana karkada skert dinta da hannu,sai da naji tausayinta yanda ta rasa sukuni nace da haka kike so Salma tayi? Cele tace wlh ko ba yau ba sai na bawa yarinyar tunda jifa ya fada kaina ya fada kan uban kowa wallah kika sake kema sai kinyi wani cikin kafin arba’in gwara ki kyaleni Idan Zaki koya min ki koya min,Mami tsaf zan iya bata ta sha Baffa ya kwashi gara,muka yi dariya tace to tsofaffin sai soyayyar tsiya wai harda ce mata honey a gaban mutane ku da suruka duk Yan bariki.

Nace to ni yanzu Cele me zan koya Miki? Uwarki Zaki koya min Idan iskanci ne ai Kun iya ,Nayi dariya nace Ahsan ne zai koya Miki Nima mijina ne ya koya min,ko me kika ga yanayi kawai ki masa,inda kika taba kika ga yaji Dadi shi Zaki yi har ku Saba,Cele tace to da biyayya, ta shiga wanka tace bari na shirya kafin Yazo naci dariya kamar me,na Kira Star na bata labarin ta tab reshe Ya juye da mujiya ta dinga dariya Nace yau kuna ta Shan zagi tace ai gobe zamu zo gashi rai fess wlh ko a jikina,Cele tayi wanka ta fito na bata Yan magungunan mata na niima da sauransu na hada mata da Madara ta shanye kuwa ta shirya ta zaro sabuwar rigar baccinta gantalalliyar rigar bacci me kyau dark green ta Saka na bata turaruka na daban ta shafa ko Ina lungu da Sako nace bafa daga zuwa Zaki afka masa ba nasan halinki ki daure ki ja aji,Cele tace Ina ajin yake wlh Babu,yo aji ai sai Makarantar boko yana can har da winduna da kofofi ni nawa a bude yake na bude kofofin ajin da winduna duka ke ceiling dinma na bare shi da rufin kwanon kango ne kawai, ke ni karki dameni fa kiji da danki shi Zaki wa fada ba ni ba baki haife ni ba.

