Hausa NovelsKurkukun Kaddara Book 2 Hausa Novel

Kurkukun Kaddara Book 2 Page 16

Sponsored Links

_~*BossLadiesWriters*~_

_*KURKUKUN ƘADDARA*_

~Middle step~

_The Prisoners E16_

 

*Daga alƙalamin Boss Bature*

 

Kusan a tare Aneelerh da zahra su ka shigo palourn, a saman carpet kowan nan su yai zaman cin tuwo Junaid na azaune gefenta, tun da su ka zauna idanuwan su Mami da Abie na akan su, at same time suka haɗa baki wurin gaishe dasu cikin girmamawa, fuskokinsu Uncle abdallah da fara’a suka amsa masu.

Bayan kowan nan su Ya natsu, Hajiya adama ta soma magana cikin nutsastsiyar murya
“Dama jiyane Aneelerh ta ke faɗamin dangane da tada zancen 6acewarsu tajuddeen da za’ayi, a gaskiya naji daɗin jin hakan sosai, Kuma na yabama zahra da ta kawo wannan shawarar ta yi tunani mai kyau” Tun da ta fara magana sun natsu suna sauraronta, Zahra sai faman washe baki take yi jin anyabi shawararta, tana matuƙar son taga An yabeta.

Bayan Hajiya adama ta ƙare magana Uncle abdallah Ya ɗaura da cewa”yanzu haka abun da mu ke tattaunawa akai kenan, Ni kaina Naji daɗin tunanin nan da akayi abune mai kyau da buƙatar atada zancen 6acewar su ya dawo sabo, wata’ƙil ta silar hakan Allah ya agaza mana Muji ɗuriyarsu duk da bamu da tabbacin ko suna araye don ni har yau bana ji araina cewa babu su a doron duniyar nan!”

Numfasawa Abie Yai Kafin ya ɗaura da nashi jawabin”In sha Allahu muna sa ran wannan Karan zamuci nasara, dama dalilin taruwar mu anan don kowa Ya bada tashi shawarar” Bayan Kammala Maganar abie, Uncle ɗan Iya Ya soma magana

“Na riga nayi magana da Ziyad babban ɗan jarida ne, Tun ranar da muka Yi magana da Aneelerh, ta turo min hotunansu already na tura mashi su, da duk wasu bayanai da za’a buƙata, Ya ce min in sha Allah cikin weekend da zamu shiga komai za’a fara yaɗa labarinsu” Murmushine Ya bayyana akan fuskokinsu da alama sun ji daɗin Jin hakan
Uncle abdalla yace”Wai kana Nufin Ziyad ɗan Gidan senate Lateef”?

Jinjina kai Uncle ɗan Iya yayi”ƙwarai kuwa, Ziyad yanzu ae shi ke jan Ragamar Companynsu Na jarida mai suna Obinna News Network (ONT) Yaron Akwai hazaƙa Kullum ne saina bibiyi Labaransu a shafinsu, ƙwararrune a 6angaren Aikin Jarida, duk wani labari da zaiyi trending a social media Sune na farko da zasu fara buga shi a shafinsu”

Uncle abdalla Yace”Allah sarki, Uzair Da tajuddeen Sunci burin yin Aiki a companynsu, suna son Yin aiki tare da Ziyad Allah bai nufa ba” cikin karyayyiyar Murya Uncle abdallah ya ƙarasa maganar, jikin kowan nan su Yai sanyi

“Nima a bakin uzair na ta6a jin labarin Ziyad ɗin nan shahararran ɗan Jarida, ” Acewar Hajiya adama

Uncle ɗan Iya na murmushi yace”Allah sarki, ae muna mutunci da Iyayensu, lokacin da ace nasan suna da burin yin aiki da shi ai dana haɗasu, Yadda Taj da uzair suke da hazaƙa a 6angaren Jarida tabbas da suna atare ba ƙaramin Cigaba za’a samu a ƙasar nan ba, don shima Ziyad ɗin Akwai ƙwalwa Bashi da tsoro gaskiya tsirararta yake faɗin ta” murmushi kowannan su Ya saki.

“Yakamata ka gayyato mana shi agidan nan, tunda kowa nasan ganin shi, Ko da ya ke nasan zaiyi wuya ya iya samun lokacin zuwa sai dai mu muje inda Yake” Abie ne yai maganar

“In dai ziyad ne baku da matsala, mutunne mai sauƙin kai, zan Gayyace zuwa gidan nan”

Tun da suka fara magana sai Yanzu ummi tasa baki”kaga daga nan Idan Yazo sai mu bashi auran zahra….” tunkan ta ƙarasa magana zahra dake chatting da wayarta A sukwane ta ɗago Girarta a haɗe tana kallon fuskar mami.

Hakan da ta yi ba ƙaramin dariya ya basu ba, Uncle ɗan Iya yace”kin kawo shawara mai kyau, Ni kaina nayi tunanin hakan don yaron akwai farin Jinin ƴan mata ita kanta zahra nasan zata ƙyasa” Kifa kai zahra tayi saman cinyoyinta, takaicin Duniya ya isheta, ita da ta ke da burin mallakar Uban gayyar family ɗin su kuma suna yi mata zancen Ziyad.

“Akwai Kyauta ta musamman da zan ba Aneelerh, nasan Itama zata taimaka mana sosai” Hajiya adama ce ta yi maganar idonta Akan uncle abdallah.

“Na baro ta a mota, jiya na manta ban shigo da ita gidan ba, Bari naje na ɗauko” yai maganar yana yunƙurin miƙewa Sai ga Mahboob Kamar an wurgoshi Rai a6ace yake Tafiya Fuskar shi a haɗe babu mutunci.

