Kurkukun Kaddara Book 2 Hausa Novel

Kurkukun Kaddara Book 2 Page 22

Sponsored Links

_~*BossLadiesWriters*~_

_*KURKUKUN ƘADDARA*_

~Middle step~

_The Prisoners E22_

 

*Daga alƙalamin Boss Bature*

 

_UMMIN AMERICA_

 

A hankali ta zuro ƙafarta ɗaya daga cikin motar wow, high hills ne launin army green sanye a ƙafarta, sunyi bala’en yi mata kyau, Launin fatar ƙafarta ka ɗai abun kallo ce, kai kace hasken rana bai ta6a shafarta ba, tsabar kyan fatar da salƙinta.

Tun kafin ta ƙarasa fitowa sojojin suka sassauta fushin fuskarsu, Jikin kowan nan su yai la’asar ƙamshin shu’umin turaren jikinta ya daki hancinansu har cikin maƙoshin su fragrance din ya ratsa, Tabarakallahu ahsanul khaliƙin, gaba ɗaya ta tafi da imanin su, basu san sa’adda Bindugun hannunsu suka faɗi ƙasa ba, Ta yi matuƙar tafiya da hankalinsu, wani irin mayataccen kallo suke bin surar jikinta da shi kamar zasu kai mata hari.

Black american ce, A zubin halitta tana da tsayi da jiki, Launin fatarta Chocolate colour ne, Bodycon ce a jikinta, long sleeved gown dai dai gwiwa rigar ta tsaya mata launin Army green, daga ganin ta kaga ƴar duniya hayaƙin taba, baƙar a shana ƙona gari, Irin Ruƙaƙƙun karuwan nan ne Waɗanda suka amsa sunansu A harkar Bariki,Wannan da kuke gani bakowa bace face UMMIN AMERICA, hamshaƙiyar macace mai zaman kanta, Idanuwanta A tsaitsaye suke, Bata da mutunci, kuma bata da kunya ko misƙala zarratin,Tun daga kan shigarta zaka shaida fitsararta, Gaba ɗaya rigar ta bayyana tsiraicinta, boobs ɗinta sun cika faffaɗan kirjinta, tamkar zasu fasa rigar su fito waje don atakure suke an matsesu.

Flat tommy ɗinta tamkar ba’a saka abincin acikinsa tsabar ɗamewarsa, ga Uban qugu dake gareta tamkar ɗaura mata shi akayi saboda faɗinsa, ko kofi aka ɗaura a tudun mazaunanta tsaf zai zauna batare da ya faɗo ba.

Wani irin daddaɗan ƙamshine ke fita saƙo da lungu na Jikinta.

Round face gare ta,Tasha Uban make up, tamkar an zanata don kyau, Ga eye lashes da akayi mata fixing masu tsayi, dogon hancinta Na manne da Nose ring mai kyan gaske, Haka yatsun hannunta na dama na sanye da knuckle ring, long nails din yatsun hannunta fixing dinsu akayi.

Sumar kanta tasha gyara, sai dai daga gani hair wing ne ta daura ba asalin sumar kanta ba, amma zai wuya mutun Ya iya ganewa.

Hankalin maza fa ya tashi haiƙam, gaba daya sun rasa natsuwar su, sai faman haɗiyar yawu suke yi kamar zash lashe ta.

Muryarta tamkar ana busa sarewa ta furta”Zan Iya shiga Ciki”? Har suna haɗa baki wurin bata amsa da cewa”You’re welcome”

shu’umin murmushi ta sakar masu, har dimple din gefen fuskarta Ya lotsa, juyawar da za ta yi, mazaunanta suka girgiza gaba daya sojoji suka zabura tamkar zasu tallabe mata shi.

Komawa Cikin motar tayi, kafin ta rufe motar, wani daga cikin sojojin yai saurin datse mata murfin, A tsanake taci gaba da yin driving ta nufi cikin head quarter din.

Ta tafi tabar su da jarabar kallon surar jikinta da su ka yi, ba zasu iya jurewa ba ai ko da sauri suka nufi cikin head quarter din donsu samu damar ƙare mata kallo ko sun rage raɗaɗin da zuciyarsu ke yi masu.

Bayan tayi parking ɗin motar, ta fito hannunta ruƙe da i phone dinta, Hankulan sojojin dake Zarya a headquarter din gaba ɗaya ya dawo kanta, kamar sun samu talabijin, Matarce akwai Iya jan hankalin maza da surar jikinta, duk idan Tayi taku ɗaya jikinta sai ya girgiza hakan ba ƙaramin hayaƙa maza yake yi ba.

All eyes on her, Sojojin Tamkar zasu kai mata hari, sai dai ba damar Yin hakan,Wani irin ƙwarjini gareta, A fuska bata da wasa, Zazzafa ce, Me zaman Kanta.

Ta wutsiyar ido take kallon masu ɗago mata hannu da masu yi mata alamar suna son yin magana da ita.

Ko kallo basu ishe ta ba, jefi jefi takan ɗan wurga eye balls dinta akansu, da gangan take kashe masu ido ɗaya ko ta ciji lower lip dinta da harshe, ɗabi’arta ce Yin hakan, duk don ta ƙara hayaƙa su.

Kaitsaye ta nufi hanyar da zata sada ta da office din commender domin amsa kiran da yayi mata, tasan ko’ina na headquarter din, don ba baƙuwarta bace, Ba yau bane rana tafarko da ta fara shigarta.

Tun kafin ƙarasowar ta, tuni Anyi mata iso wurinshi, jiranta kawai Yake yi, yana daga zaune saman chair, acikin katafaren office dinsa, komai na cikinsa army green ne, hatta desk din gabanshi, dake dauke da computer dinsa, da wayar hannunsa tare da flag and map, daga jikin bangon office din akwai book shelf, da jerin hotunansa da awards dinsa, bashi kaɗai bane a office din hada Major.