Umma ce ta Kira waya ta mana gajiyar suna tace Cele fa,a hankali tace kice nayi bacci yau ko kaka Bai Isa na daga wayarsa ba sai masu abin bayarwa su Ahsan ,wayarta ce tayi ringing nace wa Umma tayi bacci tace to kice da safe ta kirani nace to ta kashe wayar .
Cele daga Kiran Ahsan tayi yace suna cikin gidan ma sunyi parking ta fito,Cele ta dakeni a baya da mugun zafi na dafe wajen tace Yazo banza ki tayani murna yana gidan nan,nace ki Daina murna Cele kuka zakiyi yau,Cele tace ni na tafi Yar bakin ciki sabo da ke ba dama Nawwar yayi shine kike kishi Dani,nace Allah sarki mu Antena Allah na tuba wanne kalar Vitamin ne nata bamu ji ba mu,kici gaba da shayar da danki ni na tafi ta Saka hijab har kasa a saman rigar baccinta ta fita
Tana fita ya hangota ya fito yana dafe Kansa,ciwon Kai yakeyi Bai Saba tafiya haka ba shi Kam sai yau,Cele taje a hankali tana cewa a ranta aji aji taho taho aji taho har ta karasa a hankali a ranta tace slow slow ta tafi a hankali ta rungume shi ba ayi gaggawa ba,ta masa sannu da zuwa yana ta murna har ya manta da ciwon kan ma,hancinsa me tsini ta ja masa tace sai yau? taki sakinsa ta makale a jikinsa Ahsan ana ta murna tunaninsa missing nasa tayi haka,ta kalle shi sama da kasa mamaki ya isheta ya dauki wankan shadda Dunkin Dan Dede shi cif cif me Hannun links farar shadda Kal yana kamshi harda coka hula a gaban goshi hular ma me kyau komai fari dama su akwai son farin Abu,Cele tayi dariya sosai tace duk dama wannan Shirin yake,yace wai ya taho da lefen a dakko tace ba yanzu ba sai anje gidan Iyaye ake kaiwa yace to,duk zancen nan da suke Cele tana jikinsa ta makale,ta leka suka gaisa da Hammad,tace Yazo su shiga yace shifa yayi booking hotel room Kuma securities zai Sallama su tafi sai gobe Hammad ma yana bukatar hutu, Cele tace gwara hotel din ma,tace ya sallame su Auta ya kaisu Hotel har Hammad duk ya Sallama yace suje da motaocin su bar masa Daya gobe zai Kira su,Shima Hammad hotel din da ya kama daban, mutane sunyi bacci ba Wanda yasan Yazo,ko ni nace da Safe ma gaisa.
Cele ta rike hannunsa suka tafi part din Auta shi Auta ma bai dawo ba,Salma ce a Palo tana kallo jiransa take yi su kwanta,Cele ta bude kofa suka shiga,Salma taga Ahsan tace lallai kice Ango yazo,Cele taja kwafa a ranta tace kunga yarinya fes da ita na gano ki Zaki ci ubanki,Ahsan ya dagawa Salma hannu da jagwalalliyar hausarsa yace Ina kwana,tace ai dare ne barka da dare zaka ce ah su Cele an dace oh yau kice mu toshe kunnenmu? Cele tace ke wallahi haushinki nake ji karki dameni karuwar yarinya sai kissar tsiya kamar ba rainon Namiji ba taja Ahsan suka yi gaba cikin bedroom Ahsan yace sai mun fito,Salma tace a fito lafiya chansa Cele chansa dai,Cele tace zamu hadu ne bari in sauke damuwata Zaki ci kwal ubanki,suna shiga ciki Cele ta nuna masa abincin tace ko zaka iya ci? Yace a’a shi baya cin wannan,Cele ta hau masifa tace ai kuwa sai Kaci fita nayi da nisa na Nemo maka a restaurant din larabawa kace baza ka ci,yace shi a lallai bazai ci ba ga larabawa da kafiyar masifa su basu san babu da tattali ba sam yace bazai ci ba,Cele ta Kira Auta tace kana Ina yace ya kusa da gida tace ka koma please ka nemowa Ahsan abincin larabawa ni na siyo masa irin rice dinsu da wata stew da naga suna ci yace shi a kasarsu ba irinta bace,Auta yace yo ba sai ki bar Dan banza da yunwa ba Idan yaji wuya tuwo ma cinyewa zaiyi wlh da kin sani tuwo kika masa ba a birge su fa kin sani basu san talauci ba,Cele tace please Auta wani aiki zaiyi ne sai yaci ya koshi,Auta yace da Daren nan a gidan mutane wanki zai Miki ko guga haba Cele ki dinga tausayin balaraben nan kullum ana nuna Miki hanya bakya ji,Cele tayi dariyar takaici tace Auta ka kiyayeni tam,Yace ko aikin magidanta zaiyi ne? Wayar Cele ta kashe ta rabu da Auta,Auta yana zuwa ya siyo sakwara da miyar Egusi da farfesun naman kaza me yaji,ya siyo gasashen kifi aka bade shi da wata miyar yaji ya kawo yace an samo,Cele tana murna tace shugo ku gaisa Auta ya shugo yace a’a sadaka yalla,tace wannan yafi karfin sadaka yalla,Annabin Allah a kasarsu yake,Auta yace dole na bashi girma,ya Mika masa hannu suka gaisa Ahsan yace ya Nigeria? Auta yace da sauki gamu a ciki muna ta hakuri,Cele tace jeka to ka tafi dakinku ka kama matarka kar na ganku a nan haka,Auta yace kallo zamuyi mu,Cele tace wai baka sha zobo bane Auta ya tuna Salma ta fada masa Cele ta bata zobo ta kawo masa amma ya subuce kofin ya fashe Idan sun hadu yace ya sha ya gode,Auta yace Ina ta so ma in Miki godiya zobo haka me dadin gaske na gode,Cele tace Kuma ba abinda kaji? Auta yace ni dai naji dadinsa gaskiya a bakina ya min kin iya Kuma thanks ya juya ya fice,yana zuwa ya ruko Hannun Salma yace muje Autar Auta,ta mike tana murza Ido na shagwaba wai bacci take ji, hannayen ya cjre yace muje I’m sorry aikena ake tayi na zama boy boy a gidan nan, Allah tun dazu nake jiranka ai kasan bacci nake ji,Auta yayi dariya yace sarki Yar Auta ni na bar Miki sunan nawa ma,mije yau tare zamuyi wanka,Salma ta zaro Ido tace ni nayi wanka na gaskiya suka shige bedroom.
Ni kuwa Ina kwance da jaririna kawai naji nono na Daya ya soke ni a ciki kamar an tsira min Allurai,a Daren nonon nawa ya fara ciwo guda Daya,na kwana Ina kuka na dinga Kiran Nawwar yana ta bacci,kafin safiya nono Daya ya kumbura sosai.

