Auren Gado Hausa NovelHausa Novels

Auren Gado 3-4

Sponsored Links

3⃣&4⃣

………….. D’an karamin gidane mai zaure a cikin tsohuwar unguwar ta jakara, almajirai ne birjik a zauren da Alama malami ne a gidan mai Y’ar Karamar tsangayar Almajirai, ko tsakar gidan ma akwai wasu dakuna dake dauke da Almajirai, rayuwar gidan sun dauki Almajiran kamar Yaran gida ba kyama ba wulakanci, matar gidan inna kulu mace mai hakuri, tanada ya’ya mata guda hudu manya biyu sunyi Aure sai Naziya da kanwar ta Shukrah, Yanzu Naziya nada shekara goma shatakwas sai shukrah mai shabiyar, ta kammala secondary dinta Bana a makarantar gwamnati, a tsugune take tana wanke kwanonin da suka bata Y’ar Karamar wayarta ce a kunne a gefen ta tana sauraron karatun Al’qur’ani mai girma tana bi a hankali cikin kwarewa,
Kare mata kallo nayi domin yarinyar batayi Kama da kalar talaka ba domin dai dai da duddugen kafarta farare ne tas kyakkywa ce sosai kamar wata Y’ar larabawa tana sanye da guntun hijabi akan al adar ta da kuma koyarwar inna kulu domin gidan su akwai mazajen Almajirai akoda yaushe, fitowa dattijuwar tsohuwar tayi tareda cewa “inkin kammala ki dora mana Abincin rana Naziya, shukrah ta kai mana markade tunda duk babu Almijirai yau, “toh Inna. Tafada tana wanke wurin data bata, she is really cool and beautiful ga tarbiya dake tattare da ita jikinta ba rama kuma bakiba duk da tana cikin hijabin ta nagano hakan jikinta D’an dai dai bazaka taba yimata kallon talauci ba duk da Abinci baifi karfin tukunyar suba, mahaifin su yana koyarwa yana sana’oin shi wanda yake daukar gidanshi da kuma hidimomin iyalin shi,
Haduwar ta da Ahmed wata rana ce tadawo makaranta a gajiye shikuma yazo unguwar su gidan wani yaron shi dabaida lafiya, tafiya takeyi cikin gajiya a kuma natse ta gefen titi, y’anda ya kwaso motar tashi yasa ya watsa mata ruwan datti kasancewar gari ne na damuna ga kuma yanayin unguwar da yatara guraben ruwa ta ko Ina, saurin jatayi ta tsaya domin gaba daya uniform d’inta ya baci Har fuskar ta ma ruwan ya fallatso mata, saurin fakawa yayi ya fito da sauri yana so yabata hakuri,
Dago kyawawan idanun ta tayi tareda goge fuskar ta da gefen hijabin ta inda jan ruwan bai bata ba, ta kuma kallon y’anda ya saki baki yana kare mata kallo batareda ya iya cewa komai ba, yarinyar ta gama tafiya dashi, juyawa tayi ganin baida niyyar cewa komai tayi gaba, saurin shan gaban ta yayi “Am sorry please ki tsaya muyi magana, ya zaki wuce batareda kince komai ba bayan nayi miki laifi?
Saurin Tsayawa tayi tareda dago idanun ta masu narkar da zuciya tace “nice zanbaka hakuri domin hanyar bata Y’ar talaka bace Nazo kuma na tsaya, sannan don Allah ka matsa in wuce kafin ayi wani tunani akaina a cikin unguwa ba mutuncin gidan mu bane tsayuwa da bako a kan titi. Tafada tana rabewa tayi gaba.
“Wow wow wow what a magic voice, yafada yana binta a hankali tana sauri har ta fada gidan su da gudu domin tana jin takun shi a bayan ta a mugun tsorace take dashi domin yayi Kama da Aljani a wurinta domin he is very handsome kana ganin shi kaga D’an hutu,.

Gefen Ahmed tunda yasa Naziya a ido yakasa sukuni saida yabi ta gefen yaron shi yaji komai akanta, tuni yagano Y’ar babban gidace wato gidan dattijan kwarai, baiyi kasa a guiwa ba ya dawo yasamu mahaifinta tareda neman izinin neman ta, Malam garba yaso ya hana domin ganin D’an gidan wani ne Bayason ya saka Y’ar shi cikin matsala, ya nuna mai mahaifin shi ya rasu kuma shike rikeda kanshi ba wata matsala, bai Amince ba saida ya turo kawun shi yazo suka tattauna ya Amince yabada izinin neman ta,.