Shigowarta office din, Tuni sanyin Iskar A.c ɗin cikinsa ta gauraya da ƙamshin shu’umin turarenta.

Har saida suka shaƙe shi sosai a hancinansu.

Da kwarkwarsa ta ƙarasa gaban desk dinsa, kamar yadda ta saba yi mashi duk in tazo office dinsa haka yau ma tayi mashi, Ta buga ƙafa tare da sara mashi, hakan ba ƙaramin ƙayatar da shi yai ba, har sai da suka saki murmushi, tun kafin Ya bata iznin zama, ta zauna saman chair din dake facing dinsa, ta ɗaura ƙafa ɗaya bisa ɗaya, murmushi ta sakar mashi haɗi da ɗaga mashi gira ɗaya ta kashe mashi ido.

A wayance ta soma yin magana cikin harshen turanci”fatan na same ku lafiya” lumshe ido commender yai tare da kai hannu ya gyara zaman wuyan rigar kakinsa.

“Lafiyalou ummi, I’m glad to see u, Ina fata kiran da mukayi maki bai taƙura maki ba”?

Ɗaga mashi gira tayi alamar eh ba tare da ta furta ba, a mutunce suka gaisa da junansu. Bayan kowan nan su ya natsu, Major Ya miƙe ya bi ta ƙofa ya fuce waje jim kaɗan ya dawo hannayen shi ruƙe da mugs na coffee guda biyu ya ɗaura su saman desk, ya ɗago da ido Ya kalli Ummi”zaki Iya sha” ta furta okey, kafin takai hannu ta dauki mug din ta soma kur6an coffee din, da alama ya yi mata dadi kusan sau uku tasha kafin ta ajiye mug din, ta dawo da dubanta ga commender”am all eyes”

“Dalilin da yasa na kira ki ummi, Magana ce mai muhimmanci muke san yi da ke, Ina fata za ki bamu haɗin kai kamar yadda kika saba taimakon mu” cikin harshen turanci commender yayi maganar a tsanake.

Hankalin major na akan ƙirjinta har wani ƙara leƙensu yake yi kamar zai zura kanshi cikin rigarta.

Kallon da Commender ya watsa mashine yasa shi saurin kawar da idonshi ya kame mutuncin kansa

“Babu takura, ko da yaushe ina maraba da ku, zaka Iya faɗin komai ka ke so kai tsaye”

ta ƙare maganar tana shafa saman boobs dinta da yatsun hannunta.

Yawu commender Ya haɗiya Kutt throat dinsa Ya bada sauti, shi kanshi daurewa yake yi, surar ummin America na neman kwance mashi masarrafinsa.

“Ina so ki natsu ki fahimce ni kafin ki bani amsa” amsa mashi tayi da toh
Bayani ya soma yi mata dalla dalla tun daga farkon tsintarsu Angel da su ka yi a Daji, har izuwa kawosu asibiti, da kuma abun da su ke buƙata daga gare ta, tunda commender ya fara labarta mata, ta natsu tana sauraronshi.

“Muna so ki bamu haɗin kai wurin Kula da yaran ki ruƙe su tamkar ƴa’ƴanki, munsan zaki Iyane shiyasa muka za6e ki, tun da ba yau kika fara yi mana aiki ba, mun yarda dake ummi, burinmu ki tarairayesu ta yadda yaran zasu yarda dake har su Iya faɗamaki ainihin abun da ya faru arayuwarsu’ ya ƙarasa maganar idonshi akan fuskarta.
Lumshe ido ta ɗanyi kafin ta waresu akan fuskarshi

“ta ya ya zaku yi tunanin damƙa amanar yara har goma sha ɗaya a hannuna? Bayan kunsan wacece ni, Ban ta6a haihuwa ba, kuma ni banason Rainon ƴa’ƴa, ban ta6a sha’awar haihuwarsu ba, balle har in iya kula da yaran wasu, Ina mai baka haƙurin Cewa Ni bazan Iya wannan aikin ba! zaifi ku samu macen da tasan zafin haihuwa mai kamun kai ku bata rainon su” tana magana jikinta na jijjiga, major duk yabi ya susuce ya rasa natsuwarshi, ba dan commender na akusa ba da ba abun da zai hana ya damƙeta ko da zai sha mari ne.

“Ummi, Ki sassauta kalamanki, Kina yi min magana da tsiwa, Ko kin manta a ina kike ne? Ki duba da kyau ki gani, nan ba club ba ne, ba kuma gidan karuwai bane, sannan ba ga6ar taku bane, Head quarter din sojoji ce” Ya yi maganar tare da zaro bindiga daga cikin drawer chest na desk din gabanshi Ya daurata saman desk din.

Tuntsirewa Tayi da dariyar rainin wayau

“Kai ma ka sani, Ummin america bata tsoron bingida, ni da ni ke yin mu’amala da masu ruƙeta, yanzu haka da nake yi maka magana shigowa ta head quarter din nan gaba ɗaya na tada masu jarabarsu, suna can waje, wandunan su sunyi masu nauyi’ cike da shaƙiyanci tayi maganar, ta riga ta gama raina su bata jin tsoron su ko kaɗan.

