Cuta ta Dau Cuta Hausa NovelHausa Novels

Cuta ta Dau Cuta 3

Sponsored Links

*_Typing_*

 

 

 

*_CUTA TA ƊAU CUTA_*
_(Ɓarawo ya saci akwatin maciji)_

 

_ _

 

_Shafi na uku_

 

……..Da murnarsa ya shigo gidan yana faman washe baki. Tun a farkon tura ƙofar soron gidan yake ƙwala kiran sunanta tamkar mai shela. “My Queen! My Queen! Kina ina ne? Wai nikam. Fito! Fito ki gani fito My Queen!!”.
Har cin tuntuɓe take wajen saurin fitowa da ga bayin, tsabar yanda ta fito a rikice saboda kiran da yake faman ƙwala mata bama tasan da botikin wankansu da akoda yaushe yake a bayin ajiye ba ta fito. A ƙaramin tsakar gidan da bai wuce cin tabarma biyu ba sukaci karo. Kafin ma tace wani abu yayi wani kalar jawota ya rungume tare da ɗagata cike da farin ciki ya shiga juyi da ita. Ɗan ihu ta fara mara sauti tare da roƙon ya sauketa tana faman ɓoye fuskarta cikin jikinsa. Shiko duk da yasan bata son hajijiya sam bai sauketan ba, sai faman dariya ma yake abinsa yana cigaba da juyinsa. Sai da yay mai isarsa sannan ya afka ƙofar dake kusa da su, falone matsakaici dan kujerun da aka ƙawatasu da shi ma a mugun matse suke. Tsakar falon kuwa bai wuce girman sallaya ba, direta yay a saman doguwar kujerar yana hakki. Itako ta sake ƙanƙamesa har yanzu fuskarta na jikinsa. Sai da kusan mintuna biyu suka shuɗe taji hajijiyar ya saketa kafin ta ɗago kaɗan tana tura baki da kwaɓe fuskan tamkar zatai kuka.. a shagwaɓe ta ce, “Haba Husby so kake kaga bayana ne?”.
Dariya ya ƙyalƙyale da shi, cike da nishaɗi ya furta, “Ai mai ganin bayanki sai kin juya My Queen. Wlhy wani farin ciki ne na shigo da shi wanda na tabbatar idan kika jishi yau ƙyautata sai ta kasance ta musamman ne”.
“Woow Mijina bani nasha mana”.
“Ai dole kisha kuwa Matata, sarauniya ta, dan haka rufe idanunki”.
Ruf ta sufesu murmushi na sake ƙawata kansa a black beauty fuskarta mai wani irin sirrin laushi da sheƙi. Ga ɗan ƙaramin bakinta da yafi komai ƙawata sirrintaccen ƙyawun nata. Hannunta na dama ya kamo cikin nasa, yana cigaba da murmushin ya ciro abu a aljihunsa ya saka cikin hannun nata ya rumtse yana faɗin “Zaki iya buɗewa”. Buɗewar tai da sauri tare da ware tafin hannunta, ta ɗan zubama keys ɗin idanu zuciyarta na wani irin rawa-rawa. Sai kuma ta ɗago da sauri tana kallonsa da girgiza kanta. “Husby ka ɓaddani ALLAH. Keys ɗin miye haka?”.
Ido ɗaya ya kashe mata tare da jawota jikinsa ya rungumeta har zanin dake ɗaure a jikinta na kwancewa. Basu damu da hakanba su duka, suka ƙanƙame juna. A cikin kunnenta ya gwargwaɗa mata maganar da ta sakata ɗagowa da sauri tana kallonsa idanunta gaba ɗaya a waje. Cikin rawar lips idanunta na ƙiƙƙiftawa ta furta, “Naka fa Dafeeq?! Taya hakan zata kasance bayan nasan ko key na keke bamu da hanyar samunsa a gidan nan balle mota har ma da gida”.
“Ikon ALLAH kenan Deejoh na.”
A hankali ta ce, “Hakane. Sai dai komai ai yana da sila. Tayaya hakan ta kasance?.”
“Karki damu zan sanar dake komai. Amma fara mun haƙuri naɗan watsa ruwa ki bani abinci kuma naci. Dan yunwa nake ji ALLAH sosai. Banci komai a cikin nan nawa ba tun karin da mukai da safe”.