Allah yagani bawai Ahmed baiyi mata bane, ita batada burin shiga gidan da yafi karfin ta wanda bata ma riga taga dukiyar ba tukun kawai shitake gani kudin su na bata tsoro, ganin irin k’a’i dar mahaifin ta, baya ko sake mata kudi infact tuni ya daina zuwa da shigar da zata hanata sakewa dashi domin ya lura da yanayin ta dana gidan su tsab, yasamu kanta ta hanyar nuna mata akarkashin wani yake shima yana hustling ne,. Shiyasa yasamu kanta har ta Amince suka Gina soyayya mai karfi a tsakanin su she really loves him domin he is very simple baida fushi baida girman kai saurayi ne mai natsuwa wanda ko yatsanta bai taba kokarin kamawa ba soyayya yake mata mai tsafta, har kawo yanzu da Al amarin yakai ga zancen Aure, zaman ta dashi tagano Abu biyu sune masu matukar muhimmanci a rayuwar shi, mommy and khaleel wanda basa hira sutashi bai kira sunan shi ba tagano irin tsantsar soyayyar da yakewa kanin nashi ta hanyar bata labarin shi a kullum zaice “in munyi Aure zaki rika dafa mai Abincin da yakeso baya son irin namu na nija zansa akoya miki irin dishes din da yakeso. Abun na bata mamaki ace mutum Abincin mu na nija mai shegen test baya burgeshi sai mara magi? she almost know everything about him by now saboda labarin shi, tasan yana karatu a waje kamar yadda Ahmed yafada mata kawun su ya kaishi waje karatu, Ita kanta so take taga wannan khaleel din da labarin shi baya karewa a bakin Ahmed,. Tana son Ahmed sosai halin shi, yanayin natsuwar shi ya banbanta da na samarin zamani masu burin cakumar mace da sunfara soyayya……..
Wannan shine D’an takaitaccen labarin Naziya da Ahmed.

A hanyar su ta dawo wa daga sabon titi yake bashi labarin komai na su Naziya tareda fadamai boye mata kudin da yayi saboda batason mai kudi y’anda ta nuna mai. Khaleel yasamu kanshi da yin dariya, ” she is funny wace mace ce batason hutu da kudi in this era? ” my Naziya wants a simple life ba a ginata akan greedness ba, all this kyale kyalen duniya basa burgeta do you know nasha siya mata gifts in ajiye domin gudun matsala ko fushin ta, do you know tun zaman mu bata taba demanding tana bukatar wani Abu a wurina ba, “she is such a diamond in the rocks, she is different khaleel my Naziya is perfect I told you. “Hmmm Allah yasa tana sonka like you love her? “She do Insha Allahu, koda baikai wanda nake mata ba nasan tana sona,
Karar wayar khaleel yasa yace “my God this witch. Yafada yana cutting call din. “Fauzy right? “Yes yaya ta cika naci bana son mace mai naci. “Hhhhh you are lucky khaleel fauzy batada laifi and secondly irinta mommy keso Y’ar gidan wasu kaga babanta ne minister na kudi, don haka bakada matsalar mommy kabada kai musha biki bayan nawa. “Yaya why ake Aure? “Hhhh khaleel saboda Aure sunnah ce mai karfi, sannan ba Abinda ke karawa namiji mutunci irin Aure, ga kuma samun natsuwa da soyayya idan kayi dace. “Yaya I don’t need any natsuwa a wurin mace ni. “Ah bakada lafiya ne? “Kalau nake kawai bana jin akwai macen da zatasa inji ni a namiji sai kawai in lafiyata ta motsa,. “You are wrong khaleel, kana samun macen da kakeso manhood dinka yadaina kwanciya cikin sauki, domin the moment you fall in love, zaka ji duk duniya ba Abinda kakeso sai kasamu kwanciyar hankali da farin cikin zuciyar ka, you are my younger brother but bazan boye maka ba na matsu ba a daura min Aure da Naziya ba am eager to have her ban taba jin lafiya ta tana aiki ba saida na hadu da ita, don haka kaima duk ranarda ka afka soyayyar wata zaka gano komai. Dariya kawai yayi domin shi yasan lokacin da kawai yake samun erection sai inya tashi a bacci yake sanin he is healthy ba wata Y’ar macen dake daga mai hankali domin bai sawa ranshi ba ma bare Abun duniya ya dame shi.

