Hausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 70

Sponsored Links

70
Mutuwar bokan Jin sukai gwara ace Wani jininsu ne ya mutu,
Safnah tawar jiki ta ringa zubawa tana Neman kamuwa da ciwon zuciya Dana qwaqwalwa.
Wuni biyu da kwana daya sukai babu me cikakken hankalin kama Wani tinanin duk da sun San komai rintsi dole Wani hanyar zasu
Kuma samowa tinda ba tsayawa zasuyiba su rissina.
Cikin baqin ciki Safnah dake zaune palo ta Kalli momy idanuwanta jajir tace
“Momy dole cikin gaggawa fa zamu San abin
Yi,
Ina cikin hadarinda kowane lokaci wlh Bena zata iya ganina,
Tsawon shekarun Nan Muna auren miji Daya nida ita, Nazo na tare gida Daya nida ita tsawon lokaci
Muna guri Daya Muna rayuwa rabo da Sa’a yasa bamu taba ganin juna ba sbd Allah Yana
Sona yasa ko a yanxu din nice na ganta Bata
Ganni ba,bansan tsawon Wani lokaci Saar Nan zata bini ba,
Kada sa’a ta tayanke batareda munyi Shirin hakanba,
A baya banajin komai nake rayuwata sbd tinanin suna can cikin rayuwar Dana barsu acikinta bantaba tinanin ko a masu aikin irin dunivarsu Kaantes zan samu Daya daga cikin yan uwanaba shiyasa na sake bana shayin komai Dan nasan duniya biyu mabanbanta muke rayuwa ni da su,
Momy wIh tallahi asalina na bayyana Ababa salya mun ratayar da bazan mutu ba bazan rayu ba,
Momy sunan Ababa kawai idan na Tina bana iya Jan numfashi batareda azabtacciyar tsoro da tashin hankali ba..
Cikin tata masifar data addabi zuciyarta momy ta katseta da jajayen idanuwanta itama tana cewa “So nawa zan fada Miki ki Dena Kira mana ranar tonuwar asiri?
Kin manta inda dukkanmu muka fito?
Ni kaina anfada Miki ko rayuwar Dana fito a baya Ina bugatan tinawa bare fatan komawa
Wallahi bazan yarda na koma ba,
Asirin da kike magana akansa idan ya Toni nice zan fara kwabewa nabi hanya da hauka kafin ke,
Mutuwar Bashara ba snine karshenmu ba,yanzu ne zamu tashi tsaye muyi Aiki da qwaqwalwa da qarfin zuciyarmu,
Waye Benazir da zata kashemu da ranmu tsaye?
WIh ba Bena ba ko ‘yarta sai mun janye sbd kada ta tafi ta barmana baya da qura sbd yanda Dawood Bai iya hada komai da kowa da yar.
Cikin Dan Jin sassaucin zafin dake cinta
Safnah tace “Daman Banda niyar a bar ‘yar,tabi uwarta su tafi sbd barinta na nufin inada sauran alaga da dangina na baya”
Cikin zurfafa tinani sosai da tabbatarda cikin biyu bazasu yarda su rasa duka ba momy ta sake juyawa ta juya tinaninta tace
“Ko zamu rasa komai na bulama bazamu yarda mu rasa DD ba sbd idan muka rigesa ta
– hanyarsa zamu tsira daga sauran tonan asirin
Cikin bagin ciki sabo Safnan tace
“Tayaya bayan kallan namiji yakemun,