“Ka koma ka zauna Ga mahboob nan, ka bashi key ɗin motar ya ɗauko maka” Karaf acikin kunnanshi Maganar ta sauka, Har ƙara sauri yake yi don yabar falon
Ɗaga murya Uncle ɗan Iya yai”Kai Mahboob zonan” Cak Ya tsaya da yin tafiyar fuskarshi A murtuke ya Juyo Ya nufi inda suke zazzaune saman sofa.

Zuƙunnawa Yai ƙasa Ya ɗago da fuska Yana kallon Abie ɗin nasu

Rai a6ace yace dashi”Mahboob ba ka ga munyi baƙi bane a gidan namu”?

Hannu yasa ya ɗan sosa ƙeyarshi Muryarshi ƙasa ƙasa Ya furta

“Bana Jin ɗaɗi jiya shiyasa ban samu damar zuwa ganin su ba,”

Wani kallo Da Ummi ke wurga mashi daga inda take zaune saman Sofa kamar zata kifa masa mari, Hakan yasa shi yin sauri kallon Uncle Abdallah Ya furta”sannunku da zuwa, ya gajiyar tafiya, ya kuma aka baro mutanan can”

fuskar uncle abdalla asake ya amsa mashi”lafiyalou Mahboob, ya school ko an kammala” fuskar shi ba yabo ba fallasa ya ce”diploma ce na kammala”

Ganin yanayin fuskarshi babu walwala Uncle abdalla yace “Ko dai har yanzu ba lafiyane? Naga kamar baka acikin natsuwarka”

Sai lokacin Ya ɗan sakin murmushin yaƙe “Bakomai, ai naji sauƙi” Iya abunda ya furta kenan, Baby Junaid ya tsareshi da ido, Dariya ce ƙumshe a cikin bakinshi don ya fahimci damuwar rashin zoban shi ce ta sanya shi shiga wannan halin, Cikin kunne yai ma Aneelerh raɗa”Mommy zoben yake nema, kalli idonshi ki gani sunyi jawur, Allah bani bashi mommy sai ya zubar da hawayensa”

Ƙiris ya rage Aneelerh ta saki dariya yayin da take sauraron muryar junaid, ita kanta ta lura da 6acin ran da ke akan fuskar Mahboob.

“zai baka Key ɗin mota, saƙo zaka ɗauko mashi” Fuska a ɗaure uncle ɗan Iya yai mashi maganar, tare da kallon uncle Abdalla

“Bashi key ɗin motar,” acewar ɗan Iya, ciro key ɗin uncle abdallah yayi kafin ya miƙa ma Mahboob, Ya sanya hannu biyu ya kar6a.

Yunƙurawa yai ya miƙe ya fuce daga ɗakin yana ƙunƙuni.

Kafin dawowar Mahboob Junaid Ya miƙe da sauri Ya nufi ɗakin Mommyn shi don Ya duba zoben da su ka 6oye.

Yana shiga ɗakin Ringing wayar Aneelerh Ya daki dodon kunnan shi, Da sauri ya nufi wayar dake Ajiye saman pillow Ya haye gadon ya janyo ta.
Jikinshi har kerma yake yi wurin yin Picking call ɗin ya kara wayar a kunnanshi.

Da ƙarfi Ya furta”Wanene”? Shiru ba”a tanka masa ba.

Hakan baisa ya fasa yin maganar shi ba

“Mommy bata nan tana a palour suna magana da su Abie, I’m the only one in the room.” still ba’a tanka mashi ba, Surutu Yaci gaba da Yi

“Angel ce ke kira”? Shiru ba amsa”Sister Angel, say something! It’s your brother, Baby Junaid. I miss you so much”

Da shagwa6a ya yi maganar, Sai lokacin Muryar mutumin da ya kira a wayar ta bayyana da sauti mai matuƙar Ratsa zuciya.

“Where is the owner of the phone?” ta6e baki Junaid yai”ai na faɗa maka tana a palour”
“Okey ina son yin magana da ita, ko zaka Iya kai mata wayar” Tuntsirewa Junaid Yai da dariya yana faɗin”a’a Sai dai ka yi magana dani, sai in faɗa mata”
“Pls ka kai mata wayar, ” maƙe kafaɗa Junaid Yai kamar yana agabanshi”ni dai a’a, Ka faɗamin sai in faɗa mata saƙon”

“Shekarunka nawa”? Ga dukkan alamu wanda ya kira wayar ya fahimci ƙaramin yaron ne ya ɗaga tun daga kan voice ɗinsa.

“Huɗu Biyar shidda” Sautin dariyar mutumince ta ratsa kunnan junaid.

“No wonder ashe babban mutun ne kai, zamu iya zama abokai” maƙe kafaɗa junaid yai”to aini yarone kai kuma babba”.
“Okey yanzu faɗamin Ina yayarka Angel”? Kwa6e fuska junaid yai cikin muryar shagwa6a yace”ta 6ace 6era ya cinyeta ita da daddynta da daddyna sun mutu nima mommyna ta faɗa min” sosai mutumin Ya fashe da dariya, jin wautar Junaid

“Ka hana Ni Yin magana da mommynka, gashi kanata cinye min kati”
“Ae nace ka faɗamin saƙon sai In gaya mata” mutumin yace”Okey, ka faɗa mata DADDYN UNAISAH NE ya Kira”!

