Hausa NovelsNi da Patient Dina Book 2

Ni da Patient Dina Book 2 Page 49

Sponsored Links

suna kokarin barin dakin zeenat Abba da ummi suka shigo dubata , ganin su adakin ne abba yace ” Kuna nan kenan ? fatima ya kikejin ki yanzu fatan ba wata matsala ko?” amsawa fanan tayi da ” eh abba bakomai” kanta a kasa zama ummi tayi akan gadon tana magana da zeenat kafin ta juyo gun fanan fuskanta da dan damuwa tace ” my feena Allah ya miki albarka, tabbas ke alkhari ce acikin rayuwarmu bamuda bakin da zamu gode miki kedin ya ta garice ” wasa kawai fanan takeyi da yatsunta tana sakin murmushi dan taji dadin adduah ummi, Mr azaad yana zaune yana binsu da ido seyaji sun matukar burgeshi haka zalika abba ganin irin kaunan dake tsakanin ummi da fanan duk da sudin sirkanun juna ne . ( Yanada kyau ya kasance tsakanin ki da uwar mijinki ko matar danki akwai kyakyawar mu’amula , bakomai yake kawo hakan ba fa ce kyautatawa Koda uwar mijinki bata wani sonki ke yakamata kisamo hanyar da zata fara kaunarki domin kyakyawar mu’amula da ita ze kara miki mutunci da kima a idon mijinki barinma yaga yanda kike kyautata mata ,girmamata, koda yaushe kidinga bata girmanta yanda zakiwa mijinki biyayya itama kiyi mata tunda ita ta haifeshi har ya auroki to kinga kuwa bazeji dadi yazama bakya mutunta uwarshi ba , rashin kunya banaki bane barinma da uwar miji wasu ko kadan basa ganin mutuncin surkan su a zo a ta kana nan maganganu , yanda bazakiso a rena mahaifiyarki ba karki rena mahaifiyar wasu Kuma hakan shizesa batare da bata lokaci ba ki fara fita aran mijinki da kuma family shi har azo ana maganar zaa hadashi da wata ya aura tunda ke kin renasu.
Abinda zakiyi domin siye zuciyar dangin miji shine yawan kyauta inde kinada hali kidinga musu kyauta ko bama na wani abu ba wata rana de kiyi girkinki me dadi ki tura musu, sannan kowa kidinga bashi respect yanda yakamata, babu ruwanki da sa kanki a kana nan maganganunsu koda kinji kowa na tofa albarkacin bakinshi kija naki bakin kiyi shuru dan yanzu abin magana baya kadan abinda zaki tofa daban abinda zaa canza kince daban tsakaninki dasu Allah yakyauta bawai kuma hakan na nufin ba ruwanki da damuwar family bane ah ah. Se abu na gaba ziyara musamman ma mahaifiyarshi , wannan de sune kadan daga ciki.
Se kuma uwar miji in danki nada mata babu ruwanki dasu babu sa ido dakuma korafe_korafe kikama girmanki yanda sirkanki bazata samu hanyar renaki ba , karda kidinga nuna mata kyara hakan zesa taja baya dake dakuma family.)
Sallama suka musu suka koma part dinsu hanyar bedroom dinta tayi yariko hijab dinta har cikin bedroom dinshi dariya takeyi ganin yanda ya kwabe fuska barinta yayi yashiga toilet yayi wanka fitowa yayi yasamu bata dakin shiryawa yayi ya hau gadon ya kwanta batare da ya kashe light din ba . dauke da sallama a bakinta tashigo hannunta rike da cup din coffee yana tiriri tana sanye da hijabi dogo ajiyewa tayi tazauna agefenshi tace ” Mr azaad ga coffee” bece mata komai ba yadauka yafarasha da ya gama yakoma ya kwanta lura tayi da yan maganan basa kusa cire dogon hijab din tayi wasu sexy outfit ne ajikinta wayanda da su da babu duk daya mini skirt take sanye dashi na roba daya tamketa tam se rigarshi yar karama kamar vest gashinta tayi donot dashi atsakiyar kai jikinta se tashin kamshi yakeyi , arba yayi da kyakyawan surarta yana daga kwancen be mike ba yamata alama da ta kwanta ajikinshi hakan tayi , tayi lamo ajikinshi idonsu alumshe rike kugunta yayi dakyau sannan ya sa hannu ya warware donot din datayi da gashinta dan yafison su ahaka zubowa gashin yayi yarufe musu fuska mirginawa yayi da ita takoma kasa shikuma yamata rumfa da faffadar kirjinshi kare mata kallo yayi daga sama har kasa lokaci daya yaji kasala yarufe shi murya a shake yace ” baby irin wannan kwalliya haka za ki barni kuwa ?” Yar murmushi tayi daya kara mata kyau tace ” Mr azaad……” Yatsanshi daya ya daura akan libs dinta hadiye abinda zata fada tayi girgiza mata kai yayi yana fadin ” shiiiish ! daga rana kamar ta yau karki kara kirana da wannan sunan banaso” ” tom Mr azaad mezan kira ka dashi ?” dafe goshi yayi yana ” oh my God” kunshe dariyar da yake kokarin fitowa tayi dan tasan metayi , rike habarta yayi yace ” nace miki banason wannan Mr azaad din ” tsayawa tayi tana kyafkyafta mishi ido kamar bata gane me yake fada ba kafin tace ” Mr azaad na gane me kake nufi amma ai bansan dame zan kiraka ba” tsura mata mayun idonshi yayi lumshe idonta tayi dan bazata iya kallon cikin nashi idon ba sake daga habarta yayi yace ” ki kalli cikin idona fanannnn” kamar wata qadangaruwa tafara girgiza mishi kai magana yakara mata ” meyasa bazaki kalla ba? in harde na isa dake ki kalli cikin idona ” babu yanda ta iya haka ta dago ta kalleshi ido cikin ido , jitayi jikinta yayi sanyi sosai kallon cikin kwayar idonshi ya kashe mata jiki lumshe idanu tayi kamar wata me jin bacci tace ” na kalla habiby” , manna mata kiss yayi a kumatu jin sunan data kirashi dashi, sunce igiyoyin rigar yafarayi ta baya yafara shafata shuru tayi tana jin abinda yake mata, cire mata rigar yayi ya zubawa dukiyar fulaninta ido sa hannunta tayi ta rufe ido dan kunyanshi takeji musamman yanda taga yazubawa kirjinta ido, rufe su yayi da bargo yana wasa da ita, fanan so takeyi yayi sex da ita amma taga bedama alamar hakan kasa shuru tayi kasa_kasa muryanta a narke tace ” Mr azaad kaban hakkina yau ina bukatarka” dakatawa da romancing dinta da yakeyi yayi yazubawa kyakyawar fuskanta ido jin maganar da ya fito daga bakinta yamutsa fuska yayi kamar bazeyi magana ba kuma can yace ” baby you’re to young bazaki iya daukana ba ki bari nan gaba inkin kara girma kinji” sosai kalamansa suka batawa fanan rai jin wai she’s very young, mikewa tayi ta lullube jikinta da blanket din tabar mishi dakin , bedroom dinta tashiga tasa key ta rufe toilet tashiga tayi wanka tasa wani kayan baccin ta hau gado tayi adduah bacci takwanta duk ranta a dagule .
Rike kai yayi ganin babyn nashi tayi fushi ta tafi , ita bazata gane me yake guje mata ba tayi yarinya sosai tausayinta yakeyi yafiso ko da zeyi wani abu da ita seta kara girma tunani yakeyi taya ze lallasheta sannan ya fahimtar da ita, yanda yake sonta bazeyi abinda ze sa tasha bakar wahala ba, haka jiki asanyaye yatashi yayi wanka yanufi bedroom dinta knocking yayi tana jinshi taki tashi balle ta bude mai haka har ya gaji ya koma nashi bedroom din gaba daya yayi abin tausayi.

