Hausa NovelsMiskili Ne Hausa Novel

Miskili Ne 11-12

Sponsored Links

❤‍ *MISKILI NE*❤‍

*11&12*

 

https://chat.whatsapp.com/JHvLho4664m0KcDHi1EDmF

1) *Invitation card, video invitation card*
2) *Book cover 3d mackup, normal book cover 3 colors*
3) *Data flyer, Account number sticker*
4) *3d mackup logo, normal logo*
5) *Ideogram ai logo*
6) *How to remove background*
7) *How to download icons*
8) *Yanda zaki haɗa document na littafi,da kuma yanda zaki cire password idan aƙwai a jikin littafi*

9) *Zan bada application guda 3 waɗanda ba’a samun su a play store*

*Kuɗin da zaki shiga Class ɗin da zaki samu wannan garaɓasa ₦300 idan kin shirya ki turo kuɗin ki ta 1632036584 Saadatu Balarabe Access Bank ki turo shaida ta wannan number 07032895551 ko katin MTN*

 

……..tsaye turus Abdallah yayi batare daya rufe k’ofar ba suna kallon kallo shida Amaan “wanda ya tsorata matuk’a da kyawun yarinyar”kasa furta mata komai yayi yana dai kallonta da kallon kayan datake cillawa”wanda saida gabansa yafad’i dayaga Abinda ke hannunta”yasan halin yayansa in and out,baya fatan yaya shariff zaiso b’ata rayuwar wata….wanene kai wai? siririyar muryarta ta katse masa tunani”saidai kafin ya furta wani abu baba ladi ta fito daga cikin kitchen tana fad’in Amaan halan kallon kikeyi ne?”shiru tayi sbd ganin Abdallah tsaye daya maida kallonsa gareta”kamar zatayi mgn sai kuma ta fasa”saidai ranta yabata yaron jinin shariff ne sbd kamannin data gani sunayi”ta zauna gefen Amaan tana kallon kayan hannunta”waye yabaki wa’annan kayan ne? hamma ne! Amm Ina wuni?”baba ladi ta Amsa da lafiya qlau “yaya shariff na nan pls?”kafin baba ladi ta bashi Amsa yaji motsin takun shariff yana sakkowa down stairs d’in “ya canza kaya zuwa jallabiya da Alama masjeed zaije yajira Akira sallar magrib”ganinsa yasa bbu wanda yayi mgn Acikinsu”tunda yafara doso parlourn yalura da Abdallah”saida yaji k’irjinsa yabuga”Amma ko a fuska be nuna komai ba”ta wutsiyar Ido ya lura da yadda Amaan ke wasa da kayan ta fiddosu daga cikin ledar”Aransa yace”idan tanada cikakken hankali bazatayi hakan ba…Amaan na ganinsa da sauri tace”hamma kagansa ya shigo beyi sallama ba ko?”ta fad’a tana nuna Abdallah “shariff kuwa had’e rai yayi kamarma badashi take ba”Abdallah yayi saurin cewa” yaya barka da fitowa”hannunsa ya d’aga masa yanufi k’ofa shi kuma ya kalli Amaan yamata gwalo yana murmushi yabi bayan shariff “suna fitowa shariff yace”lafiya zaka biyoni Anan?”nifa wlh yaya bansan meyasa kake hakan ba?”tab’e baki shariff yayi murya bbu Alamar wasa yace”kasan Allah kasake kasanarwa Ammi kasamu matarcan da y’arta gidan nan ranka zai b’aci”nifa bazan sanar mata ba”Amma yaya miye Alak’ar ka dasu ne?ban sani ba”kaji dai mena fad’a maka ko?”naji Ai”Amma pls yaya ka bani sakon saina wuce nayi sallah”sharesa yayi be koma mgn ba yayi gaba”Abdallah ya turo baki yana mgn k’asa k’asa”yayinda shariff besan yana yiba”yama manta dasu mus’ab saida zai wuce ya lura dasu”d’an tab’e baki yayi yanufi wajen su”tun kafin ya zauna mus’ab yace”Abokinah hardamu Acikin wad’anda ake jama Ajin?”pls ina jinka mansoor kasan befi 7minit ba Akira salla”ya fad’a yana kallon Abdallah daya iso yana gaishe dasu mus’ab”dan d’azun be lura dasu ba”kai ! ban hanaka irin wannan Askin ba?”yafad’a fuska ahad’e yana maka masa harara”dan