“To zan faɗa mata Sai anjima” Yana kai ƙarshen magana Yai rejecting call ɗin tunkafin mutumin yai mashi sallama, Pillow Ya janyo ya zuge zip ɗin Ya curo ring box ɗin Yana Kallon zoben
“Na Angel ne wannan, Bazan bashi ba Allah tun da ya cinye min chocolate ɗina” Yana magana yana ta6e la66ansa.

Shigowa Mahboob Yai cikin palourn Hannun shi ruƙe da Kyautar wani abu Mai faɗi an rufe shi da wrap sheet mai Ƙyalƙyali, Karasowa Yai agaban sofas din da Uncle Abdallah Yake zaune Ya sauke gift ɗin kafin ya miƙa mashi key ɗin motar, Kar6a Uncle Abdalla yai”nagode sannu da ƙoƙari” muryarshi ƙasa ƙasa Ya amsa da”yawwa” Juyawa yai da sauri Ya nufi Sashen kitchen ganin Ana na zarya kai abinci a dining.

Tunkafin a buɗe Kyautar kowa Ya ƙagara da son ganinta, musamman zahra ta ƙura idanuwanta kamar na mazuru.
Ummi na murmushi tace”masha Allah wannan kyauta tunkafin abuɗe mun fara zumuɗin ganinta” Mami tace”ni kaina a ƙagare nake Allah”
A hankali Uncle Abdallah Yake warware wrapping sheet ɗin, slowly Kyawawan idanuwanta dara dara suka Fara Bayyana, da mamaki su ke Kallon juna cikin rashin fahimtar wacece wannan Kyakkyawar Matashiyar.

Lokacin da ya warwaro wrapping sheet ɗin dai dai Saitin hancinta ya ƙarasa 6an6are ledar gaba ɗayanta, adai dai time ɗin Mahboob da Ana sun fito daga kitchen Hannun shi ruƙe da glass Na lemu Karaf Idanuwanshi suka sauka akan Hoton zanan fuskar Angel, Nan take ya saki glass ɗin hannunshi gaba ɗaya ya tarwatse ruwan lemun dake acikinsa ya tsiyaye saman tiles.

Tsabar Al’ajabi da mamakine Yasa Aneelerh da mami Yunƙurawa a sukwane suka miƙe tsaye Suna ƙare ma Zanan Kallo Yasha fenti kamar horonta aka ɗauka.

Gaba ɗaya sun Rasa bakin magana, zanan yayi bala’en Yin kyau, fuskar Angel ta fito raɗau Kyakkyawar matashiyar balarabiya bugu da ƙari buzuwa a 6angaren Mahaifinta” Zahra Ko sai faman Yarfa hannu take yi tana ambaton Wow wow Tabarakallahu ahsanul khalikin! Gaskiya koma wanene portrait artist ɗin da ya zana hoton nan ba ƙaramin ƙwararre bane ya baje basira”

Ummi tace”Masha Allah, Yarinyar ba ƙaramar kyakkyawa bace, kamar tajuddeen Ya yi kakinta, Kamanninta sak Kalar nashi, Hasken fatarne ta ɗauko Na mahaifiyarta benazir”

Lamarin ya ɗaurewa Ana kai Ganin yadda Mahboob Ya fasa glass cup ko ajikin shi, Hankalin sam baya atare dashi, Zanan Fuskar Angel Ya tafi da Imaninsa, dama can tun fil azal Mahboob Mayen mata ne.

“Mahboob Meke damunka ne? Baka ga 6arnar da ka yi ba ne’?

Ba tare da ya kalli fuskar Ana ba Ya furta”dama akwai matan Hurul aini A duniya”?

Girgiza kai Ana ta yi Fuskarta ɗauke da murmushi ta nufi dinning, don ta jera kayan tray din hannunta.

Farin Ciki Ya hana Aneeleeh furta kalma, agaban zanan da ke a jingine jikin hannun sofa, ta zuƙunna saman gwiwowinta, yatsun hannayenta na kerma ta ɗaura su saman fuskar Angel, Lokaci ɗaya ta fashe da matsanancin kuka ta kifa kanta saman zanan

“Haba Aneelerh menene abun kuka? Ke da za ki yi farin Ciki”? Mami ce tayi maganar

Hajiya adama ta miƙe ta nufi Aneelerh ta ɗan ranƙwafa ta ɗaura hannunta saman kafaɗarta.

“Share hawayen ki Aneelerh, banaso pls, Ni ban Kawo maki zanan nan don ki yi kuka ba, saboda farin Cikin ki yasa Nasa aka yi min shi, nasan zaki ji daɗi sosai” Abie yace”in dai ko bazaki daina kukan nan ba, zansa su koma da zanan” sai lokacin ta ɗago da rinannun idanuwanta da suka kaɗa jawur ta kalli fuskokinsu cikin shessheƙar kuka tace”Nadaina, wlh kukan farin cikine Ya kubce min, Inason Angel sosai, na kasa jurewa ne, da na ga zanan nan sai naji na ƙara ƙagara da son ganinta a shekarunta Na yanzu” Mayar da idanuwanta ta yi a kan hoton

“Allah sarki my Angel, ɗiyata ƙanwata kuma ƙawata abokiyar firana, Na yi missing ɗinki sosai bazan ta6a mantawa dake ba har abada” Kifa kanta tayi saman hoton Hawaye suka cigaba da wanke fuskarta, ta yi matuƙar karya masu zuciya.

*Middle step A gidan Alhaji ubaid*

Tun lokacin da Dr. shureim Ya kammala kimtsawa ya zauna gefen gadon shi ya natsu yana kallon hotunan abar ƙaunarsa, Ƙarfe Goma sha Biyu Na bugawa, Kiran Alhaji musa Ya shigo wayarsa.