Tun datayi sallah asuba bata koma bacci ba seda ta gyara musu part dinsu ko ina yana daukan ido da kuma kamshi dawuwa yayi daga masallaci yasameta tana kunna burner tsayawa yayi akanta yayi shuru , dagowa tayi fuska ba yabo ba fallasa tace ” Ina kwana Mr azaad?” be taba ganin ta canza fuska ba sede in kuka ne tayi amma ganin yanayinta nayau yasake tabbatar mishi da jiya kwana tayi da bacin rai kuma shi bawai yafadi maganar dan yabata mata rai bane, numfashi yaja sannan ya furzar yace ” wifey fushi kikeyi da ni ne?” cigaba da abinda takeyi tayi batare da ta kalli inda yake ba tace ” ah ah” ” to in ba fushi kikeyi dani ba meyasa jiya kika tafi kika barni gashi yau mood dinki ba kamar yanda nasani ba?” cewar Mr azaad dake zama a gefenta gama kunna burner tayi bata tsaya bashi amsa ba ta wuce bedroom dinta ta kwanta dan maida baccin safe , yau de Mr azaad ji yayi kamar yasa ihu dan yarasa yanda zeyi ya shawo kan fanan ta hakura duk wani abu dakuma hakuri yayi amma daga bayama dena mishi magana tayi sede tadinga binshi da ido kamar batasan abinda yake fada ba. badan komai fanan ta mishi haka ba se dan tasan inde bayasan bacin ranta ze mata abinda take bukata domin hakan shine babban abinda takeso ta aiwatar kafin ta tafi amma shi baze gane bane hakan ba karamin taimaka musu zeyi ba .

After one month.

yau wata daya da rasuwan mansoor,haka kuma saura wata biyu da sati uku auren fawwaz da suhaima.

Mr azaad yanzu duk ya susuce kwata_kwata fanan ta dena kulashi dan bayan abinda yafaru a wannan ranar ta yafe mishi sunci gaba da mu’amularsu ranar da ta nuna tana bukatar shi nan ma yasake fada mata abinda ya fada mata kwanaki tunda ga wannan ranar ta canza mishi , haka ya koma kamar wani mara lafiya ita kanta daurewa takeyi ji tayi bazata iya cigaba da shareshi ba saboda bashi take horarwa ba kanta take horarwa.

 

Back to top button