Cikin kwantar da murya commender yace”is ok, kibar yi min wasa, Muyi magana ta hankali, ki taimaka ki kar6i buƙatarmu, kome kikeso zamuyi maki, sannan ɗawainiyar yaran da komai nasu mune zamu bada tallafin da za’a cigaba da kula da rayuwarsu, tun daga cinsu shansu, suturarsu, da karatunsu, Iya taimakon da muke so kiyi mana kija su a jiki ki zama tamkar mahafiyarsu” yamutsa fuska tayi tana faman wurwurga eye balls dinta tace”Kana nufin wai a gidana zasu zauna? Ka san gidana gidan mazane, a koda wani lokaci Ina busy wurin biya masu buƙatarsu, how ka ke tunanin zasu Iya samun kulawar data dace? Kuma naji kace yaran suna fama da depression hada me ciwon ciwo, gaskiga ba ƙaramar ɗawainiya bace kula da su, bazan Iya ba commender, kada ka tursasamin, kasan ina girmamaka saboda halaccinka agareni”

Kallon major commender yayi, hakan ya bashi damar Yi mata magana

“Ba zamu takura maki ba, amma kafin ki tafi Inaso zan nuna maki hotunan Yaran Ki gansu”

Miƙewa Major yai daga saman kujerar da yake a zaune Ya zagaya ta 6angaren Commender Ya juyo mata da laptop din saitin fuskarta.

Operating ɗinta Ya soma Yi, hotunansu Angel Ya buɗo, daga kan hotonta Ya fara Nuna ma Ummin america
“Sunanta Angel” Ya ambaci hakan yana kallonta, da alamun mamaki akan fuskarta ta furta “wow she’s beautiful sai dai daga ganin bakinta za ta yi tsiwa, ni kuma bana sha’awar Yara masu masifa” ta faɗa haɗi da yamutsa fuska, still murmushi ne akan fuskar major da commender.

Hoton Batul ya nuna mata, sai da ta ta6e la66anta kafin tace “tana da kyau, sai dai daga ganin fuskarta bata da masifa, wannan ko yatsa aka sanya mata abaki bazata Iya cizon shi ba” ta kare maganar tana hura hanci.

Hoto na gaba fuskar Hanna ce, Ummin america tace”har ƙwara Yarinyar daka wuce akan wannan, taci ka sanyi daga gani babu kuzari a jikinta” yadda take fayyace ɗabi’unsu kamar ta ta6a ganinsu.

Ko da akazo kan Hoton Parveen Ya cika screen din laptop din.

Da buɗar bakin Ummi sai cewa tayi”yarinyar nan daga ganin kumatuntu mayyar abinci ce, zai yi wuya idan ba asame ta da shegen ci ba, Ni bana so mutun mai ciye ciye” murmushin fuskar Major da commender sai ƙara faɗada yake yi, don ba ƙaramin nishaɗi take basu ba.

Hoton Jamimah Ya nuno mata, waro ido waje tayi hada sanya Hannu ta dafe saman ƙirjinta.

“Major, ruƙon wannan Yarinyar ai sai likitan mahauka, shi kaɗai ne zai Iya sarrafa ta, ba dai ni ba, Ni ina zan Iya kula da ita, daga ganin bakinta zatayi tsiwa” Major yayi dariya tare da nuno hoton Azeeza, shiru tayi tana ƙare mata kallo, kafin ta ɗago da ido ta kalli Major”sai naga kamar ƴan biyu ne ita da Yarinyar da ka nuna min kafin ita, sunyi kama” Major yace”haka muke tsammani, sai dai muna hasashen azeeza tafi Jemimah shekaru kamar yadda ɗan uwansu ya faɗa mana”

Yamutsa fuska Ummin america tayi”tana da kyau sai dai daga ganinta matsoraciya ce, wannan ko tsawa na daka mata zata Iya sakin fitsari a wando, gani da tsiwa bansan ya zamu ƙare da ita ba” ta fada tana ta6a baki tace”wai Iya matane Yaran”? Ta yi tambayar tana kallon Fuskar Major

“akwai maza” ya bata amsa, a dai dai kan hoton Haris Ya buɗe mata shi.

“Sunan shi Haris, shine yaron da commender Ya faɗa maki cewa Yana fama da ciwon zuciya”

Ta6e baki tayi”nifa banason namiji mai raunin zuciya, daga gani baya da hayaniya ba laifi yana da kyan fata” ta faɗi hakanne saboda kasancewarta baƙar fata, tana son mutun me duhun fata.

Wuce hoton Haris yai adai dai kan hoton Javed ya dakata Yana dubanta

“Amma dai wannan Yaron ɗan south korea ne ko?

Major yace”bamu da tabbacin ɗan Ina ne, duka yaran bamu san wani jinsi bane, sai dai sun faɗa mana cewa Ƴan Nigeria ne” da sauri ummin america ta girga kai tana fadin”Impossible, babu kalan waɗannan a nigeria, may be sun yi loosing memory ɗin su ne shiyasa su ka faɗi hakan”

Hoton Naufal Ya budo mata, lumshe ido ta ɗanyi tare da waresu akan kyakkyawan fuskarshi
“Wow, kaga Namiji, sumar kanshi ta burge ni, Yayi min kyau” ta yi maganar tana hura mashi kiss.

“Yaro ne” Commender ne yace haka,
Ummi tace”Ai shi namiji baya kaɗan, especially idan abunsa ya ruƙa, a wurina wannan ba yaro bane Namiji ne” murmushi suka saki, basu damu da abun da tace ba saboda sun san halinta, bata mu’amala da matasan samari, Sai mazan da su ke da aure waɗanda tasan idan ta bibiyesu za’ayi bala’i idan matansu suka kamata.