Da sauri Yai picking call ɗin Ya kara a kunnanshi

“Shureim Ina Jiran ka a palour!”

Abun da Ya furta mashi kenan, Ajiyar zuciya ya sauke Tare da miƙewa Ya fito daga Bedroom ɗinsa, Yana mai jin kewar ɗakin nashi, tafiya yake yi tamkar bayason Taka ƙasa, Ji yake kamar In yabar gidan zai ƙara nisanta kanshi da ita ne, duk irin yadda yake zumuɗin barin gidan hakan bai hana wani sashe na zuciyarshi ƙin amince masa ba, Saboda acikin gidan ne, abar ƙaunarsa ta kafa tarihi acikin zuciyarshi.

Lokacin da ya ƙaraso palourn, A zaune ya samu Alhaji musa da Uncle ubaid, Sai Mahaifiyarshi laila Da Mai aikin gidansu zainab, Hannunta ruƙe da shopping bag.

Yanayin fuskokin su Ya nuna alamun rashin jin daɗin tafiyar shi, musamman mai aikin gidansu zainab da kuma Mahaifiyarshi Layla, tana a tsaye ta ruƙe qugu fuskarta babu annuri ko misƙala zarratin zallar 6acin raine.

Shi ko Alhaji ubaid sai faman sakin fara’a ya ke yi babu alamun zaiyi kewar ɗan nashi idan ya tafi.

Idanuwan dr. Shureim akan na mahaifiyarsa, da sauri ya nufi inda take atsaye, hannu biyu ta sanya ta rungumo shi a ƙirjinta, hakan da tayi mashine yasa shi jin hawaye sun cicciko idanuwanshi.

Bubbuga bayanshi take yi a hankali tana faɗin”Shureim ɗina, zanyi missing ɗinka sosai, naji takaicin tafiyar nan duk da ba wani wuri zakaje me nisa ba, sai dai sam hankalina bai kwanta da tafiyarka ba, Naci burin In gatantaka In baka kulawa ta musamman tuntuni, sai dai rashin zamanka agida da kuma gudunmu da ka ke yi, shi yasa ban samu damar yin hakan ba, Yanzu kuma na samu na shawo kanka, an nuna anfini iko da kai za’a rabani da kai,’ tun da ta fara magana Alhaji musa Ya haɗe rai fuskarshi a tamke ba annuri, don yasan dashi take magana.

“Mommy ki samin albarka ita nake buƙata daga gare ki, Sannan ki kwantar da hankalinki, Ni musulmine kuma nayi imani da Allah dashi na dogara, aduk inda zan kasance Allah yana atare dani, ballanta kuma agidan Uncle ɗina ne ba nisa zanyi ba, nasan za ku dinga zuwa akai akai kuna ganina, Nima kuma zan dinga zuwa gida” Maganar Dr. shureim ta yi matuƙar karya mata zuciya, Allah na gani tana son ɗanta sosai, Muryar Alhaji musa ce ta katse su”shureim bamu da isashen lokaci, ka wuce mu tafi”

Ɗagowa Yai daga jikin mahaifiyarshi ido cikin ido suke kallon Juna, Canza harshe ta yi zuwa larabci kafin taci gaba da magana

“Shurem hankalina bai kwanta da kawunka ba, Ni ban yarda dashi ba, Bai ta6a nuna damuwa akanka ba, tun lokacin da ƙaddarar nan ta risƙe ka har ka fara shaye shaye a ƙarshe ma kabar ƙasar gaba ɗaya, musa bai ta6a bibiyar rayuwarka ba, babu ruwanshi dakai Ƴa’ƴanshi kaɗai Ya sani, Ta ya ya hankalina zai kwanta da zuwan ka gidan shi? Allah kaɗai yasan mugun nufin shi akan ka” Tana magana tana shafa sumar kanshi da ta sauko saman wuyanshi, babu wanda Yasan me ta ke cewa, dama da biyu ta yi mashi maganar da larabci don saboda tasan basa Jin Yaren, mai aikinsu kaɗaice ta ke ji saboda itama balarabiyace, jikin zainab duk yai sanyi da jin maganar Hajiya layla, baiwar Allah duk ta damu da Shureim gani ta ke yi kamar idan ya tafi wani abu zai faru dashi.

Muryarshi araunace Ya soma magana da harshen larabci”Mommy kidaina wannan tunanin dan Allah bana so, ki kwantar da hankalin ki, Uncle musa bazai Ta6a cutar dani ba, duk da bai damu dani ba a lokacin baya, yanzu ya nuna yana ƙaunata zai Iya yiwuwa ko dan saboda tausayin halin da nake aciki ne, Nafi so ki yi mashi kyakkyawan zato mommy”

Gyaɗa kai ta yi “Shikenan shureim zan cigaba da yi maka addu’a akan Allah ya kare mun kai ya tsaremun kai daga sharrin duk wani abun cutarwa” Cikin harshen labaraci ta dinga jero addu’o’i tana tottafa masa Yana amsawa da ameen.

Bayan ta kammala ya ɗago da ido Ya kalli zainab, idanuwanta sun cicciko tab da kwalla.

Matsawa ya yi kusa da ita, fuskarshi ɗauke da murmushi yace”auntyna zan tafi asanyamin albarka” yai maganar tare da duƙar da kanshi, Hakan ba ƙaramin daɗi yayi mata ba, Ƴan hawayen da ta ke matsewa tuni sun soma shararowa saman kuncinta.