Wata na nawa a gidan Bai taba barin ko kalan gadon Dayake dakinsa na sani ba bare shiga,.
Wallahi wannan tafiyar da yayi dole kafin ya dawo muyi shirinda babu Abinda zai hanasa bani matsayin matsarsa. Jiniina Kai momy tayi tana cewa
“Wannan matsalar na gama da ita sbd sakonmi Yana hanya,
Idan kika ga ya dawo Bai mayar dake matarsa ba to wih ba namiji bane mace ne kokuma
•babu mazakuta a jikinta,
Maganin biyu ne dayan na bulama ne zamu aje Incase,
Idan asirin gaskiyarmu na ke ba jininsu bace ya kusa bayyana aikasa kawai zamuyi batareda sanin kowa ba ko Ganewa kowa a gama zaman gaisuwa a raba gado a kwashe
Rabi a baki matsayin yarsa qwalli Daya mu San da Benazir din zamuii mu huta.
Sai alokacin Safnah taji sanyin ranta ta sauke ajiyan zuciya da numfashi a tare tana Jin sauran hope da nutsuwa na shigarta ta saki dariyan Jin dadi da farin ciki zatayi magana idanuwanta ya sauka kan hajiyarsu dake kofa tsaye kaman ta Suma tana kallansu hannunta riqe da wayar data gama da Umme akan safnah Bata sanar dasu zata koma gida ba ta taso tazo Dan yiwa safnan fada kunnuwanta suka Jiyo mata Abinda yafi karfin rayuwarta da tsufanta.
Ganin kallan da Safnah kewa kofa idanuwanta na Neman fadowa qasa jikinta duka Yana
• daukan rawa ya saka momy hadiye tata dariyar ta juya taga hajiya tsaye tana kallansu.
Hawaye ne kawai suka gangarowa tsohuwar ta Kalli momy bakinta na rawa zuciyarta na radadi tace
“Me kunnuwa na suka jiyemun Nuratu?
Balain da masifar da muke ciki kenan bamu sani ba a hannunku.
Kallan juna sukai tareda nufota Safnah na
cewa “Hajiya bakiji daidai bane ba…
IIA
Wani gigitaccen Mari ta saukarwa Safnah din
Daya sakata kifewa qasa ta dago idanuwanta nayin ja ta Kalli hajiyar zatayi magana momy tace
“Yanzu da kikaje hajiya to me zakiyi?
A zafafe ta Kalli momy tace
“Zakiga Abinda zanyi”
Juyawa tayi tana Bude wayarta Dan saka kira ko taku biyu batayi ba momy ta dauko garamin glass stool din dake palon me shegen nauyi ta daga da qarfi ta kwada mata bayan kanta
Saida glass din ya fashe duk nauyinsa. Cak hajiya ta tsaya kaman Bata daku ba ta Dan motsa kadan wayar hannunta na faduwa qasa jini ya fara zuba da garfi ta Yanke jiki a gurin ko waiwayowa batai ba.
Da sauri jiki na rawa Safnah ta tashi tana kallan hajiyar kafin ta Kalli momy muryanta da-jikinta na rawa ta ce
“Momy idan Bata mutu ba zata fadawa dady da kowa gaskiyar Abinda taji,. Kuma ya zamuyi yanzu da ita Idan aka sameta anan haka zaa ce mun kashe,innalillahi,momy wlh banason zuwa prison,momy Bena zata samu DD ni Ina prison, Dan Allah momy ki.
Tsawa momy ta daka mata tana cewa
“Haukarki zata saka asan munyi Wani abin ki nutsu babu Abinda zai faru damu.”

