Hausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 68

Sponsored Links

68
Yau ciwon Mararta Bai barta ta samu iya zuwa office ba Dan haka ko fitowa bataiba a daki
Nafisat takai mata breakfast dinta Amnah
Kuma yanzu school yasa Bata zama gida sosai.
Zeenah kafin ta fita office sai data zo dubata cikin kulawa da kauna sosai kafin ta fice, Umme ma haka ta ringa yawon dubata a dakin tana mata sannu
Wanka tayi taci abinci kadan ta kwanta bayan
Tasha magani bacci ya Dan dauketa sama sama sbd ko ta fara idan ta Murda zai ta farka.
Ahaka tayi wunin wayarta ma kashewa tayi sbd Bata bugatan kira, Daqyar tai yinin duk bayan 2 hours saita tashi ta lallaba ta canja pad da pants harta samu da yamma ta iya sake wanka ta shirya sai alokacin ta Umme ta takurata dole taci Tuna macaroni salad tasha ginger mara sanyi ta
Dan fito Palo ta zauna ko zatafi Jin jikin ya sake.
Amnah ganin mummynta ba lafiya tinda ta dawo Nafisat nata dawainiyanta har Arabic teacher dinta yazo Nafisat ta kamata suka tafi
Daman baa barinta ita Daya da Nafisat ake karatun Dan haka suna can sai kusan magrib time na tafuyarsa yayi ya wuce suka dawo.
Ana gama sallan magrib jikinta Yakuma yin dumi sosai taji ta gaji da zaman ta miqe ahankali ta koma dakin tasake wanka da Shirin bacci ta Haye gado tana Dan rufe Ido sbd jikin lokacin har anyi sallan ishal.
Amnah da Nafisat ke Tayata karatun Arabic dinta dakin Zeenah suka koma sbd kada su dameta ganin tana Dan Jin jikin
acan bacci ya dauke Amnah sai kawai Zeenah tace Nafisat tabarta anan taje ta dauko mata kayan bacci ta shiryata ta fice musu daga dakin.
Daidai lokacin Shima ya samu wartsakewa daga ciwon kan Dayake fama dashi tin jiya
Dan haka Koda ya shigo palon babu kowa duk suna dakunansu kowa na Abinda yakeyi
Nafisat ce kawai ta gansa tana fitowa dakin
Zeenah tayi gasa da kanta tareda tausasa murya cikeda girmamawa ta gaidasa.
A taqaice ya amsa a gajarce
Zeenah data Jiyosa ta miqe daga alkin datakeyi a laptop tareda ajiyewa gefe ta zira slippers ta fito palon sanye cikin kayan bacci tana gaidasa da tambayan yaya kan nasa.
Amsawa yayi a hankali cikin sanyi kafin ya Kalli kofan dakin Bena da lazy eyes dinsa

Zeenah na ganin Hakan tayi saurin cewa
“Tin jiya itama batada Ify yau ko office Bata iya zuwaba.”
Kanta ya dawo da lazy eyes din yayi mata kallan tambayan meyake damunta.
Kallansa tasan me yake nufi sbd tasan Dan uwan nata dakyau Dan taka Kai tsaye tace
“Menstrual cramps”
Wani kallan Yakuma sakar mata cikin kasala da mamaki sbd baisan me take nufi ba sosai.
Murmushi ta sake sbd tasan Bai sani din ba tace

“Period, monthly bleeding na mata,haila in Arabic.”
Shiru yayi sbd sai alokacin ya fahimta ya Kuma
Gane.
Ahankali ya gyada mata Kai Yana cewa
“Tana Ina?”
Hannunta ta nuna masa bedroom din tace
“tana ciki, Amnah Kuma tana gurina zata kwana acan.”
Wucewa yayi dakin Kai tsaye ita Kuma ta koma nata dakin.