Tafin hannunta ta ɗaura saman arab turban ɗin dake naɗe akanshi, a tsanake take jero addu’o’i tana tottofa masa a ƙarshe ta ƙara da cewa”Allah yasa Silar komawarka can ka samu farin Ciki na har abada” Ya amsa mata da ameen ameen”Allah ya saukeku lafiya shureim” ya ƙara amsa mata da ameen

Daga Haka Ya juya ya nufi Mahaifinshi Alhaji Ubaid.

Fuskarshi ɗauke da murmushi yake duban shureim”daddyna, asanya min albarka”

Da buɗar bakin Alhaji ubaid sai cewa yai “Shureim sai ka ce zaka Bar ƙasar, irin wannan bankwana haka! Na lura Jikinka duk Yai sanyi, Ko kamanta Abuja ne zaka je gidan ƙanina”? Harara Hajiya layla ta jefa ma Alhaji ubaid a fakaice.

“Lokacin da ka ke ƴan guje gujenka ba tare da sanin kowa ba, Ka ke barin ƙasar nan sai yau don zaka tafi gidan uncle ɗinka kake Neman albarkarmu”?

Da mamaki akan fuskar Dr Shureim ya ke kallon Alhaji ubaid, Ran Hajiya layla ya 6aci A harzuƙe tace”Dan Allah Ya isa haka! Me yakawo wannan maganar? Saboda kawai yace ka sanya mashi albarka? Idan baza ka sanya mashi ba sai ka ƙyale shi Ya tafi, dama albarkar uwa aka fi buƙata, bata uba ba”

Runtse ido shureim Yai, Maganar daddynsa ta ta6a mashi zuciyarshi tuni ƙwalla sun Ciko idonshi, Hatta zainab ta ji ɗacin maganar Alhaji ubaid ji take kamar ta kikkifa mashi maruka a kuncinsa.

Still da murmushi akan fuskar Alhaji ubaid ya ke dubanta, kafin ya maida dubanshi ga shureim.

“Ka ji abunda Mommynka tace, babu buƙatar albarka ta, Don haka zaka Iya tafiya” cikin jin ƙunar rai Yace”daddy na roƙe ka, Ka sanya min albarka ina buƙatar taka”! hawaye tuni sun wanke fuskarshi, Jinjina kai Alhaji Ubaid Yai, Kafin Ya janyo Dr shureim Ya rungume shi, Yana tofa mashi albarka, Hankalin shi ba ƙaramin kwanciya ya yi ba.

Miƙewa Alhaji musa yai daga saman sofa ɗin da ya ke azaune, ko kallo basu ishe shi ba, Cikin takun nan nashi na izza, ya juya ya fuce daga falon don shi arayuwarshi Ya tsani 6ata lokaci.

Tsoki Hajiya layla taja aranta tace”abanza, Uban Ji da kai, ai ni da za ka burgeni, ka kama Hanya ka yi tafiyarka, kabarmin ɗana”

Ruƙo Hannun dr shureim Alhaji ubaid Yai, Yaja shi suka nufi Hanyar fita falon, Da sauri Zainab Tabi su Hajiya layla kam zama tayi dirshan saman sofa tana faman cije le6e.

Abakin Engry hall na gidan, Zungureriyar motar da zata ɗauki Alhaji musa zuwa airport tayi parking, Hamshaƙiyar gaske Ƴar ubansu mota mai numfashi.

Yana daga kishingiɗe a ɗaya daga cikin back seat na motar, tamkar yana acikin bedroon ɗinsa saboda tsabar haɗuwarta, slowly murfin motar ke zugewa Dr shureim na ƙoƙarin shiga ciki, Muryar Zainab ta katse masa hanzarinsa.

“Namanta da wannan, kai na haɗamawa” juyowa yai tare da kallonta, Ledar hannunta ta miƙa masa, fuskar shi ɗauke da murmushi ya kar6a Yana yi mata godiya, kafin daga bisani yayi masu sallama, yasa kai cikin motar, daddaɗan Sanyin a.c ya ra6i sassan jikinsa shi kanshi Ya yi al’ajabin haɗuwar motar.

Mutun Biyune agaban motar, Driver ɗinsa da kuma p.a ɗinsa wani gabjejen mutun mai ƙirar Ƙarfi daga gani yana gym saboda ko’ina na jikinsa a murɗe Yake, wankan suit ne a jikinsa Baƙi wulik baida fara’a a fuska.

Kaitsaye Airport Suka nufa, already An shirya mashi privet jet dinsa, Bayan shigarsu cikin jirgin wanda Tsayawa zayyana Haɗuwarshi 6ata lokaci ne, abune da hankali bazai ɗauka ba, saboda an kashe dukiya kamar ba asan zafin nemanta ba, Kai kace saman bishiya ake tsinko kuɗin ana amfani da su. ()

Dr. shureim Yaga aljannar duniya, Bayan tashin jirgin Cikin mintuna da basu wuci arba’in ba Suka ƙaraso Airport ɗin Abuja, Tun kafin jet ɗinsa ya ƙaraso airport ɗin tuni Escords ɗinsa sun hallara abakin motocin su cikin shiga ta baƙaƙen suits domin tarbarsu da kuma basu tsaro.

*EX-PRISONERS❤*

Tun Bayan da suka kammala Cin abinci kowan nan su yai kulu wash rabu hani’an, Nurse ta shigo ɗakin ta kwashe kayan abincin da suka ci ta fuce da su waje.

Gaba ɗayansu suna A saman gadon zazzaune Sai Yanzu su ka samu damar ƙarewa ɗakin kallo.

“Angel menene wancan”? Parveen ce ta yi maganar tana nuna mata plasma tv dake manne a jikin bango.