Duk da zumuɗin son jin da take haka ta daure ta danne. Cikin ƙarfafa kanta da ture abinda ke tsikarin zuciyarta ta miƙe tana murmushi. Fita tai a falon, babu jimawa ta dawo. Kusan a tare suka ɗaga labule, dan haka ta ɗan jaye baya ta bashi hanya. Fita yay yana sakar mata murmushi, ta maida masa murtani cike da son ƙarfafa kanta. Numfashi mai nauyi ta sauke lokacin da take sake kaiwa zaune a kujera idanunta akan keys ɗin nan dai. Ta kafesu da ido zuciyarta na ci gaba da kai-kawo. Haka kawai take ɗan jin kamar tsoro a ranta, sai dai bata san dalilin hakan ba, domin a zahirance ba tsoron ya kamata ace tana ji ba, murna ya kamata ace tafi kowa da wannan alkairin da ya samesu. Badan komai ba sai dan tuna baya, tuna baya akan rayuwarta da Dafeeq kafin aure, tuna baya kafin zamowarsu ƙarƙashin aure. Tuna baya bayan zamowar tasu ma’aurata har zuwa yau ɗin nan da suka wayi gari a matsayin da suke kafin wanda ke neman canjasu a yanzun nan…
Sunanta shine Khadijah, ɗiya ta farko a wajen iyayenta. Tana da ƙanne huɗu duk mata, sai namiji ɗaya daya kasance autansu. Mahaifinsu ba mai kuɗi bane, sai dai mai ƙarfin hali ne da wadatar zuci. Wannan imanin nasa ya sakasu tashi a gidansu matsayin ƴan gata, bama gidansu kawai ba har a cikin dangi da yaran anguwa sun kere tsara. Dan komai mahaifinsu tsaye yake wajen musu dai-dai ƙarfinsa. Hakama mahaifiyarsu tana nata ƙoƙarin da sana’arta ta saida kayan sanyi da kayan miya irinsu kuka, kuɓewa, magi, gishiri, daddawa. Kai duk dai wani nauyin kayan miya na gargajiya zaka samesa a wajen mahaifiyarsu. Dan haka gidansu ya kasace ɗaya daga cikin gidaje da ake zirga-zirga na sayayya. Ƙoƙarinta da ƙwazo a makaranta ya sakama mahaifinsu burin ganin tayi karatu mai zurfi ita da ƙannenta, amma kasancewar itace babba sai ya zam ita aka fara ƙoƙarin ginawa. Lafiya lau ta kammala primary ta shiga secondary ɗin dake ƙasan layinsu ta ƴammata, sai dai makarantar iyakarta jenior ce. Wato iya aji uku. Matuƙar ƙwazo da himma ta bada a karatunta, inda ta kasance ɗaliba mai ɗaukar first class a ajinsu tun daga jss 1 har zuwa jss 3. Sun zana jsce cikin nasara da jin kewar rabuwa da makaranta, musamman ita data kasance mai farin jinin malamai saboda ƙwazonta. Dan randa akai musu walimar fita ta samu ƙyaututtuka daban-daban da suka saka iyayyenta farin ciki tare da sake jin ƙaimi akan tsaya mata cigaba da karatu. Sun ɗanyi zaman gida har jarabawa ta fito, inda ta samu nasarar samun wata makaranta dake can wata anguwa, sai dai ita haɗe take ƴammata da samari. Makarantar babbar makarantace dan duk ɗalibin daya kasance a cikinta sai mai ƙwazon gaske. Saboda akan tsinto yara ne masu ƙwazo sosai daga makarantu daban-daban zuwa nan a duk shekara, itama ƙwazonta ya bata wannan damar. Tayi farin ciki matuƙa da zamowarta ɗalibar wannan makaranta mai farin jini da kowa ke fatan ganin ya sameta, hakama iyayyenta sunyi murna mara misali. Anan ɗin ma lissafin bai canja ba, dan ta matuƙar dagewa a tarm ɗin farko itace ta ɗauki ta ɗaya a ajinsu, ta kuma sami ƙyautar yarinya mai tsafta da kuma rashin yin latti. Iyayenta sunyi matuƙar farin ciki tare da ƙara ƙarfafata, dan har ƙyauta baba ya mata ma, hakama Inna ta siya mata kaza guda ta soya mata tace taita ci har ƙannenta na kukan an nuna musu wariya. Ta gama ss1 lafiya, a tarm ɗin da suka shiga ss2 komai ya fara, dan shine farkon labarinta tsakaninta da _Dafeeq Abubakar Ja’e_…….