Yana shiga dakin nata babu haske sosai sanyin da qamshinta duk ya gauraya dakin tana kwance sanye cikin kayan bacci Riga da wando guntaye cinyoyinta masu lafiyan fata da kyan Kallo sai daukan idanuwa sukeyi.
A kasalance ya qarasa gadon Ya tsaya akanta kafin yakai hannu ahankali ya Dan qara hasken wutar dakin ya sake kallanta ganin yanda ta kwanta ta Dan dungule kaman baby Amnah.
Tausayinta ne ya sakasa lumshe idanuwansa tareda zaunawa bakin gadon a hankali ya Kai hannunsa kan hannunta dake kan Mararta ya janye ya Dora nasa a hankali.
Ajiyan zuciya suka sauke ahankali tare,
Shafa marar yayi ahankali Jin jikinta da dumi
Ita Kuma shafan da yakewa marar ya sakata farkawa ta Bude idanuwanta ahankali batareda da motsaba sbd qamshinsa Daya mamayeta yasata Gane shine a tareda ita.

Jin ta farka ya saka shi janyo bayanta ya hadata da kiriinsa suka lumshe idanuwansu a tareda tareda sake sauke ajiyan zuciya kowannensu a boye.
Babu Wanda yayi magana a cikinsu shiru sukai kowannensu na Jin dumin jikin Dan uwansa hannunsa na kan Mararta ya Dena shafawa
Amma dumin tafin hannuwansa Daya hadu da fatan marar nata ya sakata Jin tana samun relief da nutsuwa.
Ahakan shikuma yake shaqan qamshinta da dumin jikinta tareda taushin fatan Mararta ya sakasa lumshe idanuwansa yabarsu a rufe ita
Kuma ahankali bacci ya dauketa a Hakan.
Saida baccinta yayi Nisa sosai ya zameta jikinsa tareda gyara mata kwanciya ya rufeta da lallausan duvet cover ya fice daga dakin lokacin kusan karfe Daya na dare yayi.

Koda ya koma bangarensa Daman baiyi tinanin samun Safnah ba wadda kwana Biyun ta Dena zuwa dakinsa Sam ba kaman baya ba da kusan kullum saita Kai kanta.
Tin daga futarsa Safnah take zaune bakin window na dakinta tana Kallo ya shige bangaren su ummen Kuma Bata motsa a gurin ba duk tsawon awannin har lokacinda ya fito, ta Kalli agogo da idanuwanta dasukai
Wani irin ia na tafasar zuciya da baqin cikin datakeji kaman zai fasa zuciyarta ya kasheta take.
Barin ilkin window din tayi tana dafa bango sbd gafafunta dasukai mummunan rigewa sbd tsayuwa.
Wani masifaffen yaji da radadi idanuwanta ke mata tareda zuciyarta harma da qafafunta.

Tabbas bazata bari ta rayu acikin wannan mummunan halinba zuciyarta ko wata bazatayi a haka ba wIh bugawa zatayi ta mutu dole ta tsaya ta busar da zuciyarta a komai
Amma dai yau taba buqatan tabbatarda babu
Abinda ya shiga tsakaninsa da Bena sbd ma a yanzu kam ko wane abun ya shiga tsakaninsu to kenan ta tabbata sunan Bena din a gurguje zai fita cikin tsari su kawar da itan.
Washe gari ne zaiyi tafiya Dan haka Bena yafara kira a waya yace ta shirya likita zaizo ya dubata.
Cikin nutsuwa da yar basarwa tace masa taji sauki sosai ba laifi.
Shiru yayi sai Kuma yace ta shirya kawai dai likitan zatazo ta dubata.

Taji saukin da gaske ba laifi Dan hakama kusan ita ta taimaka Amnah tayi Shirin school
Abbakar ya tafi kaita.
Wanka tayi itama ta saka kaya marasa takura, pencil jean Daya lafe jikin siraran cinyoyinta sai black sweatshirt din blackpink.
Gashin kanta kaman baby haka ta dauresa tsakiyan Kai ta cusa cikin band ta fito Umme ta hada mata tea da kanta ta Bata ta karba tana Sha a hankalin sai ga Dr Ashley ta shigo
Nafisat datai mata iso tana bayanta
Dayake Umme sun Santa a asibitinsu take Aiki
Dan haka a sake suka gaisa aka zaunar da ita lokacin Zeenah na bedroom Bata fito ba ita
Kuma Umme tana gama gaisawa da ita tace
Nafisat ta kirawo Bena.

