Hausa NovelsNi da Patient Dina Book 2

Ni da Patient Dina Book 2 Page 52

Sponsored Links

Be sauketa ako ina ba se a motar yaja suka hau kan titi , cikin nutsuwa yake driving zubawa kyawawan fuskanshi ido tayi tana kallonshi cike da so da kauna, batare da ya kalleta ba yace ” baby wannan kallo haka ?” tace ” to ai bana gajiya da kallon kane ” cize libs dinshi nakasa yayi jiyayi magana ma kadai idan tayi kara ingizashi take bece mata komai ba ya nufi migration office barinta yayi a motar yashiga ciki after some few minutes yafito hannunshi dauke da envelope daura mata yayi akan cinya ya tada motar suka dau hanya bata ko dauki envelope din ba saboda bece mata komai ba yanda yadaurashi hakan tabarshi kallonta yayi yace ” open it” sa zara_zara chocolate color yatsunta tayi ta bude passport da visa ta gani nata daduk wani abu da mutum yake bukata inzashi abroad duk akwai jujjuyasu tayi a hannunta kafin ta kalleshi tace ” habiby to sukuma wannan fah tafiya zamuyi ?” driving dinshi kawai yakeyi be kalli direction dinta ba ya gyada mata kai, bata sake cewa komai ba ta maidasu ta rufe , cikin makay shawarma suka shiga yayi packing motar fita yazoyi tarike hannunshi tace ” habiby nide bazaka barni nidaya anan ba ” matso da kanshi yayi ya manna mata kiss a libs dinta yace ” bazaki iya tafiya ba kibari inje in fito” kwabe fuska tayi tana kokarin yi mishi kuka bayanson ta tayar mishi da rigima yasa yafito yazo yabude mata itama tafito duk idon jamaa yadawo kansu se kallon akeyi saboda sun burge jamaa sosai musamman ma wayanda suka ganesu , rikota sosai yayi ajikinshi yanda bazataji zafi sosai ba intana tafiya dukda tanajin zafin ba sosai ba haka ta sake daurewa tana hada tafiyanta. makay shawarma babban joint ne a gombe yana da girma dakuma kyau sosai babu abinda babu a ciki , rike hannunta yayi suka fara tafiya har ciki wajan shopping tsayawa yayi yace ta dauki abubuwan da take bukata side din su perfumes taje ta diba masu kamshi da dadi hade da lotion’s se shower gel, body spray, mouthwash, sannan takoma kan kayan kwalama ta dibe chocolate sosai da ice cream security wajan ne yariko keken kayan yatura har wajan yin bills ATM ya bada suka cire kudinsu suka hada musu komai a leda karba security yayi akasa a bayan motar suka shiga suka tafi duk tunaninta daga nan gida zasuyi setaga ya sakeyin packing a yahuza suya yafita ya karbo nama da yogurt dinsu masu matukar dadi .