Safnah na Jin Hakan tayi shiru suka kama hajiyar zuwa bakin kofar shigowa palon suna ajiyeta kwance kanta daidai kaifin stairs.
Wayarta Safnah ta dauko da sauri bayan ta saka hannunta leda kadama Wani abin ya biyo
baya a ga hannunta a jiki.
Cikin hannunta suka Bude suka saka mata wayar.
A tare suka koma palon suka share glass din cikin sauri bayan sun share Sabon towels uku suka dauko suka goge jinin Daya zuba suka zuba tirarika da kayan qamshi sosai.
Glass din dasuka kwashe toilet sukaje sukai floshin nasa towels din Kuma a cikin toilet momy tahau konesu itama Safnah ta fito ta tsaya kan hajiyar ta kwada Wani irin ihun Daya saka masu aikin gidan kaf fitowa tafara ihu tana cewa hajiya ta Fadi a stairs da sauri aka fara salati ana ihun Kiran sunan hajiyan.

Momy kuwa a cikin toilet kaman hayagi zai kasheta haka ta Kone towels din tsaf ta Bude window hayaqi ya fita ta wanke toilet din tas da kanta ta fesa tirarika ta fito
Lokacin tini driver da Safnah dake Kuka suka kwashi hajiyan zuwa Asibiti.
Hankali tashe masu aiki sukaiwa mom data tambayi meke faruwa taji hayaniya tana toilet.
Tanajin haka itama hankalinta ya tashi ta zari mota ta bisu Asibitin tana saka Kiran bulama ta sanar masa hajiya ta Fadi a stairs bayan kanta ya bugu anyi asibiti da ita.
Hankalinsa tashi yayi sosai gashi Yana porthacort Dan haka Shima Umme ya kira ya sanar mata.
Koda aka Isa asibiti da hajiya ko dubata baa fara Yi ba Rai yayi halinsa take Safnah ta ringa
Kuka tana rusa ihu,
Momy ma haka ta ringa kukan tana Kiran sunayen Allah a baki.
Umm Koda ta iso Asibitin tareda Zeenah hajiyan ta Riga ta rasu Dan haka sai kawai ta
Yanke jiki ta Fadi.
Daukanta Akai aka shiga emergency da ita
Bata taimakon gaggawa.
Su Safnah kuwa shiga taitayinsu sukai suna
Kuka suna waige waige sod fargaba da sanin akwai yiyuwan zuwan Bena dole Asibitin sbd
Umme.
Rasuwar hajiyan yasaka baa tsaya Wani kwaie kwaie ba da sauransu tana rasuwar aka lullubeta ana jiran lokacin daukan gawanta.
Cikin ganqanin lokaci Rasuwan hajiyan ta zaga dangi da abokan arziki.

Alh basheer bulama kuwa a ranar da yamma
•yayi Siya ticket shida sauran matansa na
tahowa.
Rashin nutsuwan da Safnah ke ciki na tsoron haduwa da Bena ya sakata somewan qarya momy ta kwasheta suka koma gida takaita ita Kuma ta dawo sbd kada a ga sun tafi du dukan.
Daga momy har Safnah Kuka suka ringa yi ba tsayawa har sai da idanuwansu sukai sintim,
Bena itama tini ta iso Asibitin Basu Wani jima ba aka sauyawa Umme Asibitin zuwa ta kaantes.
Cikin dare Alh basheer ya iso a cikin dare Akai komai aka Basu gawan hajiya da har lokacin kanta na Dan tsiyayan jini.

Duk girma da shekarunsa sai dayayi Kuka
sosai gaban gawar mahaifiyarsa
Umme ma dake asibiti kusan a cikin tsananin
hali kukan takeyi sosai na rashin uwa da ita
Daya ta rage musu.
Bena ce a tareda da ita asibiti Zeenah Kuma
tana gidansu Safnah din sbd zaman gaisuwa.
Anyi janaizarta da safe karfe Tara aka kaita
makwancinta aka dawo
Haka aka ringa karban gaisuwar daga manyan mutane da mokata da abokan Hulda.
Familyn kaantes kusan duka na kusa da nesa
sunzo sunyi gaisuwa dad kaante kuwa sai
dayayi kwana uku a Jere Yana zuwa kullum ya
sake musu gaisuwan tinda sirikarsa ce Shima
ya rasa.
Jinyan momy kwana biyu ya saka Bena Bata
taba leqa gidan gaisuwan ba har Saida Akai adduan uku aka watse zaman gaisuwar ranar
Kuma aka sallami Umme Dan haka Kai tsaye can gidan Zeenah ta wuce da ita
Bena Kuma Dayake ranar Zeenan ta rigata shiryawa sai ta wuce Asibitin tinda Angama zaman karban gaisuwa tanajin an sallami ummen gasunan dawowa saita Jira su dawo din Bata bisu ba bare tasan zasu biya can gidansu Alh basheer din.
Bayan sunyi gaisuwa da kukan rashin da sukai itada Alh basheer ta dawo gida Shima sauran matansa washe gari suka koma tinda Angama zaman shi zai sake kwana biyu a garin kafin ya koma can ma yayi karban gaisuwan wainda
Basu samu zuwa Nan din ba sbd Nisa.
Tinda Umme ta dawo suke kulawa da ita sosai kaman ‘varsu sbd tausayin damuwan data shiga na rasuwar sosai,
Taji radadin rashin hajiya fiyeda yanda tayi tinanin zasu iya jure rashinta.

DD ma kullum saiya kirata a waya ya ringa nuna mata kulawa sosai tareda Bata hakuri akan juriya.
Da haka ta Dan sake sbd ganin ta saka yaran cikin damuwa.
##MAMUH#
#DBENA
#DAWOOD
#BENAZIR
#ABABA
#SAFNAH
#BILAL
#SUMAYYAH
#MOMY
#ANNE

Back to top button