Allah kabarsa ya wuce ai shine manyan yara ke yayi ko?”cewar mus’ab “Abdallah yayi dariya ya wuce Abinsa”Dr Mansoor kuwa yama rasa ta Ina zai fara?cikin k’arfin hali yace”Abokinah nazo da k’ok’on barata a wajenka game da yarinyar nan Amaan k’anwarka”wlh tun ranar danayi tozali da ita naji soyayyarta Ara…. look mansoor! idan mafarki kakeyi yaka mata ka farka mu Ajiye wannan maganar”mus’ab meka sanar masa game da itane??”yafad’a fuska bbu walwala yana jifar mus’ab da wani irin shegen kallo irin na tuhuma”ni kuwa miye zan sanar masa?”yamun zancen yana sonta nace bbu ruwana yamaka mgn da kansa tunda k’anwarka ce”tsaki shariff yaja yana mamakin wace irin jarabace ke damun Dr Mansoor?”yanada mata da yaransa biyu Amma yake kok’arin hararo wata…..pls Abokinah wlh bada wasa nakeyi ba da gaske Ina sonta zan kuma Aureta”idan zaka bani dama na fara mgn da ita har zuwa ta Amince da soyayya ta……tsabar takaici kasa mgn shariff yayi saidai yafi Azawa mus’ab laifin komai”har zai juya yabar musu wajen sai kuma ya kalli Dr Mansoor cikin izzah yana cije baki yace”inaso kasani ba kowace mace Ake gani ba Ace Ana sonta kai tsaye ba”sannan kasan bbu Abinda na tsana sama da irin wannan shirmen”so pls mu Ajiye wannan maganar”Amaan ban bata damar kula wani ba”duka shekarunta nawa suke?”kai yanzun da matarka da komai Amma kake hangen wata?”yak’are maganar agundure yana tab’e baki….look shariff! karkaga nazo kamun k’afa ta wajenka ka raina mun hankali, ko kacimun mutunci”idan sonta kakeyi sai ka fito kasanar mun tunda dai nasan ba iyeyenku guda da ita ba ,bakada k’anwa mace ko?”cewar Dr mansoor cikin zafin rai….cikin gadara shariff ya girgiza kansa Ido iso cikin Ido yace”idan har hakane araina kai baka Isa na maka k’arya ba”kuma baka Isa ka kalleta kace kana soba”ka rubuta ka Ajiye indai Ina numfashi babu kai bbu Amaan”yak’are maganar yana huci”subahanallahi!! saida na gaya maka mansoor daka dena zancen nan sbd gudun matsalar dazata biyo baya Amma kak’i ji”pls kuyi hakuri sbd k’aramin abu be kamata kuyi ha….kabarsa mus’ab”sbd yaga gidansa nazo na nuna ison k’anwarsa gara yacimun mutunci yadda yaga dama”doguwar tsuka shariff yaja yajuya kamar zai tashi sama yabar musu wajen”gaba d’aya zuciyarsa Acunkushe take”haushin mus’ab da Dr Mansoor sun masa yawa”ga damuwar Abdallah yaga Amaan “fatansa Allah yasa karya sanarwa Ammi”da wannan yanayin yayi sallar magrib”be baro masallacin ba saida Akayi sallar isha’i “yana ganin kiran mus’ab yamasa banza”cikin zafin zuciya ya shigo gidan”Amaan da baba ladi na cikin parlourn”zama kan kujera yayi ya gaisheta ta Amsa masa”hamma Ina wuni?”cewar Amaan cikin yarinya”lafiya qlau”naga kayan nagode”da mamaki ya kalleta”saita masa murmushi”ya kawar da kansa”yana zaton baba ladi zata ce mata tamasa godiya….be gama wannan tunanin ba yaji motsinta kusa dashi”d’aure fuska yayi saima sannan ya lura da baba ladi tabar parlourn”hamma! menene?”tsuke baki tayi tana kallon yatsun hannunta tace”dama banida turare….saida ya d’auki kusan second 10 kafin yace”bayansa sai me kike buk’ata?”inaso kasiyamun wannan madaran me sanyi danaga suna sha cikin TV “murmushi yaso yasub’uce masa sai yak’iyi”sarai yagane ice cream take nufi Amma miskilin sai yashareta yana kallon k’aramar wayarsa da fareeda keta faman kira….hamma! d’ago kansa yayi ya