Bayan Ya wuce hoton Naufal Ya buɗe mata hoton Gabriel, tunda ta kafe shi da ido bata ƙyaftaba sai faman jinjina kanta take Yi alamar mamaki

Can dai ta numfasa tare da cewa”Allah Ya yayi halitta, gaskiya idan aka bani rainon yaran nan tamkar kun ba kura ajiyar nama ne, major idan akwai wani hoton nuna mini na ƙosa na ƙarasa ganinsu”

Lokacin da Major Ya hasko mata hoton Danish daga zaune ta zabura ta miƙe tsaye tana duban fuskarsa data cika screen na laptop din, duk suna akwance akayi masu hotunan idanuwansu arufe.

Muryarta tamkar tame Yin raɗa ta furta “Speechless! Major Ina kuka samun Kyakkyawar matashin nan mai kama da ɗan sarkin aljanu? Anya Cikakken mutunne? Ko dai A cikin Dajin da kuka tsintosu Aljana ta haife shi Ta yada” dariya kowan nan su ya saki jin sambatun ummi dama sai da ransu ya basu zata ruɗe idan taga hoton shi.

Major yace”sai ma kin ganshi a zahiri, ba ƙaramin kyaune da shi ba”

Ko da ta koma ta zauna, sam takasa ɗauke idonta daga kan fuskar Danish, Yayi matuƙar tafiya da imaninta, aranta har ta fara Ayyana koya surar shi zata kasance a zarihi?

Muryar Commender ce ta fargar da ita ga dubanshi”dukansu ne muka nuna maki, shin kin canza ra’ayinka akan kula da su ko kuwa har yanzu kina akan bakanki”

Shiru ta ɗanyi tana yanke shawara da zuciyarta, duk sun ƙagara da son jin amsarta.

“Yanzu haka case din Yaran mun miƙa shi hannun shugaban isod, shine zai cigaba da jan ragamar bincike akansu, jiya muka samu amincewarshi na kar6ar case din nasu, sai dai ya nuna baya buƙatar 6ata lokaci yanason ya tafi tare da yaran can nigeria a jet dinsa, a satin da zamu shiga”

Lokaci ɗaya ummin america ta canza fuskarta zuwa 6acin rai, da farko tayi murnar jin cewa Case din Yana a hannun chief na Isod, daga bisani daya furta komawa Nigeria ne taji komai ya fita aranta.

“Naji kin yi shiru, baki ce komai ba”
Ajiyar zuciya ta sauke kafin ta soma magana ranta a6ace”Idan har kuna so in ruƙe Yaran a hannuna, they should stay in America. I will not follow them to Nigeria,”

Commender yace”amma meyasa? Ke kanki fa ƴar ƙasar Nigeria ce why baki son zuwa ƙasar Ki”

Girgiza kai Tayi still fuskarta da 6acin rai ta furta”Ni ba ƴar nigeria ba ce, asalina ne acan, amma Ni black american ce, tun da nace banaso mubar maganar kawai, Ni zan koma gidan idan ka gama maganar ka”

Yanayin fuskarta Ya canza sosai, 6acin raine tsantsa, sun fahimci kamar akwai wani abu daya ta6a faruwa da ita wanda har yajawo silar barinta ƙasar, kuma batason Anayi mata maganar komawa can”

Ganin yadda ta haɗe rai babu annuri ko miskala zarratin akan fuskarta, Yasa Commender cewa”Shikenan ki kwantar da hankalin ki, ba zamu takura maki ba, Zaki Iya tafiya” ba don yaso ba ya ambaci hakan, duk basu ji daɗin canzawarta ba, muryarta a disashe ta furta”thank u” ta yunƙura ta miƙe ta nufi ƙofar fita daga office din, Har ta kusa ficewa Muryar Commender ta katse mata hanzarinta”duk da bansan abunda ya faru dake a ƙasarki ba da har yasa kika tsani jin an ambaci sunanta, da akwai wani abu da nike so in faɗa maki ummi” yayi maganar tare da miƙewa hannun shi ruƙe da mug na coffee, Ya kur6a kafin ya ɗaure da cewa”wannan dama ce agare ki, da zaki koma ƙasarki a karo na farko ki nuna ma waɗanda sukayi silar barinki ƙasar cewa Kina araye kuma kinsamu cigaba a rayuwarki ba kamar yadda sukayi tsammani ba, inaso ki basu mamaki ummi, sannan zuwanki Nigeri bana dundun bane na ɗan lokacine zaki dawo nan da zarar Mun samu nasara akan binciken Yaran, zamu dawo dake nan, saboda mu kanmu ba zamu so mu rasa nagartacciyar mace irinki ba, ke kanki kin sani muna ƙaunarki kuma muna daraja ƙimarki a idanuwan mu, ba zamu so abunda zai 6ata maki rai ba ummi, kina da damar da zaki Iya zuwa gida ki zauna ki yi tunani akan maganata kafin ki yanke shawara.

Kalaman shi sun ɗan ta6ata, tuni zuciyarta ta fara sassautowa, ita kanta zataso wannan damar ta zuwa Nigeria ko dan taba waɗanda sukayi silar barinta mamaki.

Numfasawa ta ɗanyi kafin a hankali ta juya tana kallon commender dake tsaye abayanta, kamar bata son furta maganar tace”babu buƙatar yanke shawara, Na amince Zan bi su zuwa Nigeria, Kuma nagode da karramawarku agareni, da zarar na gama aikin, zan dawo ƙasata”

Murmushi major da commender suka saki, Jin abunda tace, har yanzu bata yadda ta kira Nigeria da sunan ƙasarta ba.

Sun ji daɗin amincewarta, ba tare da 6ata lokaci ba, Commender ya dauko mata kundun dake ɗauke da bayanansu Angel, duka takardun akwai Signature dinsu a jiki, saura sanya hannunta suke buƙata, cikin ƙanƙanin lokaci su ka Ƙulla Yarjejeniya ta (guardianship agreement)atsakanin su da ita, sai da ta natsu ta karanta sharuɗɗansu dalla dalla akan irin rainon da suke so tayima yaran kafin ta sanya hannu a takardun, bayan ta kammala sun bata wasu takaddun yarjejeniyar da zata ruƙe a hannunta.