“Tv ce da ita ake yin kallo”
“To ki kunna mana mu gani mu ma” girgiza kai Angel ta yi”a’a Parveen ku bari sai munje gidan daddyna tukunna”

ta faɗi hakanne don tasan muddin ta kunna masu kallo zasu birkice mata ne, a ƙarshe ay abun kunya, tun da basu ta6a gani ba.

Tambayoyi suka dinga jera mata kamar ƴan jarida, komai na ɗakin sai sun tambayeta menene shi ya akeyin amfani da shi, ita kanta ba komai ta sani ba saboda ba kalar ɗakinsu na gida bane, Iya abunda ta sani take amsa masu.

“Zan shigo toilet” Batul ce ta yi maganar, saukowa ta yi daga saman gadon ta nufi ƙofar da take tunanin ta toilet ce ta tura da hannu ta shiga, tun da ta shiga take bin ko’ina da kallo sauƙin ma toilet ɗin su na prison na zamani ne, da ko anga ƙauyanci sai dai da banbanci sosai, don wannan akwai sink da bathtub hada shower ga mirror da sauran Kayan amfani.

Agaban madubi Batul ta tsaya tana kallon fuskarta, bata ta6a ganin Kyanta irin na yau ba yatsun hannunta ta tura cikin Curly hair ɗinta tana cakuɗa shi.

Acan bedroom ɗin Bayan shigarta toilet, zuciya da saƙe saƙe Angel sai ta dinga ayyanawa aranta ga Batul can ta kunna Ruwan zafi amaimakon na sanyi” Jiki Na rawa ta sauko daga saman gadon ta nufi toilet ɗin, ko neman excuse babu ta shigo toilet din kamar an jeho ta.

Jin motsin shigowar mutun yasa Batul Juyowa a firgice don ganin wanene. Kusan atare suka sauke Ajiyar zuciya

“Dama ba wani abu za ki yi a toilet ɗin ba”?
Murmushi Batul ta sakar mata”Inaso ne in ƙare ma ko’ina kallo,”

“In dai wannan ne kada ki damu zan yi maku bayanin komai, amma Yanzu ki fito mu koma ɗaki” Amsa mata ta yi da toh ta juya ta nufi Angel ta ruƙo hannunta suka fito, shugowarsu ɗakin ke da Wuya Aka buɗe ƙofar, Dr Daniel brown ne tare da Nurse rebecca.

Fuskokinsu ɗauke da murmushi, cikin harshen turanci ya soma yi mata magana.

‘Masoyiya Angel da ƴa’ƴanta, fatan na same ku Lafiya” Amsa mashi sukayi da lafiyalou
“Ya jikin naku? Ko akwai inda ke yi maku ciwo “? Atare suka girgiza mashi kai

“Okey, Starting tomorrow, you’ll be receiving injections for three days, and you’ll also be taking regular medication to improve your health.” cikin kulawa dr brown ke yi masu magana idonshi akan fuskar Angel.

Murmushi ta sakar mashi”mun gode sosai da kulawarku agare mu, Allah ne kaɗai zai Iya biyanku”

“Kada ki damu, aikin mu ne, Ko akwai wani abu da kuke buƙata”?

Cikin raɗa Batul ta yi ma Angel magana a kunne”muna son ganin Haris da Danish”

“Doctor, can we see our brothers?” kamar mai jin shakkar shi ta yi maganar.

Jinjina mata kai Yai alamar eh, Kafin ya ɗaura idonsa akan Nurse rebecca” Ki kai su ɗakin Ƴan uwansu”
“Okey sir” Mayar da idonshi yai kan Angel” pls muna so ki samu natsuwa sosai, ki kwantar da hankalinki dana ƴan uwanki, akwai magana da zamuyi dake tare da sojojin da suke ceci Rayuwarku, sunce da zarar kin farka a sanar da su, Ni kuma na bari sai zuwa gobe idan kin ƙara wartsake wa duk da naga jikin naki da ƙwari”

shiru Angel ta yi tana faman zazzare mashi gray eyes ɗinta aranta ta ayyana komai suke son sani? fatanta Allah ya bata ikon amsa masu tambayoyin da zasu Yi mata

“Haɗin kanki mu ke buƙata Masoyiya Angel” murmushin yaƙe ta sakar mashi wanda bai kai zuci ba.

Bayan fitar shi daga ɗakin, Nurse ta kalli faces ɗinsu”zamu Iya tafiya” A hanzarce suka sassauko daga saman gadon suka bi bayanta, tun da suka fito daga ɗakin gabansu ke faɗuwa ganin haɗaɗɗen wurin da suka tsinci kansu a cikinsa, Asibitin Har ya gaji da haɗuwa, babu tazara a tsakanin ɗakunansu da inda aka kwantar da su Haris duk acikin amenity ward ne.

Abakin ƙofar ɗakin da aka kwantar da Haris suka tsaya, sai da nurse ɗin ta fara tura ƙofar ta shiga tukunna Ɗaya bayan ɗaya su ka soma shiga cikin ɗakin cike da zumuɗin son ganin ɗan uwansu, tun kan su ƙarasa suka hango Haris kwance magashiyan saman medical bed an sanya mashi robar oxygen a hancin sa.

Da sauri suka ƙarasa gaban gadonshi, gida biyu suka raba kansu, gefen dama Gabriel ne da Javed sai Naufal da Parveen ta 6angaren hagu Angel ce da Batul, Jamimah da azeeza sai Hannah, tsananin tausayin Haris ne Ya kamasu, tuni idanuwansu sun cicciko tab da ƙwalla.