zuba mata firgitattun golden eyes nashi”da sauri tayi k’asa da kanta “ki tashi kije ki kwanta bacci kiyi addua”to yaushe zaka….kinsan Allah zan b’ata miki rai”bazaki kyaleni na huta bane?”yakatseta cikin deep husky voice d’insa “oya tashi ki bani waje”kuka ta fashe dashi tabar parlourn “yaja tsaki shima yatashi ya haura samansa”kan royel bed nasa ya kwanta yayi matashin kai da hannayensa ya lumshe Ido yana tunani”ak’agare yake Amaan tasamu lafiya koya samu yasadata da iyayenta”beso yana yawan jin dama be taimaka mata ba”sbd karya zobe ladansa”daya tuna time d’in data kama kuka sai yaga kamar be kyauta mata ba”musammun daya fahimci dagashi sai baba ladi tafi yadda tayiwa mgn”tashi zaune yayi ya d’auki Abinda zai d’auka a d’akin ya fito ya rufe da key”har zai fita sai kuma kawai ya tsintsi kansa da shiga d’akin su”baba ladi na bayi”Amaan na kwance saman bed “da kayan bacci Ajikinta kanta bbu d’an kwali “ta rufe jikinta da lallausan bargo”tana ganinsa ta d’aure fuska ta juya masa baya”batare data Amsa sallamarsa ba”shiru yayi yana k’arema d’akin kallo”can yace”kinyi addua ne?”yafad’a kamar Ammasa tilas”kukan shagwab’a tasaka tana fad’in hamma ni bbu ruwana dakai ba korata kayi ba?”tab’e baki yayi yak’iyin mgn”tama d’auka yafita dayaji shiru saita juyo”ta gansa tsaye yana danna waya”toni kaje kabani waje mana”d’ago kansa yayi yana fad’in what?? da sauri ta d’auke kanta”Amaan rashin kunya zakimun?”nidai ah ah kayi hak’uri”kuma nayi adduar dakace”fad’amun yadda kikayi adduar”k’ulhuwallahu ta karanto da falak’i da nasi”waye ya koya miki?”baba ladi ce”be koma mgn ba”saidai yafad’a kogin tunanin halin da iyayenta zasu tsintsi kansu na rashinta”hamma! Ina jinki”kaje ka kwanta kayi addua sai kayi bacci ko?”girgiza kansa kawai yayi yana jin tausayinta”ya lura tanada kunya dak’in son mgn lokacin datake hayyacinta “dan ko yanzun ya fahimci bata son yawan had’a Ido dashi”hamma! be Amsaba yafita daga cikin d’akin sbd surutunta ya ishesa”bayan ya rufesu da key ya wuce mota”sai wajen k’arfe 9 saura yashigo gidan”Ammi da mijinta Alh yahaya suna zaune a parlourn “da Alama Abinci yagama ci”Ammi sannunku da hutawa”yauwa shariff dama kai nake jira zan baka acc n kasanya million 5″tamkar bazaiyi mgn ba sai kuma yaduk’a gefenta yace”na meye za’a saka?kuma Acikin Account d’in wa za’a saka? Acikin account d’in Abban kune”Atake shariff ya had’e rai dama ransa yabashi shine za’a bama kud’in “zarginsa dai ya tabbata kan Alh yahaya yana so ya yagi rabonsa Acikin dukiyar mahaifinsu”sai yanzun yatuna da CTV camera d’in daya Ajiye gidan bisaga shawaran mus’ab”sbd shima sadda Ammi zata Auri Alh yahaya yabama shariff shawaran karya Amince”da Ammi ta kafe saida ta Auresa shine saiya bashi shawaran ya Ajiye CTV camera Agidan…tabbas yanzun yaka mata yafara duba Abinda duk ya wuce da CTV camera d’in ta d’auka…..kayi shiru ?”mik’ewa tsaye yayi yace”gaskiya Ammi baza’a turaba saida yaddar sadeeq da Abdallah “sannan kuma sai naji meye za’a yi da kud’in??