Bayan tayi masu sallama, Ta fito daga office din, tana tafiya Sojoji Na binta da kallo, Yayin da ita kuma hankalinta na akan takaddun dake a hannunta, Fatanta Allah yasa Ruƙon Yaran da za ta yi da kuma zuwan ta Nigeria Ya zama alkhairi agare ta.

Tun kafin ta ƙarasa gaban motarta da ta bari a harabar ajiye motocinsu, ta hango sojoji dadda6e sun kewaye motar suna jiranta, murmushin gefe fuska tasaki har dimple dinta Ya lotsa, ta fahimci tunda ta shiga office din commender suke ta jiran fitowarta don su yi mata magana, bata tsaya sauraron su ba, daƙyar ta samu suka ƙyaleta ta shiga mota, a tsanake ta tada motar, Ta juya sitiyarin da gudu ta fuce daga head quarter din.

*EX-PRISONERS❤*

Tun ɗazu da safe kowan nan su Ya farka daga bacci, sun wayi gari da jin kyakkyawan labarin farkawar Danish, saboda zumuɗin zuwa ganin shi babu wanda ya nemi breakfast acikinsu, gaba ɗaya sun Hallara a room dinsa, tun daga kan Haris, Javed, Naufal, Gabriel, Batul, Hannah, Jamimah, Azeeza, ƙwansu da kwarkwatarsu sun yi tsaitsaye cirko cirkon suna kallon shi, fuskokinsu ɗauke da Annurin farin Ciki, Ɗaya bayan ɗaya Danish Yabisu ya rungume su a ƙirjinshi, kamar sunyi shekara basu atare da juna, Haris hada kukanshi saboda murnar ganin Danish Ya farka.

Sun tasa shi gaba suna kallonshi kamar zasu lashe shi, Musamman Azeeza da Jemimah, daɗi suke Ji Danish ɗinsu Ya farka.

Muryar jamimah da shagwa6a tace”munyi fushi ma sai yau zaka farka, kullum sai munyi kukan rashin ka, ko bacci bamu Iya yi abincin ma ba mu ci” Harara Azeeza ta watsa mata”wlh ƙarya take yi Danish kullum sai taci abinci sau uku, kuma tana Yin bacci” Murmushi ya saki yana binsu da kallo, Haris dake zaune gefen gadon Danish ya ruƙe hannunshi a Cikin nashi ji yake kamar za a kwace mashi ɗan uwanshi.

“Meyasa Angel Jiya daya farka baki tada mu daga bacci ba? Bayan kinsan irin ƙagarar da muka Yi na son ganin shi” Hanna ce tayi maganar, Gabriel Yace”Ni dai ba abunda zance sai godiya, saboda ba zamu Iya misalta farin Cikin da muke aciki ba, Yau babbar rana ce agaremu ɗan uwanmu abun alfarinmu Ya farka da ranshi da lafiyarshi” yana daga tsaye yake yin maganar Ya goye hannayenshi saman ƙirjinshi.

“Allah sarki Rayuwa kenan, Har na tuna kokawar da Ku ka yi kaida Danish akan nace zan dire taga” gaba ɗayansu suka sanya dariya.

Batul tace”ai mu bamusan abunda ya haɗa su faɗa ba”

Parveen dake tsaye gefen Naufal hannunta ruƙe da Ayaba sai ci take Yi, Kunnuwanta akansu ta natsu tana sauraransu.

Labari Angel ta basu na abunda ya faru lokacin da zata dire taga, ba ƙaramin nishaɗi su ka yi ba.

Azeeza tace”munyi kuka lokacin sosai, Munyi tsammanin Danish ɗinmu zai rasa idonshi ɗaya, sai gashi Allah ya dawo mana dashi da ranshi da Lafiyarshi, gaskiya munji daɗi” da farin ciki akan fuskarta ta ƙare maganar, idanuwan Danish akan faces dinsu, ita da Jemamah.

Parveen tace”ni banaso muna tuna baya, nafi so inji muna magana akan abunda zai faru agaba”

Jemimah tace”Genie yaushe zamuje gidan daddyn naki? Ni na ƙosa mu koma can, waɗannan mutanan masu jan kumatun, kullum sai sun tsira mana allura a ɗuwawun mu” ta yi maganar tare da nuna ass dinta da indext finger dinta, gaba ɗaya suka tuntsire da dariya, Azeeza tace”Kai jamimah ki ji tsoron Allah, Jiya fa ba ayi mana allura ba, nurse ta faɗamin an gama yi mana ita, sai dai magani da zamu dinga sha na tsawon one month” turo mata baki Jemimah tayi
Javed yace”Kufa baku gajiya da abun magana, Kun Cika ɗan uwanmu da surutu, Ko so kuke yi ya koma baccin” atare suka zaro ido haɗi da ɗan buɗe baki”A’a wlh bamu so Ya koma bacci,”

“Alhamdulillah, Tun da yanzu mun haɗu mu dukanmu, Yakamata Muyi wa Allah godiya” Angel Ce tayi maganar, Tare da Ɗaga tafin hannayenta sama, Da sauri suma suka ɗaga nasu zasu yi addu’a, Mutun ɗaya ne bai ɗaga nashi hannun ba, Hatta Gabriel da ya ke Christian sai da ya ɗaga hannunshi don su yi addu’ar atare, Don shi a yanzu baida za6in addini, yafi ƙarfi ta 6angaren musulunci saboda Angel.

