Hausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 36

Sponsored Links

img 169937935420936
Bilal Yana fitowa daga part din su Umme harabar gidan ya nufa Yana Ciro keys na motarsa duka hannuwansa na rawa,

Tashin hankalinsa da ficewa hayyacinsa akan Abinda yake tsoran Ababa zai iya Yi har sumayyah da Abinda yake cikinta su samu matsala duka Dan haka bazai taba tsayawaba anan tanacan tana fama tsakanin Rai da mutuwa.

Ummensa hankali tashe ta biyo bayansa tana son sanin meya faru sbd Bata taba ganin ‘danta me sanyi da nutsuwa ba acikin wannan mummunan yanayin Dan haka ta biyosa tana Kiran sunansa hankali tashe Wanda yayi daidai da fitowar su dd babba Suma Yana Kiran Bilal din cikin karaji da babban sautin daya tabbatarwa dasu dad kaante ba lafiya ba akwai babban lamarin Dayake faruwa.

Bilal a Karo na farko rayuwarsa Daya take umarni da Kiran dd babba ya fada motarsa tareda tayarwa da Wani mugun ribas ya nufi gate ko Gani bayayi sosai.

Dd babba cikin tsananin bacin Rai da fushi ya daga murya yace securities kada su budewa Bilal din gate

Sunajin haka take suka Maida gate din suka rife gashi yariga ya kawo Dan haka motarsa ta daki gate din Amma Bai tsaya ba kokarin sake yin gaba yayi ribas yakeyi ya sake dukan gate din Amma kafin yayi Wani yunquri DD ya iso gefen motar ya Bude ya zare key din Yana kallansa da idanuwansa dasuke masa kallan mamaki Mai tsanani Yana Jin da akwai babban lamarin dake faruwa da ‘dan uwan nasa.

Umme ta Riga dd babba isowa ga Bilal din hankalinta tashe hannuwanta na rawa ta fito dashi motar tana kallansa zatayi magana dd babba dashima ransa yagama mummunan Baci Yana zuwa ya dauke Bilal din da Wani lafiyayyan Marin Daya saka Bilal din dawowa hayyacinsa ya sauke Kansa hawaye masu dumi suna gangaro masa da tsananin damuwa da baqin cikin rashin darajarsa takai a saka masa hannu duk girman shekarunsa masu yawa.

Saukan Marin dd babba akan fuskar Bilal yasaka DD da Umme da dad kaante harma da securities shiga mummunan tashin hankali da tsoro.

Umme hannuwanta na rawa tana son kamo sa Amma bacin ran dd ya saka kowa kasa motsawa.

Kaman daga sama muryar DD Mai sanyi da nutsuwa a kame yace

“Me yake faruwa ne anan?”
Akwai Abinda ya kamata mu sani ne?

Bilal ya kalla Wanda hawaye yakeyi sosai kaman karamin yaro Amma yakasa dago Kansa,
Yau na Daya daga cikin ranakun da bazai taba mantawaba a matsayinsa na me amsa sunan kaantes.

DD Maida kallansa kan dd babba da ransa ya gama Baci yayi kafin suyi Wani yunquri
Umme ta riqo hannun ‘dan zasuyi ciki idanuwanta na cikowa da hawaye sosai itama.

A fusace dd ya Kalli Abbakar yace ya Bada umarni na doka Mai tsananin gaske kada a budewa Bilal gate ya fita gidan Bada izininsa ba

Da sauri Abbakar ya nufi gate Dan isar da sakon ga securities na gidan gabaki Daya.

Kiran Ababa ne ya sake shigowa wayar Bilal wannan Karan Umme ce ta karbe wayar tana kallan sunan me kira kafin tayi yunqurin dauka Bilal din ya amsa ya daga kafin ya iya Bude baki yayi magana Ababa Daya kusa haukacewa sbd tashin hankali kukan da benazir keyi cikin mafi girman tashin hankali kawai ya karawa Bilal din take ya tsaya cak tareda rintse idanuwansa dasukai jajir sbd masifaffen tashin hankali ya kashe wayar tareda juyowa kawai ya zube gaban dd babba Kansa a qasa cikin qunci da Wani irin ‘daci Mai tsanani na zuciya muryarsa na danne halinda zuciyarsa ke ciki yace

“Nayi alqawarin bazan taba barin kowa ya Ganni a gurinsu ba Amma Dan Allah ka bani izinin zuwa nakaisu asibiti.