…wato niban isaba nace kuyi abu kuyi ba shariff??”ah ah ki barsa bbu damuwa basai Anturaba”cewar Alh yahaya yana jin kamar ya shak’e shariff”Ammi bata koma mgn ba saidai ranta yab’aci”tasan kuma sadeeq dukda baya k’asar ko An kirashi bazai Amince ba sbd yafi kowa tsanar Auren datayi”tasan Abdallah ne kawai zai iya Amincewa idan shariff shima be zugeshi ba”kamarta Ace million 5 ta gagara tasaka su tura duk tarin dukiyar yaran nata na gado”da kuma dukiyar shariff”dukda tasan yana kashe mata kud’i kamar besan zafin nema ba” itada danginta da duk wanda zata kawo tace Ataimaka masa….haba karki damu babu komai zan samu rance kawai wajen abokaina”dama kayanne da aka rik’e yasaka nace ki bani kud’in”yafad’a kamar gaske”Ammi ta sauke Ajiyar zuciya tana fad’in wlh saiya bayar dasu Alh kama dena zancen abarsu”ta k’are maganar fuskarta babu walwala ta tashi tsaye tabi bayan shariff “yana zaune a parlourn sa yana danna laptop ta shigo bbu ko sallama”yama zata ko Abdallah ne sai yaji tana fad’in wlh wlh!! muddin baka tura kud’in nan ba shariff sai ranka yab’aci Agidan nan…. “yabita da kallo cikin taushin muryansa yace”Ammi ki dena rantsuwa zan tura da kud’ina bama cikin kud’in muba”zan tura ne sbd bazan iya tsallake umarninkiba”saidai lokaci kad’an yarage kisan waye kika Aura”daga haka yayi shiru “ita kuma tana tsaye tana nazarin kalamansa”can kuma tafara karanto masa acc n d’in”tana tsaye yatura kud’in zuciyarsa na zafi”sbd yasan ba hanyar Allah da Annabi za’a biba wajen Amfani da kud’in”murya a sark’e yace”kiyi hak’uri Ammi idan harna b’ata miki”bakida shamaki da duk Abinda na mallaka Aduniya”zaki iya komai kikeso kiyi dashi”dan Allah ki zauna kiyi nazarin mijinki”daga haka yayi shiru”ita kanta Ammin jikinta yayi sanyi”tana kuma auna maganganunsa”batace komai ba ta fita”shariff yacigaba da saita komai saiga abubuwa da yawa yana gani”Aciki harda bayan tashin Ammi yanzun daga cikin parlourn, Alh yahaya ya harari bayanta yana fad’in kud’in safaran kokin ne da kud’in dazan miki Asirin sakashi ya Auri y’ata zaki saka yaturo mun”murmushin gefen baki shariff yasaki yana rufe laptop d’in”yanzun burunsa kawai fareedah ta kamasa zobban nan”yaga Abinda yakeso yagani sannan zai dawo kan Alh yahaya yarabashi da mahaifiyarsa”ada haushin mus’ab yakeji Amma yanzun sai yaji bbu jin haushin sai jin k’aunarsa”dan yasan mus’ab Abokine nagari”gashi yabi shawaransa yaga Amfani Acikin ta”inda be Ajiye CTV camera d’in ba taya zai san me Alh yahaya ke k’ullah akansu??da wannan tunanin ya wuce katafaren bed room d’in sa Aljannar duniya”time yaduba har 10 pm ta wuce”wanda tsarin lokacinsa 9:30 pm yake shiga bath room yayi wanka”zuwa 10 pm yake kwanciya bacci “kasancewar sa kamar bature yake”be kwanta d’in ba saida yayi wankan”Abin mamaki yayi mafarkin gashi nan shida wata yarinya suna sanye da fararen kaya cikin wani lambu”suna zaune kan grass carpet,kansa saman cinyar ta”ba’a ganin fuskarta sosai ta kama hannunsa tasaka masa wata red d’in flower tana fad’in tukwicine gareka my *salfad* yanadai kallonta beyi mgn ba sai kok’arin kissing d’inta yakeyi ita kuma tak’i yarda”ya riketa sunata dariya…..adaidai nan ya farka”wanda shariff yayi mamakin mafarkin”sunan *salfad* kuma yak’i barin zuciyarsa”da hanzari ya sauka daga saman bed d’in yanufi bath room….