Kallon fuskarshi Angel tayi”danish zamuyi addu’a, ba zaka ɗaga hannu ba”
Girgiza mata kai Yayi alamar a’a, ɗaure mashi fuska tayi sai yayi tamkar baisan tana Yi ba
Cikin sanyin murya Haris yace”Danish meyasa har yanzu baka goyan bayan addinin musulunci”?

Shiru danish bai yi magana ba, Kuma babu alamun zaiyi ta.
Damuwace ƙarar akan fuskokinsu
“Pls danish just for today ka ɗaga hannu Muyi addu’a” Muyar Angel tamkar zata fashe mashi da kuka Tayi maganar.

Marairaice mashi fuska Azeeza da jemimah sukayi”Bro pls, let pray together,”

Runtse idanuwanshi Yai, ba tare daya buɗe su ba Ya furta”I can’t, ku daina yi mini magana akan Inyi, bana so”

Sai lokacin Batul ta sanya baki”tun da ya nuna bayaso mu ƙyaleshi, damu da shi duk abu ɗayane, ko da ace baiyi ba mu zamu yi mashi, hakan ma ya wadatar” Angel bata ji daɗi ƙin Yin addu’a da yai ba, addu’oi’ ta soma karanto masu suna amsa mata da ameen ameen, idanuwanta sun cicciko tab da ƙwalla, bayan sun Kammala kowan nan su Ya shafa saman fuskarshi, banda Angel maimakon ta shafa addu’ar da tayi saman fuskarta, sai ta shafa ma danish saman sumar kanshi, a hankali ya ɗago da idanuwanshi yana duban fuskarta, harara ta watsa mashi tare da murguɗa mashi baki, hakan da tayi ba ƙaramin ƙayatar da shi yai ba, muryarshi ƙasa ƙasa ya furta mata”thank u” ta6e mashi baki tayi”kada ka yi tunanin na damu dakai,” ƙayataccen murmushin gefen fuska yasakar mata, Su Batul sun natsu suna kallonsu.

Muryar Dr. laura ce ta katse masu hanzarinsu”Congratulation! My lovely Children Ina tayaku murnar farkawar ɗan uwan ku daga bacci, banjima da shigowa asibitin ba, dr Harry ke faɗamin cewa ɗan uwanku Danish Ya farka, wannan abun farin Ciki ne” ta ƙarasa maganar, a yayin da take ƙarasowa Gaban gadon Danish. Fararen idanuwanta dake asanye cikin farin glass ta ɗaura su kan face dinshi.

“An sanar dani cewa Baya kula kowa sai ƴan uwanshi, dagaske ne masoyiya Angel? Tayi tambayar tare da kallon Angel

Da fara’a akan fuskar Angel ta amsa mata da cewa “Jiya ne amma yau ya saki jiki, zai Iya magana da kowa”

Dr laura tace”Anya kuwa? Naga ko kallona baisan Yi, danish Ya jikin naka? Ko akwai inda ke yi maka ciwo a jikin ka”? Tayi tambayar cikin ƙagara da son jin muryarshi
Cikin raɗa Angel ta furta mashi”danish pls kayi mata magana, sun taimake mu, kuma suna da mutunci” kamar wanda akayi ma dole daƙyar ya iya motsa lips dinsa ya furta”da sauƙi babu inda keyi mini ciwo,”

Dr Laura taji daɗin maganarshi”ina fata kaci abinci babu yunwa atare dakai”? Ɗaga mata kai yai alamar eh
Ta furta”okey, amma meyasa jiya baka ba likitoci damar duba lafiyarka ba”?
A takure yake yi mata magana”saboda lafiyata ƙalau, bana buƙatar a duba ni,” Jinjina kai ta ɗanyi tayi mamakin Halinshi, basu ta6a samun patient irin shi ba.

Muryar Angel ce ta janyo hankalinta ga dubanta”Aunty, mun gode sosai da kulawarku agaremu, Allah ne kaɗai zai Iya biyanku,” tayi mata maganar ne don ta mantar da ita zancen yi ma Danish maganar duba Lafiyar Jikinshi.

“kada ki damu masoyiya Angel, aikin mun e kula da lafiyarku kuma Alhamdulillah, Naga Jiki yayi kyau Allah ya ƙara Lafiya,” ta ƙare maganar tare da kallon Azeeza da jemimah”My twins, Ya jikin naku” atare suka haɗa baki” da sauƙi” kafin ta ɗaura idonta kan Parveen da sauri ta 6oye Ayabar dake a hannunta, dariya dr laura ta ɗan saki”hmm ai na gani dama kin daina wahalar 6oye mini” duƙar da kai Parveen tayi fuskarta ɗauke da murmushi.

Kallonsu Gabriel Tayi”Ƴan samari, Jiki yayi kyau, badan sister dinku ta matsa akan son komawarku Nigeria ba, da a gidana zan killace ku, In cigaba da rainonku,” murmushi kowan nan su ya saki.

“Zan Koma Office, Ku kula mun da kanku” har ta juya zata fuce Angel tayi saurin cewa”Aunty, har yanzu sojojin basu kira ba naji su shiru basu zo sun duba mu ba”

Dr. Laura na niyar juyowa don ta bata amsa, ba zato ba tsammani, Suka hango Dr. Mark tare da dr. brown sun nufo ƙofar ɗakin, Kusan a tare suka shigo.

Gaisawa suka Yi da dr laura, Cikin girmamawa su Angel suka gaishe da su, Bayan sun amsa masu, suka tayasu murnar farkawar ɗan uwansu

Kafin daga bisani Dr Mark Ya soma Yin magana”Dr. Ke muke nema, Sojojin nan sun Kira Awaya, idan ba damuwa zamu Iya zuwa office muyi magana”

Amsa mashi tayi da toh, ba tare da 6ata lokaci ba suka fuce daga ɗakin.