Cikin shessheƙar kuka Angel ta ambaci sunansa”Haris!” har cikin dodon kunnanshi Kiran Ya isar mashi, sambatu ya soma yi masu Yana ambaton sunan Deeja yana faɗin”mu koma ku ɗauko ta, Deeja na tana araye suna can suna azabtar min da ita, dan Allah ku taimakamin ku cece rayuwata ku ɗauko min deeja na” tuni Hawaye sun wanke fuskokinsu, Hatta nurse rebecce Dake atsaye jikinta yai sanyi ganin hawayen su, Duk da bata iya jin abunda ɗan uwan nasu ke cewa

“Haris”! Muryar Angel ce ta ƙara ratsa kunnan su, A hankali Ya soma ƙoƙarin buɗe idanuwansa da suka kumbura jawur ya ɗaura su akan fuskarta, Ware su yai sosai, Ganin Yana ƙoƙarin miƙewa yasa Nurse ɗin Yin saurin matsawa bakin gadon ta rankwafa ta zame mashi roban oxygen din daga hancinsa, ta taimaka mashi Ya miƙe zaune Bayan ta sanya mashi pillow a tsakankanin bayan shi da headboard na gadon.

Sun natsu suna kallon shi, azabar ciwo tasa shi canza kamanni, fatarshi ta yi haske Ya rame sosai, hakan ba ƙaramin Kyau ya fiddo mashi ba, sumar kan shi a cukurkuɗe kamar mahaukaci sabon kamu, ɗaya bayan ɗaya ya ke binsu da kallo Yana ambaton sunansu da raunatacciyar muryarsa
“Angel, Batul, Azeeza, Jamimah, Hannah, Javed, Naufal, Gabriel..” Numfashi Yaja Kafin ya furta sunan Deeja”Ya akai banganta ba? Ina aka kaimin deejana? Baku zo da ita ba”? Idanuwanshi acike tab da hawaye yai masu maganar

Cikin sanyin murya Angel tace”Haris pls ka daina sanya damuwa aranka, dubi kaga yadda ka rame, tamkar ba Haris ɗin mu ba, duk kabi ka zauce, Why pls? Bama Jin daɗin canzawar da ka yi, gashi baka da ƙoshin lafiya”

daƙyar sautin muryarshi ke fita”Bazan Iya jurewa bane Angel, inason deejana ina jin tsoron ace narasa ta, donni inaji araina tana araye tun da har su azeeza basu mutu ba, Itama sumane tayi”

“Haris idan har baka kwantar da hankalin ba, Ta ya ya zamu Iya samun ƙwarin gwiwar fallasa asirin masu kurkukun ƙaddarar har muci nasarar ɗauko sauran ƴan uwanmu da suke acan idan basu mutu ba? Dole fa sai ka bamu haɗin kai ka danne damuwar dake aranka tukunna zamu Iya Cin galaba akan su”! Angel ce ke yi mashi magana cikin kwantar da murya

Gabriel ya ɗaura da cewa”Kin faɗi gaskiya Angel, Haris pls ka taimaka ma kanka muma kuma ka taimake mu sannan ka taimaki rayuwar su Deeja Rashin lafiyarka shi zai tarwatsa mana shirin mu, Nurse ta faɗamin abunda ke damun ka, Ciwon zuciyane Haris kuma nasan bakomai ne ya jawo hakan ba face Deeja!! kaga yanzu mun ku6uta daga Daji muna acikin mutanan duniya, Nan inda muke asibiti ne Inda ake duba marasa Lafiya sune suka bincika lafiyarka kuma suka tabbatar mana da cewa damuwace ta silar wani abu daka ƙwallafa rai akan son shi, pls Haris Ka taimaka mana! Idan har ba ka ji sauƙi ba Likitocin nan bazasu ta6a bari mu koma Nigeria ba gidan daddyn Angel” tunda Gabriel Ya fara magana Haris Yake bin ɗakin da suke da kallo, sai lokacin Ya gane ba adaji suke ba, shifa gaba ɗaya baya acikin hayyacinsa baisan ma a ina yake ba, idanuwanshi sun makance.

Azeeza sarkin tausayi tun da ta tsareshi da ido, Hawaye ke bin fuskarta.
Cikin shessheƙar kuka tace”Dan Allah haris ka yi haƙuri, In sha Allah deejan mu bata mutu ba da sauran ƴan uwanmu Zamuje mu ɗauko su”

Batul tace”kwanciyar hankalinka kawai muke buƙata Haris, idan ba haka ba kaga zaka mutune kafin muyi nasarar dawo da su deeja, me kake tsammani idan Ka mutu muka gano deeja araye ya za ta ji? Ka mutu saboda ita? Kaima ka sani yadda take ƙaunarka itama mutuwa zatayi tabi ka”

lumshe idanuwanshi yai, ƴan uwanshi ba ƙaramin sanyaya mashi zuciya suke yi ba, sai kwantar mashi da hankali suke yi duk don su samu ya wartsake

“Ina ɗan uwana”? yai tambayar yana kallom faces dinsu
“Danish bai farka ba Haris Har yanzu, bacci yake yi, ” Angel ce ta bashi amsa, damuwace ƙarara akan fuskarshi
“Angel wani irin bacci ne wannan Har yanzu bai farka ba? Ina jin tsoro wani abu yasame shi” girgiza kai Angel tayi”a’a Hairs ba abunda zai same shi, Ni inaji araina Lafiyar danish qalou, Bacci ne kawai ya ke yi kasan ya ɗauki tsawon lokaci bai runtsa ba shiyasa bai farka ba”

Gyaɗa kai yai”Allah yasa hakane,”
. “Haris ka ci abinci ko kana jin yunwa”? Kallon parveen yai”bana Jin yunwa parveen, Naji daɗin kulawarku agare ni, sannan Ina tayamu murnar barin kurkukun ƙaddara” murmushi kowan nan su Ya saki, shima ya ƙalalo murmushi akan fuskarshi

Muryar Jemimah da shagwa6a tace”Idan ka ji sauƙi, zamu ga deeja ma har kuci abinci atare da ita, kana bata abaki itama tana baka abaki, agidan daddyn genie ɗita” gaba ɗayansu suka sanya dariya, Nurse rebecca dake tsaye tuni ta zauna saman chair tana dubansu sam bata gajiya da kallon Yaran burgeta suke Yi kamar ta sace su take ji.