★★★★

A hankali yake buɗe idanunsa da sukai wani masifar nauyi. Da sauri ya ɗan rumtsesu ya sake buɗewa again. Sai dai yanzun ma dai a hankali yake motsasu. Fankar dake juyawa kaɗan-kaɗan ya zuba ma su na tsawon sakanni goma. Tun yana kallonta dishi-dishi har idanun nasa suka fara gani tar-tar. Tabbas ba gidansa bane, dan anan ɗin normal selling ne saɓanin gidansa da akaima sabon lafiyayyen p.o.p da yasha fitulu. Sake ware idanun yay da ƙyau tare da motsa jikinsa, jin hannunsa na dama yay masa nauyi sosai ga zafin daya ratsashi saboda fisgar da yay masa ya sashi ambaton “Wash ALLAH na”.
A karo na farko duk wanda ke ɗakin suka juyo garesa, sai kuma duk suka zabura kowa na ambaton sunansa. Idanunsa ya sake buɗewa da ƙyau yana binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya. Mahaifinsu ne, sai yayunsa biyu da abokinsa MB da SJ, sai ƙaninsa guɗa ɗaya. Jin yanda suka rufesa da tambaya da sannu ya sashi motsa bakinsa da yay nauyi a hankali ya furta, “Abba ina ne nan ɗin?”.
“Asibiti ne Jazool, an kawoka ne baka da lafiya tun jiya”.
Yayansa ya bashi amsa cike da nuna alhini da tausayawa. Da ɗan sauri JJ ya dubi hannunsa, ganin ruwa ake ƙara masa ya sashi yarda da zancen yayan nasa. Ƙoƙarin tashi yake zaune sai dai ya kasa, cikin sauri MB da yayansa na biyu suka kamashi. Zaunen suka tadashi, tare da jinginasa jikin bango da Nuhu ya gyara filo suna cigaba da masa sannu. Kai kawai yake iya gyaɗa musu shi dai, ransa fal mamakin miya kawosa asibiti shi kam.. Idanunsa ya rufe ruf, tamkar wanda ake sarrafawa da remote sai kuma ya buɗe da sauri jin abinda MB ke faɗa…
“Sannu kaji abokina, gaba ɗaya ka ɗaga mana hankali, amarya da ya kamata ace ita ke jiyya sai kuma kai a naku labarin amarcin ya juye kaine kwance a gadon asibiti? Ni dai ALLAH yasa ba pills ɗin dana baka bane ya jawo maka wannan bala’in tun jiya ake abu ɗaya kamar bazaka rayu ba”.
Rawa jikin JJ ya farayi, ya ɗan juya ya dubi sashen da Abba da Yayunsa suke, can ya hangosu a bakin ƙofa alamar magana sukeyi, sake maido idanunsa yay kan MB da SJ dake tare da shi kawai. Muryarsa na ɗan rawa ya ce, “Yaushe aka kawoni nan? Waye kuma ya kawoni?”.
SJ ne ya bashi amsa yanzun kam da “Tun jiya da safe aka kawoka. Amaryarka ce kuma tai kiran Rabi’ah tana kukan cewar azo a taimaketa ka mutu kamar yanda Nuhu ya sanar mana. Hankali tashe su Yaya Mujee suka nufi gidanka. Inda aka taddaka yashe a ƙasa baka numfashi kuma duk an jimaka ciwo a fuska da jikinka kamar da farauta, itama amaryarka jikinta duk jinin da yake biyo mata ta hanci da gefen baki alamar dukanta akai…”
Da wani irin gudu abinda ya faru tun daga barinsu gidan zuwa komawarsa ciki ya shiga dawo masa. A take jikinsa ya fara kakkarwa. Muryarsa dake a disashe na rawa ya ce, “Duka? Ita Alimah ɗin?”.
“Ƙwarai da gaske, dan tare ma aka kawoku asibitin nan, sai dai ita tun jiyan aka sallameta bayan Doctor ya dubata sosai, ya kuma tabbatar da marinta akai bakinta da ya fashe, jinin hancin kuma haɓo ne tayi. Kaiko an yayyageka da farauta ne aka jijji maka ciwukan nan. Dalilin sumanka ne dai har yanzu basu ce komai akansa ba, dan jiyan ma da ƙyar aka samu ka farfaɗo kusan sha biyun dare, shine sukai maka allurar barci sai yanzu ne kuma kake farkawa”.