Hankalin Angel yaƙi kwanciya burinta taji me zasu tattauna, fatanta Allah yasa su amince da maganar maidasu Nigeria.

Bayan fitarsu ɗakin kaitsaye office din dr Laura suka nufa, kowan nan su ya samu wuri saman kujera Ya zauna suna fuskantar Juna da ita

“Ina sauraronku, me sojojin suke ce ne”? A ƙagare ta tambayesu
Dr mark Ne ya soma kora mata jawabi”Commender dinsu ne Ya kirani awaya, Ya sanar dani cewa Chief na Isod Ya Amince zai kar6i case din Yaran….” tunkan Ya ƙarasa maganar, dr laura tasaki murmushin farin ciki

“Bayan haka, sun ƙulla Yarjejeniya tsakanin ita ummin american da su sojojin, zuwa Anjima zasu zo asibitin domin shirya yaran, zasu ɗauke su zuwa gidanta, sai dai zamuyi kewarsu saboda Commender din ya faɗamin next week chief na isod zai bar ƙasar tare da yaran” ya ƙarasa maganar idonshi Akan dr laura, mood din fuskarta ya canza zuwa damuwa, ba ta yi tsammanin zasu bar ƙasar da wuri ba, zaman da su ka yi da su na kwana huɗu ba ƙaramin sabo su ka yi da juna ba, sai dai ta wani 6angaren taji daɗi kodan saboda Angel da ta roƙe ta akan ta taimaka masu su koma ƙasarsu.

“Dr lafiya? Naga kamar yanayin fuskarki Ya canza? Ko baki ji daɗin maganar bane”? dr. Mark ne yayi maganar ganin ta haɗe fuska, Murmushin yaƙe tasakar mashi
“No ba haka bane, Na saba da yaran ne, banaso su yi nesa dani, banyi tsammanin zasu bar ƙasar da wuri ba, inaso zan nemi alfarma abar mana su ko da one month ne su yi anan kafin su tafi”

Dr brown yace”ba zai yiwu ba dr, da ace case dinsu a hannun sojojin yake zamu Iya neman alfarmar abar mana yaran su zauna a wurinmu, sai dai kash sun riga da sun damƙa case din hannun chief na isod, kuma kinsan shi ba ɗan ƙasar nan bane, A ƙasar shi yake zaune Aiki ne mai muhimmanci ya kawoshi america, tun cikin weekend daya wuce yaso barin ƙasar, saboda case din Yaran Ya fasa tafiya, yanzu haka da nakeyi maki magana, yana shirye shiryen barin Washinton zai shigo garin mu saboda ya haɗa kan yaran ya tafi dasu, mutumin babu wasa a aikinsa, Baison 6ata lokaci.

Jikin dr. laura ba ƙaramin sanyi yai ba, tana son su Angel, ganin duk ta damune yasa Dr mark kwantar mata hankali”Tafiyarsu ba yana nufin mun rabu da su ba, Kada Ki manta Sojojin ƙasarmu ne suka tsince su, bayanan su da komai Yana a hannunsu, kuma zasu cigaba da bibiyar rayuwar yaran, wannan dalilinne ma yasa suka haɗasu da Ummin america.

Gyaɗa kai Dr Laura Tayi”Ni damuwata depression din dake damun yaran, da kuma Yaron dake fama da ciwon zuciya, Hankalina bai kwanta da Ummin america ba, Shin zata Iya bamu su kulawar da zata sanya su manta da damuwarsu? nafa santa bata da mutunci macace mai izza kuma ta shahara wurin Iya karuwanci…..” Damuwace ƙarara kan fuskar dr laura, idanuwanta tuni sun ciko tab da kwalla.

“Yaran sunfi buƙatar kulawar mace wadda tasan ciwon haihuwa, bawai karuwa ba! Wadda ta saba ƙwacewa matan aure mazajensu tana fasiƙanci da su! Yakamata Kuyi tunani akan hakan, Ni zanyima Commender din nasu magana, akan su canza masu wadda zata raine su, Yara fa har goma sha ɗaya za’a damka ma karuwa, gaskiya basuyi tunani mai kyau ba, zata Iya 6ata su” ranta amuƙar 6ace take Yin maganar.

Cikin kwantar da murya Dr mark yace”ina baki shawara dr, kada kice zaki shiga maganar nan! Tun ranar da major ya kawo shawarar abata kulawar yaran, Kin nuna kuskuren yin hakan, amma sai basu damu ba, saboda sunsan halinta, kuma sunsan zata Iya ne, kamar yadda yace ta saba yi masu aiki, so bai kamata ki damu ba”

Dr brown ya ɗaura da cewa”sunfi mu sanin wacece Ita, Mu sanin da mukayi mata na karuwa ne, su kuma a matsayin ma’aikaciyarsu suke kallonta, ba zasu ta6a damƙa mata amanar yaran ba tare da sun aminta da ita ba”

Gyaɗa kai Dr Laura Tayi”Shikenan na haƙura, bazan yi masu magana ba, amma inaso zan ba Masoyiya Angel Kyautar waya, saboda inaso mudinga Yin magana da ita akai kai”

“Na fahimci kina son yaran sosai, Ni kaina na kamu da ƙaunarsu, Har na fara jin kewarsu” acewar dr. Mark

Dr brown yace”aini har ƙasarsu zan Iya zuwa ganinsu idan naso, don haka banda damuwa, muna atare da su”

Sun jima suna tattaunawa a tsakaninsu kafin daga bisani, Kowa ya koma bakin aikinsa.