Agajiye de suka dawo gida fanan duk ta gaji jira kawai takeyi taganta akan gado , bude motar yayi yadauketa cakk yama daya daga cikin securities dinsu alama da ido ya kwaso kayan cikin motar yabisu dashi har part din su direta yayi akan bed dinshi ya koma falo ya karbi ledojin ya ajiye akan kujera, cire rigar jikinshi yayi wannan hadaddiyar surar nashi ya bayyana especially his 6packs and muscles amurde suke bathroom yashiga ya sakarwa kanshi shower yafito daure da karamin towel a kugunshi se dingan ruwa yakeyi tana zaune akan gadon yanda yafita yabarta haka yasameta sede ta cire hijab din jikinta ta ajiye a gefe jin yanda ya dameta wajanta yanufa yahau kan gadon ya kwantar da kanshi akan cinyarta ya lumshe ido kamar mejin bacci sa hannunta tayi ta cusa cikin gashinshi tana yamutsawa hade da shafawa burgeta gashin yayi musamman da ruwa yajika shi se yayi wara_wara gwanin burgewa, duk abinda takeyi yana jinta beyi yunkurin mikewa ba ahankali hankali reaction dinshi yafara canzawa , rike hannunta dake kanshi yayi yadawo da hannun kan faffadar kirjinshi dake dauke da kwantaccen suma baki me laushi yakwanta luf , batayi tunanin wani abu ba tafara shafa kirjin nashi musamman inda gashin yafi yawa kasa hakuri yayi yadaura hannunshi akan dukiyar fulaninta yafara yawo dasu da sauri ta cire hannunta akirjinshi tana kokarin mikewa dan bata shiryawa hakan ba a irin wannan halin da take ciki bata manta da bakar azaban datasha jiya ba qin dagata yayi yasa hannu yamaida ita ta kwanta ya mata rumfa dede kunnenta yakawo face dinshi yace ” wifey where are you going to? karki tafi ina bukatarki akusa dani” sake tsorata fanan tayi jin yanda muryanshi one time ya canza ga idonshi dasuka rine suka canza kala mutsu _ mutsu tafara mishi hade da kuka runtse ido yayi dan bayason jin kukanta har cikin ranshi yakejin hakan dagata yayi yace ” am sorry wifey bawai wani abu zan miki kawai bacci zamuyi ” ba ta yarda da maganarshi ba ,gani takeyi kamar ze sake mata abinda yamata jiya , yasa ta maqe kafada, dafe goshi yayi ahankali yafurta ” oh my goodness” tashi tayi tafara tafiya tana bin bango taje wajan kujeran tadubo ledar naman daya siya hade da yogurt dan yunwa_yunwa tafaraji dawuwa tayi inda yake tabude ledar kamshin gashashiyar naman kaza dayasha kayan hadi ne yadaki hancinta ,cike da nutsuwa tafaraci tana hadawa da yogurt din harta koshi zuba mata ruwa yayi a glass cup yayi yabata tasha tayi hamdala ta koshi qat.
Mikewa tayi dan tanason tayi wanka , dakyar takai kanta bathroom dinshi tashiga tayi wanka tafito sanye da rigar towel fari kal samunshi tayi ya kishingida da pillow kanshi na kallon sama damuwa karara ya bayyana akan kyakyawan fuskanshi ganin yana kokarin sauke kanshi ne yasa ta dauke kanta daga gareshi tazauna a gaban mirror tashafa lotion dinshi da perfume ta shiga dressing room dinshi , dubawa takeyi ko zataga wani kana nan kayanshi dazata samu su mata dede dan qiwiyan komawa nata dakin takeji, idonta ne yasauka akan wata trolley me kyau sosai pink color burgeta yayi taji tanason ganin meye aciki durkusawa tayi tasa hannu ta bude akwatin kayan bacci ne kala kala aciki sunfi set 30 masu kyau da daukan hankalin duk wani da na miji daukan na farkon tayi ta bareshi a ledarshi , wata yalolon rigace me tsantsi da kuma raga_raga rigar transparent ne onion color tsayinshi iya guiwanta yatsaya hade yake da pant dinshi aciki shima onion color sunyi kyau sosai dauka tayi tasaka ajikinta babu abinda baa gani komai yana waje muraran harta pant din datasaka , rufe akwatin tayi tamaidashi inda yake tasa slippers tafito gaban mirror taje tasake feshe jikinta da different perfumes masu dadi dakuma sanyayyar kamshi ta gyara gashinta.
Karfin hali tayi tasamu tahau kan gadon tana ciccije libs dinta yana nan a kishingiden taje ta kwanta akan kirjinshi da har lokacin besa kayaba dagashi se towel , tun kafin ta iso inda yake kamshin turarenshi sun sanar dashi zuwanta bude sexy eyes dinshi dasuka canza kala su da kansu suke lumshewa tsabar wutar shaawar dake damunshi yazuba mata na mujiya dagowa yayi yazauna yana bin jikinta da kallo daukewa numfashinsa yayi na wasu yan dakiku ganin dressing din datayi ta matukar tafiya da duk imaninshi kallon hips dinta dake da fadi da tudu yayi yana kallonsu duka awaje gana shanunta dasuke gaisheshi , hannu yasa yazagayo dashi a kugunta yakai kanshi kan wuyanta yana shakar kamshin jikinta dake sake birkitashi , fanan duk a tsorace take . kamar zeyi kuka yace ” baby please I need you karki cemin ah ah” dukda yabata tausayi amma bazatayi gangancin barinshi ba muryanta na rawa tace ” Mr azaad akwai stitches ajikina fah ” tunawa yayi da anmata dinki yasa jikinshi mutuwa janta yayi ajikinshi suka kwanta yaja musu blanket yana manne da ita yanata tabe_tabe bata hanashi ba.

Su ummi basu tashi ankara da fanan bata gidan ba se bayan isha tukun nan ,anzo zasuci abinci suka ga duk sunfito mama ce ta tambayi hairah ” Ina antynki ” amsa mata hairah tayi da ” bata nan dazun yaya yazo yadauketa ” dake bayan fitar Mr azaad da fanan seta tambayesu waye shi sukace mata ai mijinta ne, jinjina rashin kunya irin na Mr azaad ummi da anty amina sukayi itakam ma anty amina duk tsoronta daya kar Mr azaad yace ze kusanci fanan da dinki ajikinta Allah_Allah takeyi sugama cin abinci su koma gida kafin me afkuwa ta afku. se wajajen 9:00 su ya Usman,ya al ameen, fawwaz, areef suka dawo gida tare da hafiz da yaji sauki sosai suna sallama hairah ta mike da gudu taje ta rungumeshi tana tsallen murna ganin yayanta jikinshi yayi sauki zama sukayi shida ita a kujera daya baba ma yana falon , kasa hafiz ya durkusa yana musu godiya sosai na taimakonshi da kanwarshi da sukayi murmushi kawai sukayi suna yabawa da hankalin yaran baba ne yace ” hafiz tunda baku da kowa zaku zauna atare damu kunzama yayanmu da yardan Allah! kanwarka zata zauna a gidan nan zan maida ita makaranta! Kai kuma dazun kafin azaad yabar asibitin yamin magana kancewa tunda ni nadauki hairah shikuma yadaukeka zaka koma gidansu da zama ze mayar dakai makaranta duk sanda kakeso zakazo kaga kanwarka haka itama sanda ba makaranta zatazo ta ganka, kun zama jininmu yanzu in sha Allah bazaku sake kukan maraici ba kusaki jikinku munzama daya” tsabar farin ciki hafiz da hairah har hawaye sukeyi basuyi tunanin akwai irin wayan nan mutanen a doron duniya ba dan duk inda sukaje neman taimako sede abisu da kyara da tsangwama.