Auta wanka ya shiga Salma tayi Shirin baccinta yayi wanka da brush ya fito bacci yake ji Shima ya gaji,ya fito Salma me Miji ta zabo masa kayan bacci ta Taya shi shiryawa Yazo Saka wando ya jefar da towel Salma tayi tsalle ta fada saman gado ta rufe ido da pillow tace Dan Allah mene haka ai sai kasa ta dinga min gizo cikin dare tana tsoratani ai sai na dinga firgita ni kadai,yana dariya ya shirya yace kika ce Smally ce? a’a biggy ce wlh bacci Yazo ta kwanta harda baccin karya,Auta yace a Sannu sannu zanyi maganinki kawai Dan yau na gaji ne nafi so na kamaki a nutse in dinga yagarki Sala Sala wlh duk ranar da nazo tausayinki ko digo bazan ji ba duk sai na goge Miki raini kina tashi Zaki gaishe ni,Salma tayi dariya tace to zo mu kwanta ya haura Saman bed harda wani lafewa a jikinta,tace Auta yace na’am tace magana zamuyi me muhimmanci,yace Ina jinki duk sanda Allah yaso kazo yin abin nan da Antena muyi shuru kar wani yaji ka rufa min asiri Aunty Wise ta koya min yanda ake gashin nan Idan muka yi zan koya maka gashin nan kayi min abuna muyi shuru da bakinmu Dan Allah sai dai aga Ina da ciki,Auta yace tun yaushe na San yanda ake yi, cikin Shima muyi shuru Karka fada na sanka da Surutu Dadi ya kwashe ka sai ka fadawa Mami ba kunya ce da Kai ba amma Idan kayi shuru sai dai ayi ta hasashe ana cewa Salma ciki ne da ke Ina cewa a’a haba yaushe aka yi abin Ina basarwa Ina cewa karya ne sai dai aga ciki yana ta girma yana ta girma ana ciki ne Ina cewa sanyi ne munje asibiti sanyi ne akace ya kamani,kace kaima sanyi ne sai sanda karya ta Kare zasu San gaskiya Idan suka ga Abu kamar dutsen zuba rock yana tsiri,Auta ya sha uban dariya ya rungume Salma yace wacce irin mata Baso ya aura min ne? Fari tayi da Ido tace Salman Auta me abin mamaki,Kallon Auta tayi da wani irin Kallo tana lumshe ido tace Dan sammin bakinka,Auta yace Iyye haka kike dama? Salma tace wai mutum da mijinsa ko me yayi sai an masa mamaki ka bani Idan zaka bani, Auta yaji Dadi yace a ransa yace ni dama irin wannan nake nema shi yasa nake ta Neman babbar mace Sahar na godewa Iyayenki da suka hanani ke,a hankali suka fara tsoste tsotsen juna,Auta ya taba na shanun Salma yace nan fa? tace ai naka ne ka daina tambaya ma jeka kawai Babu doka da order a Kansa ka fa biya sadaki Auta me kake Jira ne,Auta yaji Kansa kamar ya tarwatse da baiyi niyyar sex ba yau amma zuga shi Salma take yi sai yace yau zaiyi a ransa ita Kuma ta saki jiki Auta bazai yi yau ba ya gaji bacci zaiyi ta dinga zuga Auta,duk ya hargitse komai yarda take ya taba Kuma ta dinga zuzutawa kenan sai kace Yar iska,sai da taga Auta jikinsa ya dauki rawa kamar ba karfinsa ba haka yake sarrafata ta fara jin wuya,sai ta sakko tace na gamsu ba uwar da tayi tace ta Gamsu.