Haris Ya ji daɗin maganar Jemimah har saida yaɗan murmusa
“Sannan Haris zai dinga wanke ma deeja gashin kanta yana sharce mata shi,” Batul ce tayi maganar, tsabar daɗin maganarta har saida fararen haƙoransa suka bayyana.

“Bayan haka zai dinga goyata a saman bayanshi Suna yawo” acewar Hannah sosai Haris ya fashe da dariya yayin da hawaye ke cigaba da yin sintiri akan fuskarsa, Lamarin ya ɗaurewa rebecca kai, mamakinta yadda yaran suke matuƙar ƙaunar junansu, wani abu da ya ƙara burgeta yadda suke ta sanya shi dariya tabbas su ka ɗai suke Iya sarrafa junansu.

“In sha Allah Haris our dream will come true” lumshe idanuwanshi yai tare da buɗe su akan fuskokinsu sai ya dinga ganin tamkar Deejar sa ce zaune a tsakiyar gadon tana sakar mashi murmushi, hakan yasashi sakin murmushi kamar wani zautacce

“Haris ka kwanta ka huta, kada mu cika ka da surutu, zamuje ɗakin Danish mu duba shi”

“Nima inaso naganshi Angel, muje atare”

Kallon Nurse ɗin tayi”pls sister zamu Iya tafiya da shi ɗakin ɗan uwanmu”?
Smilling gently, nurse rebecca tace”badamuwa, zamu Iya tafiya da shi” ta yi maganar tare da miƙewa Ta nufi gaban gadon, da taimakonta Haris ya sauko daga saman gadon tace mashi ya dafa shoulder ɗinta don ya samu damar yin tafiya, Rurruƙeta yai da hannayenshi a haka suke Yin tafiyar, Su Angel suna abayansu har suka ƙaraso ɗakin da aka kwantar da garkuwa, Jikin Angel har 6ari yake yi saboda tsabar zumuɗi, tun kafin su ƙarasa shiga ɗakin suka hango Danish Baje saman gadon, kamar matacce, lallausar sumar kanshi ta tarwatse saman mattress ɗin gadon, da sauri Angel ta nufi gadon Ta haye daga gefe Idonta akan Kyakkyawar fuskarshi, Har kullum kamar ana ƙara ninka mashi kyawunshi, fatarshi tayi smooth fara sol Ko tabo babu, Sun canza mashi uniform ɗinshi wanda ke a jikin sa Yanzu kalar nasu ne Riga da wando light blue, rigar tayi tighting ɗinsa, gajeran hannu ne da ita Hakan ya bayyana ƙaƙƙarfan Damtsen hannun shi, Likitoci sun sha wahala wurin canza mashi kayan Jikinshi saida suka haɗa ƙarfi tukunna su ka samu damar raba shi da su.

A hankali take bin Shi da kallon so da ƙauna tun daga saman sumar kanshi har i zuwa kan Long eye lashes ɗinsa, dogon hancin nan nashi yayi sam6al babu lanƙwasa, full lips ɗinsa sun ciza launinsu, slowly ta sauke idonta akan Zanan tattoo dake a gefen dogon wuyanshi Yayi bala’in yi mashi kyau
A gefe da gefen gadonshi kowannansu Ya samu wuri ya zauna hada haris da nurse ta zaunar dashi, natsuwa su ka yi a yayin da su ke kallon ɗan uwansu, daɗi kamar zai kashe su
Angel ta shagala da kallonsa ji ta ke kamar ta faɗa saman chest ɗinsa ta ƙanƙame shi ko ta samu sassaucin kewarsa da ta ke yi, Muryar Haris ce ta fargar da ita.

“Angel zuciyarshi tana bugawa”?

A hanzarce ta kwantar da kunnanta saman chest ɗinsa saitin heart ɗinsa nan take taji bugun zuciyarshi na harbawa a tsanake
Ɗagowa tayi fuskarta ɗauke da murmushi tace dasu”zuciyarshi tana bugawa, bacci ne yake yi”

Jin haka yasa Kowan nan su Ya matsa kusa da shi, ɗaya bayan ɗaya suke ɗaura kunnuwansu saitin zuciyarshi, nurse rebecca dake a tsaye murmushine ɗauke akan fuskarta

hankalinsu ba ƙaramin kwanciya yai ba, jin zuciyarshi na bugawa

“Sai yaushe zai farka? Baccin yayi yawa” Javed ne yai maganar, Naufal yace”may be saiya ɗauki adadin kwanakin da yayi bai runtsa ba tukunna zai farka” zaro ido Angel tayi haɗi da girgiza kanta”in sha Allah ba zai kai wannan lokacin ba zai farka.

Ta ƙare maganar tare da ruƙo zira ziran yatsun hannun Danish na dama acikin nata, sosai ta runtse su (nima kuma na runtse alƙalamina)

*Boss Bature✍️ Mu haɗu gobe Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin*

 

First bank

 

3196407426,

 

*Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai*

Back to top button