Ummi tace ” bari mu gudu dare na yi hafiz mutafi ko ?” Gyada mata kai yayi ya mike shida su fawwaz rike hannun hairah yayi har waje yana ce mata ” hairah kinga yanzu munsamu wayanda zasu taimakemu tsakani da Allah dukda nasan halinki bakida kiriniya da neman fada duk da haka dole insake fada miki kinji banda rashin kunya dukda shima ba halinki bane kimusu biyayya kamar appu da amma Allah yajikansu karki zama me manta halacci ” ya karisa magana yana shafa kanta gyada mishi kai tayi tace ” in sha Allah yaya zanyi yanda kace ” ummi dake bayansu basu sani ba tajiyo duk abinda suke fada tayi murmushi tasakejin yaran sun kwanta mata arai.

Sallama suka musu suka tafi hairah se bye-bye takeyiwa yayanta hafiz , rike hannunta suhaima tayi zasu koma ciki yar gyaran murya ya usman yayi yama suhaima alama da ido tashiga ciki tagane abinda yake nufi , yasa tasaki hannun hairah tashiga ciki tabarsu a compound din gidan su biyu , kallonshi tayi da manyan idanunta tace ” laaah ya usman kaine ?” Yace ” eh khai…. “Sekuma yacanza tunawa da yayi ba khairaty bace yace ” hairah yayanta nine zo kitayani hira ” zama sukayi akan plastic chairs dasuke cikin compound din, haka yadinga janta da labari harta sake itama tadinga zuba mishi hira nan yagane itama gwanar surutuce gashi ko magana tayi se angane akwai tsantsan yarinta a tattare da ita haka yabiye mata suka dinga hira har karfe goma yace mata taje ta kwanta dare yayi gobe zasu karasa tashi tayi tashige dakinsu shima yashiga daki ranshi fess komai normal yakeji yana tafiya mishi yasan yau zeyi bacci me dadi.

Karfe 2:30 nadare fanan tafarka sakamakon Kiran sunanta da taji akeyi cikin sigan bada umarni dakuma girmamawa tashi tayi taga Mr azaad na baccinshi hankali kwance sauka tayi akan gadon tabude kofar ahankali yanda bazeji karan ba fitowa falo tayi tana sanye da kayan baccin jikinta falon ne yasauya daga falo zuwa wani irin hadaddiyar daji me dauke da shuke_shuke gwanin ban shaawa ga kamshi hade da dusan kankara sama kuma sararin samaniya ne , batayi mamakin hakan ba ji tayi an kara kiran sunan nata acan saman sararin samaniya yasa tabude hannayenta duka biyu tafiya tafarayi akan iska tana firewa sama inda sautin muryan ke fitowa seda ta kusa isowa wajan tukun kayan jikin yacanza zuwa doguwar riga fara sol komai din jikinta seda yacanza yazama hadadde hatta gashin kanta style dinshi canzawa yayi takoma sarauniya sak, isa wajan tayi taga bakowa babu alamar mutum ko tsuntsu kallon kudu da yamma tayi can ta hango jaaazana shi kadanshi akan iska yana daukar ido hular mulkin da yake ran kowa daga mutane har aljanu kowa burinshi ya mallakeshi , shine yayi wannan kira ga fanan wajanshi taje ta tsaya tanajin sanyi na ratsata , jitayi magana na fitowa daga jikin jaaazana ” sarauniya fadima shin kinsan da lokacin ki yakusa karewa a duniyar bil adama? lokaci kalilan ne yarage miki da ki fara gabatar da abinda yakamata”

 

To semun hadu gobe inme duka yakaimu da Rai da lfy .

 

Masu comment Allah yasaka muku da aljanna ina godiya sosai matuka.

via- https://play.google.com/store/apps/details?id=com.happyverse.diarywithlock&referrer=utm_source%3DD
https://chat.whatsapp.com/Jo87gS6QxQF58XSV10dYL8

‍⚕️‍⚕️ NIDA PATIENT DINA

 

Story & written by ✍️
MRS ISHAM

JARUMAI WRITERS ASSOCIATION

( J. W. A )

 

Back to top button