You are so sweet my husband I love you so much ta rungume Auta kamkam tace ban taba samun nutsuwa ba sai yau my life, gaskiya kayi hadda a industry,Auta zaiyi magana tace uhm uhm ba sai ka gode min ba anything for you my love muyi bacci sai gobe Maci gaba,Auta ya tsaya kallon ikon Allah fafur ta hanashi magana kafin yace komai sai ta rufe masa baki tace Karka gode min ai banyi gwaninta ba sai nan gaba Idan mun nutsu zamu soye na gaske,Auta zai ce shi Ina wlh bazai yarda ba ta toshe masa baki da hannunta ta makalkale shi kamar Yar china da kyar ya banbareta yace ke ni Zaki yiwa bariki wlh baki Isa ba hakkina Zaki bani tab,Salma tace kace sai ka nutsu ya fututtuke yace na fasa ni Babu wata nutsuwa,Salma tace to zan maka ko mene ka samu nutsuwa amma kayi hakuri mu nutsu tukun da sauran baki a gidan nan, Auta yace ba wannan zance,tace daga yau nazo tayaka kwana shine zaka min haka Babu Amana abin shike nan ni zanyi fushi,Auta yace karki bari nayi zuciya Salma da abin nan naki Zaki jika ki sha ne,dariya Salma tayi tace ai zaka dawo ne tuni ma zan kalallameka sanda zaka dawo ma ka sani ne mu ai ba a fushi Damu ko anyi sai an dawo, Gyarawa yayi yace naga dai so kike mu gwada kwanji ko? Ya gyarata ya rike hannayenta tayi tayi ta kasa kwacewa, kafafunta ya tale ya danne da tasa kadan ma ya sa mata kafafunsa kar ta balle yace kinganki Salma duk abinda naga dama sai nayi a haka tayi tayi ta kasa ko motsi baki yasa ya janye pant din,Salma ta fashe da kuka kamar wacce za a yiwa Allura ka bari na gyara wayyo ka bari na gyara zan tsaya,Auta yace to karki ce daga yau Zaki min wayo duk abinda naga dama zanyi dake ko kina so ko bakya so,Salma da sauri tace na yarda,yace kawai dan da baki ne na hakura,tace to da sauri,yace sai Kuma kinyi min na baki tace to ya dagata ta mike tana godewa Allah bata so mutane su ganeta ita Kam,Haka duk abinda Auta yake so haka ta zage tayi masa ta samu Antena ya koya mata ta mata tass da bakinta ya samu nutsuwa ya zubar da abinda ya dame shi ya cikawa Salma baki taf ,ta tashi da gudu ta fada toilet ta zubar ta dinga kuskure bakinta tana kakari,Auta ya mata dariya ,ta dawo Salma tun daga romancing ta fara jin tsoro taga abin bana wasa bane aiki ne ja ashe,kwanciya tayi abinta tayi luf lakwas,tana jinsa yayi wanka ya fito,tayi sauri ta boye fuskarta kar ma yace idonta biyu,har ya shirya tsaf,yace baza ki wankan ba? tace ni me na ji da zanyi wanka, kika ce kin gamsu ai dole kiyi wanka ko Local government ban je ba kika ce ke kin gamsu, Salma tace kaji da shi bakina ciwo yake ya karye,ka balla min baki,kwanciya yayi yana nishadinsa ya dafa kanta ya girgiza Yan mata,taki magana ya kwanta ya jawota jikinsa suka shige bargo sai bacci.

