Adandi Hausa NovelHausa Novels

Adandi 2

Sponsored Links

*2*

 

Yana fita Rams ta tasheta tace “tashi muje hostel mu kwanta Zeee inajin feeling dinki sosai wlh” itadai batayi mgn ba saboda kowa yasan Samha yasan miskila ce da ake cewa tafi mahaukaci ban haushi.
Motarta ta shiga ta jirasu suka iso taja suka fice maimakon hostel din fita sukayi daga mkrntar suka nufi cikin unguwar Janguza gaban wani matsakaicin gda sukayi parking ta cilla musu key din tace ku wucce kawai bazan samu zuwa birthday din Najwa ba kice mata banjin dadi” tana fadin haka ta sanya key ta bude gdan ta shiga ta sake bude qofar falon ta shiga ta zube a kujera tanajin kanta na juyawa miqe ta shiga dakinta tayi wanka ta dawo tayi sallah ta kuma shiga kitchen tayi jallop din cous-cous ta dawo ta zauna bata iyacin na kirki ba ta koma dakin ta kwanta duk son Samha da yawo ranar a kwance ta yini tana tufkawa da warwarewa sai sha biyu da rabi na dare qawayen nata suka shigosu hudu zubewa sukayi a falo suna mayar da numfashi, itama ba bacci takeyi ba kawai a kwance take don haka ta miqe ta fito sanye da rigar a jikinta tana fitowa Zainab ta zuba mata ido tana hadiyar yawun kwadayin son kasancewa da Samha yana damunta amma tasan ranta nw zai baci ma don duk inda take tunanin tantiranci Samha ta fita amma bata lesbian ke ko mazan ma ita bada kowanne gara take harka ba lamarinta yana bata mamaki Samha ta qware a video sex chat da call sex amma kullum cika baki takeyi batayin sex bata taba yiba kullum fada musu take Mijinta shine zai fara saninta.

 

Nadiya da Zainab cikakkun yan lesbian ne Rams kuwa da Samha sunfi qwarewa a harkar maza.
Zamanta ne yasasu kallonta Rams tace “meye ya hanaki bacci Pretty?”kallonsu tayi tana yatsina fuska tace “inajin wani abu yana damun zuciyata game da guy dinnan idan harda gaske ne abinda kuka dade kuna fadamin akan so to bana tantama na rufta Rams na fada tarkon wanda bansan ya zai karbeni ba Rams” kallonta sukayi suka “waye wannan wanne dan sa’arne?” Dago dara²n idanunta tayi tace “Abdullah…” Miqewa sukayi a firgice sukace “Abdullah kuma Samha?” Itama miqewa tayi ta dora hanunta a kanta tace “na shiga ukuna meyasa qaddarata ta hadani dashi yaya zai karbeni wlh tun lkcn da abin ya faru zuciyata ta kasa hutawa da tunaninsa da farko nayi tunanin tausayinsa nakeji sai daga baya na fahimci zuciya tace ta karbi wani baqon saqo me wuyar fassarawa game dashi wlh inajin wani abu yans ratsa jikina game dashi inason mu’amala dashi inason kasancewa dashi pls kubani shawara ya zanyi friends”

 

Ajiyar zuciya suketa saukewa gurin ya dauki shiru kafin Zainab tayi qarfin halin cewa “kawai Ina ganin kudi zaki sakar masa ki fito masa da ainihin kyawunki da surarki namiji ne kuma inada yaqinin lafiyayye ne dole zaiso kasancewa dake daga haka kawai saiku soma rayuwa dashi….” Saurin daga mata hanu tayi tace “ya isa haka Zainab bakisan so ba Nadiya inajin taki shawarar” ajiyar zuciya tayi tace “ki bishi a hankali kada kiyi gaggawar nuna masa ki rinqa shiga jikinsa a hankali sannan kisan duk wata hanya da zakibi domin siye zuciyarsa”

 

Juyawa tayi ga Surry tace “kefah?” Numfashi taja tace “ni nama rasa abin cewa kibi shawarar Nady kawai idan da gaske kike sonsa amma banda abinki ma me zakiyi da qazamin guy dinnan ko wanka bai I dauka ba don Allah kada ki zubo mana da ajinmu mana pretty ga guys na masu tafiya da zamani daidai dake zaki biyewa wani alaramma…..”