Rintse idanuwa dd babba yayi sbd dai anzo gabar da dole dadynsa da mahaifiyarsa da DD su San Abinda yake faruwa tinda hakan ta faru gabansu.

Kallansa dd babba yayi Kai tsaye yace baka buqatan zuwa zaa aika driver yakaisu Asibiti idan ta haihu anfasa Kai auren Wani wata satin Nan zaa daura auren qasar zaka bari gabaki Daya ba yanzu zaku dawo ba sai ranar danace.

Kallan dad kaante yayi cikin bacin Rai Mai tsananin gaske da Bai samu ya fidda ba tin ranarda maganar cikin ta bayyana sai yau din yace

“Yarinyar da zaa daura masa aure da ita ciki ne da ita Kuma nasa haihuwa zatayi a yau din,
Ku sheda matiqar yabar cikin gidan Nan wlh karya dawo ya hada komai nasa daga can wata qasar zai tafi bazai taba dawowaba,
Wannan shine umarnina.

Yana gama fadar Hakan ya bar gurin ransa a bace yabar su dad da Umme da mutuwar tsaye zuciyoyinsu na sanqarewa.

Dad kaante mamakin kusan illata masa numfashi yaso Yi Saida Abbakar ya kamasa da sauri sukai ciki baya ganin gabansa sosai sbd jininsa ya hau Nan take Yana buqatan likita da gaggawa Shima.

Umme ma kusan Yanke jikin tayi zata Fadi DD da Bilal din sukai saurin tarota a tare sukayo ciki da ita zuwa lokacin itama tafara ganin dishi dishi take jininta itama yake Neman hayewa Dayake tanada asthma take taso mata sbd numfashinta Daya tsaya cak na wucin gadi.

Rikicewa jikin ummen yayi kaman kiftawar Ido Dan haka hankalinsu ya tashi musamman Bilal Dayake ganin shine sila.

Likitan gaggawa aka kira Wanda yasaka familyn kaantes din ankara da tashin hankalin da ake ciki Abinda dd babba ya gudara sai gashi ya bayyana Amma a iya familyn.

Ummensu a cikin Abinda Bai gasa awa uku ba ta koma kalan tausayi Amma a hakan ta riqe hannun Bilal tana son Kuka Amma ta kasa tace ya fada mata gskia.

Sunkuyar da Kai yayi cikeda kunyarta data DD dake rungume da ita dayan gefen saidai Kuma bazai iya mata karya ba kokuma gyaran zance Dan haka cikin sanyin jiki da damuwa ya sanar dasu irin tsananin son dayakewa Yarinyar,
Itace farin cikin Daya rasa tin tasowarsa,
Kuma Bai taba Jin sonta ya sauyaba a ransa duk da Abinda ya faru tsakaninsu,
Yana sonta tsakaninsa da Allah fiyeda yanda yake son komai nasa,
Idan zaa barsa ya tafi yayi rayuwarsa da ita ya yarda aturasa kowace qasar ce abarsa da ita.

Maganganunsa suka Sanya Umme da DD yin shiru suna sauraronsa,

Bilal bamai hayaniya da son maganganu bane,
Baka Gane Abinda yake ransa duk tsanani sbd ya iya binne komai cikin ransa
Amma ayau Bilal Yana bayyanarda soyayyarsa ga macenda Allah ya qaddaro masa haduwa da ita,
Wane irin so ne wannan Daya sanyashi yakejin zai iya zabarta yabar ahalinsa.

Umme kuwa Kuka ta fashe dashi a hankali tana girgiza tareda riqe hannunsa gam tace

“Karka tafi ka barni bazan iya rayuwa babu Kai ba,
Karka zabi barina ka tafi,
Kabi umarnin dd babba ka bari ta haihu a daura Muku auren zan karbeta hannu biyu nayi Maka alqawari Amma Dan Allah kada ka karya umarninsa a rabani dakai.

Shiru yayi batareda ya iya cewa komaiba sbd maganganun ummen kashe masa jiki suke Yi Dan ita da sumayyah sune mata biyu dayafi so fiyeda komai a rayuwarsa.

Yanda take rokonsa gata batada karfi ko kadan jikinta yasa DD janyota daga hannuwan Bilal data riqe Yana kokarin Kwantar mata da hankali sbd numfashinta ya far sake kokarin daukewa Yana fizgowa.

Juyawa Bilal yayi yabar dakin sbd baya iya kallan idanuwan ummen tasa Dan damuwa da rashin sanin mafita da zabi.