Hajiya Cele kuwa ana budewa Ahsan Abinci taga Sakwara Auta ya siyo bakin ciki ya kamata,Ahsan ya leka ledar ya dauki sakwarar yana tambaya mene wannan? tace Wanda na aika ne ya siyo wannan ni yanzu ya zanyi da Kai kamar zata yi kuka Ahsan yayi murmushi yace zai ci ai dai ci akeyi tace ae yace ba damuwa ta zuba masa a plate ta Mika masa ya wanke hannunsa ya fara ci shi Kam ta masa dadi ya cinye guda Daya,farsun ya dauki nama Daya ya Dan lasa da harshe da sauri ya jefar yana zaro harshe kamar kare wai yaji ya rasa inda zai Saka Kansa yana subhanallah Subhannah,ruwa ta bashi ya sha da sauri,kifin ta duba taga Auta ya bari an bade shi da miyar jajjage tace sai naci uban Auta a gidan nan,ta sa spoon ta kwashe miyar tana zaro tsokar kifin inda ba yajin tana bawa Ahsan yana ci yaci yace ya koshi ya sha shayin data dafa masa irin nasu ya sha sosai ya sha ruwa yace ya koshi,da kyar ta takura ya sha fruits sannan yace su tafi hotel Kansa ciwo yake,Cele tace tab yau nufinsa bazai komai ba na roka ace ba aji wannan Dan Iskan aji Ina,sai ta dauki lemon tace tana zuwa taje ta digo masa maganin sha’awa a ciki kadan ta dawo ta damu Ahsan sai ya sha,ya gaji ya karba ya shanye,sai murna ta rike hannunsa suka fito mota suka suka shiga ta dinga Kiran wayar Auta yaki dagawa lokacin yana soyewa,ya gama suna kwance makale da juna suna bacci Cele ta hau dukan kofa kamar zata ballata,Auta ya taso da kyar ya Bude tace muje ka kaimu hotel ni bazan gane hanya ba,yace me yasa kika sa ya sallami driver dinsa shike nan ni baza a barni na huta da iyalina ba,rashin kunya zaka min? Auta yace gani nan to,kayi sauri fa tam ta koma motar,Auta da kayan baccinsa ya tashi Salma ta Bude Ido da kyar yace zan kai balaraben can Hotel,Salma tace Kai Kai da Daren nan 12am fa ta wuce,yace kiyi hakuri ai baki ne ya zanyi,Salma tace tsaya mu tafi tare na rakaka gaskiya ta zurma katon Hijab har kasa ta bishi suka tafi,Cele tace sai ka taho da ita,yace to ni kadai zan dawo fa suka shiga gaba ya karbi key,Cele da Ahsan suna baya Auta ya kaisu Hotel din da suka ce inda Ahsan yayi booking,tace da safe zan kiraka Auta yace to,ya juya da motar suka koma gida shi da Salma.

Mami tana ta jin mota na shige da fice a gida tace wai nikam gidan nan lafiya Ina jin hayaniya Kuma ga mota ta fita ta shiga,Baffa ya sake Jan bargo yace zai wuce Masu sunan tauraro ne sunyi da ai ba zaman lafiya,Mami tayi dariya.
Ni kuwa kwana nayi Ina jin zugi a nono,Kowa yaki daga waya bacci akeyi,da Asuba Nawwar yana yana tashi yaga uban Miss calls Dina yasan ba lafiya a gurguje yayi Sallah ya shiga mota ya taho gidan.