Qarasa Shan tea Bena tayi ta ajiye cup din ta taso daga dining ta nufo Palon daidai lokacin Dr Ashley ta dago ta zubawa Bena din idanuwanta sosai tana kallanta ta cikin farin cat eye glasses din dake fuskarta tana kokarin tantance kamanninta.
Bena ma Bata ankara da dr Ashley dinba Saida ta kawo tsakiyar palon sukai arba da juna.
Wani irin sarawa kanta yayi lokacinda taga Dr
Ashley likitar dake duba sumayyah yawanci idan Bilal yakaisu Asibitin kaantes, itace likitar data fara sanar dasu sakamakon cikin Amnah jikin sumayyah.
Neman dakatawa daga bugawa zuciyarta keyi Wani jiri ya debeta idanuwanta na duhu duhu tana Neman zubewa taji ya tarota da kirjinsa ta bayanta tareda rige zagayo cikinta da hannuwansa Yana kallanta cikin kulawa da mamakin Abinda ya sameta.

Tana gain Hakan sai kawai ta qarasa zubewa jikinsa zuciyarta na bugawa a mummunan yanayi.
Umme na gain Hakan hankalinta ya Dan tashi tana cewa
“Subhnallh,jikin ne Kuma? Yanzu fa take da sauki sauki sosai.”
Dr Ashley dataketa tinanin inda tasan Bena din ganin halinda ta shiga yasata dole watsar da tinaninta ta miqe tabi bayan D din dayayi gaba da Bena dauke ilkinsa kaman ya dauki Amnah.
Dubata Dr Ashley tayi babu Bata lokaci sbd ba Wani ciwon damuwa bane kawai dai
Dan su ummen da D din sun bawa ciwon mahimmanci sosai.

Fitowa sukai daga dakin sai alokacin Bena ta
Bude idanuwanta dasuke Neman cikowa da
hawaye zuciyarta na harbawa hannuwanta na
Dan daukan rawa sbd idan Dr Ashley ta tinata
to tabbas akwai yiyuwar mukullin Bude nasu
sirrin ya bayyana sbd itace tasan sumayyah ce
Bilal ke so Kuma itace ta dauki cikinsa ba ita
ba.
Zufa ne ya fara karyo mata sbd sai yanzu ta
Tina da bayyanar wannan gaskiyar zata saka
mutane da yawa tsanarta ciki harda yarta
Amnah da daddynta.
Bayan fitarsu dr Ashley D ta kalla tareda Umme
Kanta tsaye tace
“Ciwonta ba Wani serious abin daga hankali
sosai Akai bane,
Normally wasu matan haka suke fama every
month,wasu Kuma bako da yaushe suke
samun Hakan ba sai sun fara motsawan shaawansu ga wainda Basu taba motsata ba kenan so inaga daga ranar data fara harkan
Aure da mijinta zata Dena tinda Daman bawai ta saba ciwon maran bane.”
Shiru yayi har tayi sallama ta fice Bai furta komaiba
Ita Kuma Umme tausayin Bena din taji da wannan auren da dd babba yaqi cewa komai akansa ya zira musu Ido.
Juyawa yayi yakoma cikin dakin sai kusan bayan mintina arbain ya fito yayi sallama da
Umme ya fice sbd lokacin tafiyansa yayi kusa dole ya isa airport.
Rabi datazo bangaren a kunnenta taji Abinda
Dr Ashley ta fadawa su ummen Dan haka kaman yanda Safnah ta sakata kawo mata duk Wani zancen da zataji Daya shafi Bena haka ta tafi jiki na rawa da sakon munafurcin da Safnah tayi mata alqawarin kudade masu yawa ga kowane Sako me mahimmanci Saida D din yayi mata bankwana itama ya wuce airport kafin Rabi ta isar mata da sakon jikinta ya dauki barin farin ciki da murna Kai tsaye sai a ranar taji ta samu qarfinta ya dawo ta shirya tareda saka facemask da qaton sunglasses ta fito ko bangaren Umme Bata kalla ba sbd kada Wanda ya hangota ta sa motarta ta fada tareda Rabi suka bar gidan tareda kayanta a qaramar lv luggage bag sod bazata iya zama gidaba a tsorace take zata koma gurin mommynta kafin D ya dawo su samu tsayar da shirinsu yanda kota halin Yaya bazaa samu matsala ba.
##MAMUH#
#ABABA
#SAFNAH
#MOMMY BULAMA
#BENA
#DD KAANTE
#ROMANCE

*_Arewabooks@Mamuhgee_*

Back to top button