 

Kallon da taga Samha tana watsa matane yasata saurin tsuke bakinta Rams ta cafe da cewa ko ki yarda ko karki yarda Abdul ba tsaranki bane ba kuma abin kunya ne a gurinki damu kanmu ace wata cikinmu tanason kucakin yaron nan balle keda kanki meye ma ya burgeki dashi dan Allah meye abin sha’awa a gurin wannan yaron don baikai matsayin dazan kirashi haka kema pretty ki basar kawai ki dauki abin a matsayin raha” daga mata hanu tace “ya isa haka Rams kin sani ba abune me sauqi bayar da soyayya a gurina ba tunda baku tabajin koda wasa na bawa wani ba amma idan na badata bana qwace ta sannan abu qarami shine yake burgeni a mutum harma na mallaka masa abu mafi tsada a rayuwata so Rams jarumtakarsa itace abu na farko daya burgeni don haka nayi alqawarin zanyi juriya da hqrn duk abinda zan fuskanta gareshi har zuwa lkcn da Allah zai cikamin burina ku daina tunanin so irin na sha’awa nake massa aa so irin na aure nakeyi masa”

 

Tana fadin haka ta miqe ta shige dakinta ta kwanta sun jima a falon suna jinjina girman al’amarin da shugabar tasu ta dauko kafin Nadiya da Zainab su tashi su shiga wani dakin data basu suke kwana ita kuwa Surry saurayinta ne yazo ya dauketa saboda itadai Samha ta yarda ta kawo namiji gdanta amma bata yarda wani ya kawo mata ba.
Rams ce ta shiga dakin Samha ta ganta kwance ta zubawa p.o.p din saman dakin ido dafata tayi tace “ki fahimceni pretty wlh guy dinnan wulaqantaki bashi da mutunci baya shiga harkar mata ko kadan yanada aqidar tsiya abokin man-son nefah duk iskancin Manson tunda suka hadu yayi sanyi damma dasu Ja’afar suna dan janyeshi ” tunda ta fara mgnr har ta gama miskilar batace komai ba dole taja bakinta tayi shiru ta koma ta kwanta.

 

Da safe da wuri Samha ta tashi ta hada tea tasha ta shirya lkcn suma sun tashi duk sun gama shiryawa ita kawai suke jira ta fito cikin takunta na isa ta suka fita lkcn har almajirinta ya wankenta motar, yau a nutse take tuqin ba kamar ko yaushe ba harta shiga makarantar ba iya su Rams ne kadai suke mamaki ba harma da sauran dalubai saboda sanin kansu ne hakan sabon abune a gurinta.
Can nesa da inda tayi parking ta hanqeshi zaune saman wata mota qirar HONDA da wani littafi a hanunsa ta jima a zaune cikin motar ta dora habarta saman sitiyarin motar tana kallonsa yayi mata kyau sosai cikin qananun kaya blue jeans da black shirt me gajeran hanu dantsensa cikakke me cike da gargasa sumarsa tasha gyara da dan siririn sajensa daya qara mawa fuskarsa kyau.

 

 

Bude motar tayi batare da tayi tunanin komai ba ta nufi gurinsa rungume da takardunta na karatu sai wayoyinta guda biyu sanye take da qananun kaya riga da wando pencil ta gyara gashinta me yalwar tsayi tayi donunt dashi dan qaramin mayafi ne a kanta ta rufe gashinta dashi wanda da yawan mutane suna dauka gashin kanti ne saboda tsayinsa da baqinsa rigarta armless ce mara nauyi amma ta sauka har zuwa cinyoyinta shigarta kenan tunda ta shigo makarantar shekara biyu kenan tana qarasawa tayi masa sallama cikin siririyar muryarta tace “Assalamu Alaika Barrister Abdullah barka da hutawa”

 

 

Back to top button