Cele Kam suna zuwa hotel room dinsa suka shiga ya shiga wanka,ta zauna a bakin bed tana karkada kafa ita tasan me take ji kawai,Hijab din ta cire gaba daya surarta me matukar kyau da birgewa ta bayyana ko Ina a waje gasu nan,Ahsan ya fito a wanka yana kallon Cele shike nan ya birkice lissafinsa ya canja gaba daya,fasa ma shafa Mai yayi ya shafa turaruka kawai hankalin kowannensu a tashe yake dama kadan yake Jira bare Kuma an Kara masa da magani,Cele ya nufo ta dora kafa Daya a gado Daya a kasa tana kallon kaurinta kawai,Hannunsa ya Dora a wuyanta ta baya Cele ta wani lumshe ido,a bayanta ya zauna ta Maida kanta kirjinsa ta kwanta bata San ma ta iya slow din ba sai gani tayi tana yi,a hankali ya juyo da ita Suna facing juna Cele ta tafi gaba daya kissing suka fara na juna a hankali sai ga Cele ana ta slow motion ba damar tsayawa ayi iskanci,ajiyar zuciya suka saki lokaci guda sanda ya janye rigarta ya fara shafa na shanunta Cele tace wayyo Allah Kai maye ne ka hadu,Ahsan bai San mene maye ba,yace Maye? Mean what? Cele tace Gentle man,yaji Dadi yaci gaba da sarrafata yana murza dukiyar fulaninta Cele tace fantastic, yana Dora bakinsa a Kai tace Interesting,yana lashe ko Ina na sassan jikin Cele tace wannan shine General check up karya kuke likitoci a nan ake check up, ya gangara zuwa cibi Cele a hankali tayi baya ta kwanta rasha rasha taji Dadi tace Impressive,yana zuwa kasa ya janye dan kanfai Cele ta furta Sensational, Overwhelming, Brilliant,tana shidewa tace breathtaking,ahhhhh shiiiiii phenomenal, shi Kansa Ahsan yanda take bada amsa da baki tana yabawa dariya take bashi duk Abu daya sai ta Sako kalma duk ta haddace kalmominta da yawa dake ba boko tayi sosai ba shi yasa bata turancin amma kalmomi ta iya da yawa ba laifi,yana Dora baki a local government magana ta gagara sai kukan Dadi da ihu,Ahsan yaga abinda yake so ba irin Maheerah ba sai anyi amfani da sex gel sometimes ba niima amma wannan yaga sai ambaliya take,Shima yace first class lady, Charming, delightful,my Angel,Cele ya shiga koyawa yanda Shima zata sarrafa shi babu musu ta shiga yi Shima yana mata yanda kowa yake so yana jin Dadi,sai Nishi da kukan Dadi suke har Ahsan da samun wake Cele wai ta masa sucking saura kadan ta cije shi ya janye ya fece da sauri,Cele ba a koya ba,a hankali ya dinga koya mota yanda akeyi ta danyi kokari yace good,a nutse ya shigeta da kyar ya sha wahala shi Kansa kafin ya samu hanyar ya fada,ga magani na fusgarsu Allah yasa ma ba irin haukacewar nan yake sawa ba indai kabi ka’ida mood kawai zai Kara maka da son abun sannan a Dade ana yi,Cele ta gwada kwazo da dauriya tuni abin ya fita kanta tunda ya fara take kokarin ture shi,Ina Sam Sam,Allah ya taimaketa kadan ta digawa Ahsan bai Kai na su Salma ba da ta Saka amma duk da haka ta gurzu iya gurzuwa sai da tayi kamar zata mutu,duk da haka shegiyar ko hawaye bata yi ba Babu digon kuka Kuma tafi Rabi Shan bakar wahala sabo da nata akwai magani a ciki bazai yi da wasa ba,Yau ta sha larabci Babu yaren da yayi Wanda zata gane face ihunsa amma larabci ya dinga yi yana ta yabo da sambatu da kukansa gaba daya, Ahsan balarabe Babu wuyar kuka akan dadi harda kuka,Cele tace me na maka kaga Dan sharri ni banyi kuka ba sai Kai,dama haka kake Ahsan da sharri,Kai kaga mutum na shiga uku daga Abu,rungumeta yayi ganin tana mamakin Hakan yayi dariya ba Shiri yana sa mata Albarka yana yabonta da Hausa yanda zai iya,Cele duk karfinta kasa tashi tayi a lokacin,tace da karfina na gagara tashi ni Cele yau naga Masifa,tayi tayi sai zafi ta kwanta ta Maida kanta saman pillow tace Allah ya rabani da samun ciki a garin nan nasu Rabin kauye kar naje na haifo me kama da Peter Obi.
Ahsan yace karta damu ta huta zai mata komai.