Kai tsaye Bai saduda ba sbd yanajin sumayyah na tsananin buqatansa ayanzu Dan haka ya sake komawa sashen dd babba Dan rokonsa.

jiki ba qwari yana hada hanya ya Isa kofar palon zai shiga ya tadda kofar Bude Bata qararasa rufewa ba kunnuwansa suka Jiyo masa Abinda ya sanyashi Jin Wani mummunan jiri daukansa.

“Aje da mota akaisu asibiti tana haihuwa da ita da babyn da iyayenta a kaisu inda bazasu sake waiwayo Nan din ba,
Abasu dukiyar da zata hanasu sake tinanin sunyi zama anan ma bare sanin sunan kaantes,
Duka wannan bayan Angama da matsalar Mahaifin nata ta yanda baisan meyake ba bare ya Hana barinsu garin.”

Abbakar ne yake wannan wayar a palon dd babba shikuma ddn bayama Palon.

Wannan umarni ne da dd babba Wanda yasaka ayi Bada sanin Bilal ba ta yanda zai nemeta ya rasa Kuma a satin yakeda niyar daura masa aure da ‘yar babban gidan da yayi Niya.

Jin wannan mummunan zancen yasa Bilal kusan somewa a gurin Saida ya share mintina Bai iya motsawa ba sbd tashin hankali da firgici.

Tsoro ne ya kamasa na Abinda zaa iya Yi din Dan haka qafafunsa na rawa baya Gani ya nufi motarsa wannan Karan cikin saarsa Yana ta-da motar ana Bude gate motar DD da Naseer ya tuqo zata shigo gidan
Bai tsaya jiran komai ba yayi gate Dina guje ya fice bayan motarsa data DD din sunyi kusan kaura har Saida goshinsa ya bugu ya Dan fashe Amma Bai tsayaba yahau titi a guje.

Daga securities har Abbakar da Naseer da sauran jamaan gidan dasuka fito a rikice Basu tadda ko kurar motarsa ba ya bace bat.

 

******
Bayan sallar magrib ne lokacin Kuma a daidai wannan lokacin sumayyah tayi haihuwar da baa so ta yagata.

Daga babyn har uwar babu me motsi a cikinsu sbd galabaituw mai tsanani da azaba.

A hannun benazir yar ta fado Dan haka jikinta na rawa ta rungume ‘yar maqoshinta na bushewa tareda idanuwanta dake qafewa ganin sumayyah Bata motsaba bare numfasawa.

Anne ma hannuwanta rawa sukeyi idanuwanta na Neman dauke Gani sbd ganin sumayyah kwance idanuwanta a rufe ba alaman Rai a tareda ita ta Yanke cibiyar mahaifar ta fado ko ta kan komai Basu bi ba itada benazir a tare hannuwansu suka Isa jikin sumayyahn suka kira sunanta a tare kowannensu muryarsa na yankewa.

Ababa dayaji shiru sake fadowa dakin yayi Yana Jin tsoro da tashin hankali Shima ya Kalli sumayyahn yaganta kwance babu alamar Rai a tareda ita take yaji jiri ya debesa ya dafa bango
Daidai Nan babyn ta saki Wani irin kukan jarirai Mai karfin gaske tana motsawa da karfi cikin jikin benazir Datake a dunkule.

Kukan babyn yasaka Ababa kallan benazir da sauri muryarsa na yankewa da tsinkewa yace

“Ta haihu kafin ta rasu ne?”

Wannan Kalmar tasa ta saka Benazir da Anne tsayar da hannuwansu daga kokarin sake taba sumayyahn dasuke hannuwan Anne suka fara Wani irin rawa suna jijjigawa numfashinta na Neman tsayawa.

Benazir kuwa ganinta da jinta ne ya dauke take saidai taji Ababa Yana cire ‘yar daga jikinta Amma Bata ganinsa Bata jinsa hakama Bata iya motsa ko Dan yatsanta.

Hande dake dakinta tana sallar ishai ya Kaiwa ‘yar harya tuntube Dan tayi mata wanka.

Yana fitowa dakin hande dawowa yayi gurinsu benazir din zaiyi magana yaga gabaki dayansu Suma kaman sun mutu daga inda kowannensu yake zaune
Gabansa yayi mummunan faduwa Dan haka ya fito dakin da sauri Dan dauko fitilarsa ta Mai tsananin haske sbd duhun dakin yayi yawa.

Yana fitowa Anne ta miqe tsaye ta fito dakin batasan Ina take jefa qafa ba ta nufi waje.
#MAMUH#
#ZAFIN KAI
#BENAZIR ABABA
#KAANTES
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
37

Back to top button