misalin k’arfe 7:43 am Amaan ce zaune a parlourn taci gayunta cikin sabuwar doguwar riga gownt dark blue me zanan white”dukda bata shafa koda hodaba Amma tayi kyau na musammun”tayi tagumi da alama tunani takeyi”veil d’in kayan na hannunta”yayinda baba ladi na kitchen tana had’a musu Abin kari”wanda Amaan taso tayata Aikin itace tace tabarshi sbd gudun kar Asamu matsala”har fahad shariff ya shigo yayi sallama Amaan bata saniba”kallo d’aya yamata ya d’auke kansa yana lura tunani takeyi”gefen kujera ya zauna fuskarsa kamar kullum Ad’aure”yasha wankan suit bak’ak’e sunyi masifar haska fatar jikinsa….. k’amshin turarensa me dad’i daya cika wajen shine yasaka Amaan saurin kallon cikin parlourn”tana hangosa tasaki murmushi zumbur ta mik’e tsaye tana fad’in hamma nah yaushe ka shigo?”yana zaune yana Aikin danna waya kallo bata isheshiba”k’asa ta duk’a tana fad’in Ina kwana?”be Amsaba sai cewa yayi dama kina tunanin gulma Ina zakisan na shigo?dukda ga yadda take bata hayyacinta saida taji yabata haushi “sai bata koma mgn ba ta mik’e tsaye takoma inda take zaune”Ahaka baba ladi ta fito suka gaisa dashi ya tambayeta koda Akwai wani abu da suke buk’ata?”tasanar masa babu”daga haka ya mik’e tsaye yasaci kallon mutuniyar tasa datak’i koda kallon inda yake ya tab’e baki yasakai yafita….da yamma yana zaune office nashi mus’ab yashigo”da k’yar ya Amsa sallamar tasa”shi kuma yana y’ar dariya yace”haba hamman Amaan Abin bana fushi bane”banaso laifin mansoor yashafeni”ni kaina na masa bayanin dududu shekaransa 4 dayun Aure, babu Abinda yarasa wajen matarsa meye naya k’ara tun yanzun?”ai yabari zuwa nan gaba saiya k’ara”kuma niban sanar masa komai kan Amaan ba”Amma duk yarikice kanta…. tab’e baki shariff yayi yana d’age kafad’a yace”damuwarsa ce! kune matan ke gabanku shiyasa”Abinda nasani kawai idan na sadata da iyayenta ko a ranar zai iya zuwa subashi ita banida damuwa da hakan”mus’ab na murmushi yace”kaima Akwai lokacin da macen zata zama itace a gabanka…..dam! k’irjin shariff yabuga daya tuna kalaman yarinyar mafarkinsa *tukwicine gareka my salfad*…..yanzun ya kuke ciki kaida fareedah?”ya d’auki kusan second 10 kafin yace”zuwa jibi insha Allah zamu gama da babinta”Aikinka na kyau Abokinah”Amma kasan dai Alh isah yasan Ankama Alh tanimu?”duk nasani”kuma yanzun haka tuhumarsa akeyi shida waye keda hannu Aciki Amma yasaka taurin kai”nace su tuhumesa da shoking”gaskiya hakan shine zaifi”Amma dan Allah kamanta da komai ku cigaba da hud’d’a da mansoor”shiru shariff yayi be koma mgn ba”mus’ab daya gaji da zaman kuramen saiya mik’e tsaye yafita”sai wajen k’arfe 6:30 pm shariff ya shigo gidan”baba ladi ce kawai a parlourn “Amaan na d’aki ta shiga toilet”yana rik’e da ledar turarukan datace masa tana so da ledar ice cream d’in da duk yasiyo mata”saidai kuma daya fahimci bata cikin parlourn saiya zauna suka gaisa da baba ladi”Ahaka Amaan ta fito daga cikin d’akin ta canza kaya bana safe bane jikinta”tana ganinsa saita koma d’aki da sauri tana b’ata rai”duk yana lura da ita”baba ladi na murmushi ta tashi tabi bayanta”bbu jumawa ta fito tanata turo baki idanuwanta cike da k’wallah”da Alama baba ladi ce ta turota”tazo ta zauna kan kujerah batayi masa mgn ba”sosai tabashi haushi”yasha Alwashin saidai su kwana Ahaka bazai mata mgn ba…..✍️

wannan book d’in na kudine ! idan kina buk’atar siya serious regular grp 300
Vip grp 1000
via 2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK

Ki turo shaidar biyanki ta what’s app number d’ina 08100084251

Idan kika karanta mun book baki biyani hakk’ina ba ko kika siya kika fitarmun Allah ya isa ban yafe miki ba

Back to top button