Cikin rawar lips mamakin zantukan MB ras akan fuskarsa ya buɗe baki zaiyi magana, sai dai shigowar likita tare da Abbansa da yayunsa ya hanashi cewa komai. Duk fita likita yace suyi, yayinda shi kuma ya shiga duddubashi yana jera masa tambayoyi akan yanda yake ji a yanzu. Da ƙyar ya iya bama likitan amsa da cewar shi yanzu baijin komai, sai kansa da yay masa nauyi da kuma mararsa.
“Insha ALLAH suma zasu sakeka. Ciwon kan normal ne na daɗewa da kai a sume. Na maran ne dai ƴar damuwa itama kuma bamai tada hankali ba. Da ka samu kasancewa da matarka zaka koma normal. Pills daka sha ne suka haifar maka da hakan. Amma sai ka kiyaye gaba dan bincikenmu ya tabbatar mana daka jima kana amfani da irinsu, hasalima ƙarfin maganin da rashin sauke nauyin da suka saukar maka ne ya haddasa maka sumar nan kayi kuma nauyin farfaɗowa. Ka godema ALLAH ma kuma da baka samu haikema yarinya a wannan yanayin ba tunda naji ance amarya gareka, dan ƙarfin maganin nan zai iya sawa ka mata babbar illa musamman idan ta kasance virgin. Dan ALLAH ku dinga bincike akan abu kafin kuyisa, dan hakan wautace sosai. Musamman idan mukai dubayya da su yaran da ake kai muku basu san komai ba, binsu a hankali akafi buƙatar kuyi tunda al’amarin ba damben gwada ƙwanji bane ba. Kaga gashi nan wajen ceton kanta ta jijji maka ciwo itama ka jimata ciwon ta hanyar marinta da kayi. Hakan ai kaga baida amfani sam a daren farko fa kuma….” Likitan ya ƙarasa maganar cikin zafi-zafi. Shi dai JJ kallonsa kawai yake kansa a wani irin juye. Dan gaba ɗaya yama gagara auna maganar doctor ɗin a muzubin hankali kona fahimta. Shi harma a yaushe yay yunƙurin yin wani abu da Alimah. Ya san dai yasha pills kam tabbas, yana kuma cike da ɗokin yin shagalinsa, amma bai ko ɗau hanyaba. Kai shi bama wannan ba fa, abinda ya faru tsakaninsa da Alimah ɗinne abu mafi girman ɗaga hankali da buƙatar yin tunani, sai kuma yanda yaji labarin na neman canja kansa zuwa wani bigire daban a bakin wannan likitan. Ɗan zabura yay zai sauka a gadon har yana buge likitan. Da mamaki ya ɗago da ga rubutun da yake ya dubesa, ganin yana neman direwa a gadon yay saurin riƙesa da faɗin, “Ya ALLAHU! Lafiya kuwa?”.
“Babu ita Doctor, Alimah nake son gani”.
A halin da JJ ke ciki da yanda Doctor ya fahimci al’amarin akwai banbanci, dan haka yay murmushi yana ɗan laɓe bakinsa. “To baban soyayya kwantar min da hankalinka nan Please. Indai amaryace yanzu zaka ganta har nan inda kake duk da ma dai zamu sallameka ne muma kaje gareta a yau ɗin nan in sha ALLAHU kaji”.
“Doctor plea….”
“Shiii!!!” doctor yay saurin katsesa. Daga haka ya juya yana fuskantar ƙofar da faɗin, “Zaku iya shigowa”………✍️

_To JJ dai ALLAH yasa kar a nuna hali anan ma_

https://chat.whatsapp.com/ImF9JpXmBISJCvMBGkTKLc

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu _*

Back to top button