*DAULAR ALHAJI MUSA*

*Dr Shureim❤*

Ƴan kwanakin da yayi a gidan Uncle ɗin nasa Rayuwarshi ta fara canzawa, a yanzu dr. Shureim baida matsalar komai, ta kowani 6angare yana samun kyakkyawar kulawa, kullum yana acikin gida, idan ya gaji da zaman ɗaki yakan fito ya zagaye gidan tare da zeenatu, yana matuƙar jin daɗin kulawar da take bashi, sun shaƙu da juna kamar sunyi shekara atare, hatta abincin atare suke cin shi, sai dai akwai wani abu da ya fara damun zeenatu, hoton da yake yawan kallo awayar shi, abun yabi mashi jiki kamar ibada, Idan ya fara kallon hoton baya so kowa yazo kusa da shi, kuma baya son kowa yasan hoton menene yake kallo, duk idan ta faɗo ɗakin shi yana cikin kallon hoton da sauri yake danna power button na wayar ya kashe ta, ta rasa gane wacece yake yawon kallo? Don ta fahimci ba ƙaramin so yake yi mata ba, gashi ita kuma Allah ya jarabceta da masifaffan kishi, ba ta son ganin yana kallon hoton, Har kuka take yi a 6oye ba tare sanin kowa ba.

A Kishingiɗe yake saman katafaren gadonshi, tun safe bai fita ko’ina ba, ko ƙofar bedroom dinsa bai leƙa ba, farin short ne ajikinsa, babu riga, gaba ɗaya hankalinsa na akan screen din apple laptop dinsa dake ajiye saitin kanshi daya ɗaura saman pillow,

Sam bai ji takun tafiyarta ba, saboda hankalinshi baya atare da shi, wankan swiss lace ne a jikinta, launin ash colour riga da skirt sunbi shape din jikinta, kamar a jikinta aka ɗinka kayan, duk da bata ƙiba kayan sunyi bala’en Yi mata Kyau, Tani da Lami ne sukayi mata Make up, hatta ɗaurin ɗan kwalin kanta sune suka ɗaura mata shi, ziririyar sarƙar wuyanta ta diamond ce, stone din jikinta sai ƙyalli Yake Yi, ta yafa gyale a saman kafadarta, hannunta ruƙe da handbag, fragrance din turaren jikinta mai daɗin shaƙa ahanci.

Hankalinta ba akwance yake ba, tun kafin ta shigo ɗakin tayi mashi sallama bai amsa bata ba, har ta gaji da yin sallamar shiyasa ta yanke shawarar shigowa don ta ga ko bacci yake yi ne
Tun kafin ta ƙaraso gaban gadonshi blue eye balls dinta suka sauka akan screen din Laptop nasa

Ras taji gabanta yai mugun faɗuwa, zuciyarta tamkar zata faso ƙirjinta saboda zafin da take yi mata, zeenatu tana da saukin kai sai dai tana da zuciya idan ta hasala, ranta ya 6aci sosai ganin abunda yake kallo, hoton da ta tsana a duniyar nan duk da batasan hoton menene yake kallo ba, ranta ya bata cewar budurwarsa ce yake kallo.

Idanuwanta sun makance, bakomai suke hango mata ba face dr shureim ɗinta rungume da mace a kirjinsa.

Runtse ido tayi da karfi ta fasa wata irin gigitacciyar ƙara wadda tayi silar firgitar da shi, da sauri Ya miƙe tare da wurga idonshi Kanta, tuni ta saki jakar hannunta ƙasa, Zafafan hawayene suka wanke fuskarta.

Hankalinshi ba ƙaramin tashi yai ba, a hanzarce ya sauko daga saman gadon ya nufeta fuskarshi da alamun ruɗu ya furta”zeenatu! Lafiya? Meya faru?

Girgiza mashi kai tadinga yi tana faɗin”kada ka matso kusa dani yaya shureim, inna lillahi wa’inna ilaihirraji’un” gaba ɗaya ta gama rikitar dashi”zeenatu ki natsu kiyi min bayani meya faru dake? Ko wani abu ne ya tsoratar da ke?

Cikin shessheƙar kuka tace”yaya shureim bazan Iya jurewaba, zuciyata zata Iya bugawa, tun ɗazu mukayi magana dakai akan zamu fita yawo atare, kace min inje in shirya kafin in dawo kaima za ka shiga wanka ka kimtsa, ashe baka yi komai ba, ko wankan ma bakayi ba, ka zauna kana kallon hotonta saboda tafi ni mahimmanci awurinka, ba tun yau ba kullum ne saina ganka kana kallonta, wai wacece wannan ne? Dame tafi ni? Numfashinta na fita da hucin zafi ta ƙarasa maganar, tare da juyawa da gudu ta fuce daga ɗakin nashi.

Hankalin shi ba ƙaramin tashi yai ba, idonshi akan bayanta harta 6ace ma ganin shi.

Dafe kanshi yai da hannu ɗaya, har cikin ranshi baiji daɗin kalamanta ba, baiso yai silar 6ata mata rai ba, duk da bai fahimci inda maganganunta su ka dosa ba, lumshe idanuwanshi ya ɗanyi kafin ya ware su a hankali, yayin da zuciyarshi ke tariyo mashi furucin da tayi mashi, yasan bai kyauta mata ba, ta ƙwalla fa rai akan son su fita tun Jiya shi da kanshi yai mata alƙawarin yau zai ɗauke ta a sabuwar motarshi su fita yawo.

Cikin sanyin murya ya furta”am sorry my zeenat, ” da sauri Ya nufi toilet don yai wanka.

 

*Boss Bature✍️ Mu haɗu Gobe In sha Allah Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin*

 

First bank

 

3196407426,

 

*Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai*

Back to top button