Nawwar da Sassafe ya shigo dakina yace mene ne na ganki a zaune? Na fashe da kuka na dage masa rigata nace ka gani,ya taba yaji ya dau zafi ya kumbura,yace Subhannallahi, miracle nace Ina tsoron cancer yace kinga wasu fa dama suna yi farkon haihuwa kiyi hakuri ya rungumeta tana ta kuka Mami ce ta shigo,tace Lafiya na dage Riga nace Mami zo ki gani,Mami tace a’a nazo ni da Idan za a shayar da yaro ake kulle kofa a sa key me zanzo na gani ku Kalli abinki ke da Mijinki,Mami ta dauki hanyar ficewa nace Dan Allah Mami kizo ki gani,zo ki kalla na daina boyewa ,naci gaba da kuka, fafur Mami taki zuwa,duk wacce ta shugo Kun gani kuzo ku gani Ina kuka,Ina ta talla da nono yanzu,Wasu har dariya sukewa boyo na,Nawwar yace to su ba cire Miki zasu yi ba fa,bari nazo mu tafi asibiti,Auta ne ya shigo sunci gayu shi da Salma yace me jego lafiya? Nace Auta Ina kuka zo ka gani Auta yace cuta ce dai amma zanyi dariya Rabi nan kike kulle kofa Zaki ba danki nono yau gashi har da mu a kallo a sadaka,Nace kowa ya kalla kuzo ku ga yanda yayi wayyo Allah,Auta ya Dan leko yace Kai Kai Kai Ringim sunan wani gari na sake rushewa da kuka,yace ke kiyi shuru Dan Allah nasan inda ake bada magani na gargajiya Allah Kuma yana yi,nace to to to na gode,Auta ya fice Salma tazo tana lallashina nace Salma dagashi kiji, Salma tasa hannu biyu tace Kaiiii Rabi Nauyiiiiiiiiiii,Na sake fashewa da kuka nace ku Kira min Baffa ya gani,Salma ta fita da gudu Baffa kazo Rabi tana ciwon nono kazo ka gani,Baffa yace Allah ya sawwake za a kaita asibiti da wajen magani,tace kazo yace ke gidanku tafi ki bani waje,Salma ta dawo da gudu tace yace za a kaiki wajen magani,Ina kuka na hada zufa dama gani da kwailo, Bilkisu ta shugo tace mufa yau zamu tafi zamu bar Miki Cele da Omaira,Nace bakwa kaunata tafiya zakuyi ku barni a wannan Halin,Su Star duk na kirasu a sai ga Wise nace taho ki gani Nawwar da shigowarsa kenan yace na shiga uku Kowa sai ya gani,Salma tace har Auta,ya ja tsaki yace me yasa baki da tawakali daga ganin fa,wayyo a kaini asibiti anki ba a Sona sabo da na haihu na tsufa bani da amfani a wajenka,Nawwar yace tashi mu tafi Idan munje asibiti su cire miki tunda baza kice Allah ya yaye Miki ba,Ai nace Allah tun jiya,yace muje,yace bari na dakko Abdullah,ni bazanje da shi bazan sake bashi nono na ba.

 

Masu sharhi ayi ta yi.
na gode zanzo nayi replying.

 

 

AsmaBaffa
[8/22, 10:06 PM] +234 703 366 3239: ‘YAR AIKIN KARUWAI 2
MATAFIYA

BOOK 2

81-85

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA GA
ZAINAB USMAN

 

*MISKI 3in1 Alfirdaus* Albishirinku original miski daga *Egypt* miskin da koda yaushe Kuna yabawa dashi yana dauke 1.*Musk oil* ana shafawa agaba bayan gama al’ada inda hali za’a iya ringa sawa Koda yaushe yana maganin infection yana gyara gaban mace sosai ko yaushe gurin yakasance cikin kamshi bayaga haka sunnah ne amfani da miski
2.*Musk cream* Ana shafawa ajiki gaba daya musamman wajan cinyoyi yana sa jikin mace koyaushe yakasance cikin kamshi kuma yana gyara fata, yasa tayi laushi
3.*Turaren tsarki* wannan turaren karshe ne ba lallai se bayan gama period ba koda yaushe zaki iya rinka tsarki dashi yana gyara gurinnan sosai, kuma ana shafawa a hammata yana kawar da da wari karku bari abaku labari ‍♀️‍♀️

Masu bukata ku ne wannan number
09065959708

Page naku ne

MASOYA WANNAN NOVEL

 

 

 

Back to top button