Cikin unguwar suka nufa wadda tuni yaji wani iri musamman irin kofar gidan dayaga sun tsaya Almajirai birjik sunata karatu ga hasken farin wata daya dallare KO Ina fiyeda hasken lantarkin dake wurin, wayar shi ya daga tareda danna number ta, ba bata lokaci ta daga hade da yin sallama, “Gimbiya kifito ku gaisa da heartbeat tare muke dashi.
Cikin murna ta mike tace “gani nan zuwa yanzu inga wannan kanin namu.
Yana kishingide ko motsi baiyi ba impact bayajin zai iya fitoda takalmin shi wajen wannan unguwar, dole momy tayi spark ai, don ma batazo tagani ba ma da in sama da kasa zata hade ba Yarda zatayi ba yasani.
Fitowa tayi cikin natsuwar ta sanye da hijabin ta, ta karaso jikin motar dayake tsaye nad’e da hannu, ya zubawa kofar gidan idanu har ta karaso kusa ta d’an tsaya nesa kadan kanta akasa ta gaida shi, “Ina wuni. “Lafiya kalau gimbiya ya kike? “Alhamdulillah, cikin muryar ta mai cikeda natsuwa, kwankwasa glass din motar yayi, ya sauke a natse tareda gyara zaman da yayi kamar wani sarki, kamshin shi mai matukar tsada ya huro tareda muryar shi mai cikeda wasu irin sirrika suka sakata dago kai cikin sauri,
A cikin kyawawan idanun shi nata yasauka domin hasken motar na haskashi dakyau, wani irin sanyi jikin ta yayi Mata domin Sam baiyi Kama da sunan kanin Ahmed ba a wurin ta saidai Yaya, irin cika motar da yayi da kwarjinin shi tareda kamshi da cikar haibar shi, kallo daya ta sauke idanun ta akanshi Wanda tsab da ita gwanace ya isa ta Zane hoton shi, daga ganin shi bazaiyi yawan magana ba, kuma zaiyi miskilanci sosai. Tunanin ta ya katse ne lokacin da taji saukar muryar shi a cikin kunnen ta “Yayana naga Auntyn zamu iya tafiya ko? Shine kalmar data fito kawai batareda gaisuwa ko wani dogon zance ba. Ta shirya sakewa dashi domin karo dankon soyayyar ta a zuciyar Ahmed, amma is impossible yanzu don taki jinin girman kai da nuna isa just because yaje waje karatu, tuni taji yafita a ranta takuma daura damarar Kama kanta da Al amarin shi koda ta shiga gidan nasu,. Saida Ahmed ya leka kanshi tareda zuba mai ido “come on brother kafito mana ku gaisa da kyau, “no mungaisa daga nan ka sallameta mutafi nagaji kasan bangama hutawa ba, yafada a mugun kagare yake subar wurin yanajin warin Almajirai daga inda yake Idan yakara more minutes a wurin he will surely vomit,. Ya lura da yanayin shi don haka a gurguje ya sallameta ta tafi tana mai jin takaicin wannan khaleel din,.
Yana tada motar yace “Yaya wannan Y’ar yarinyar zaka Aura? Why?? she is too young for you please, fuskar shi a kwabe, “hhhhh she is perfect banason Auren katuwar mace ko over twenty nafison irinta mutum ya mori kuruciyar ta yafi Amma Idan ka Auri wayayyun mata bazaka mori komai ba, nafison innocent girl da zankoya wa komai,. “Hmmm zakasha aiki wallahi ai wahala zakayi kafin wannan ta iya daukar ka, kuma Yaya iyayen ta suka yarda suyi mata Aure? “Yes saboda mu anan takai Aure tunda ta kammala secondary,.
“What? Yaya this is too much, da Ina nan bazan bari kafara sonta sosai ba gaskiya. “You are too late now, domin inaji a jikina Idan ban Auri Naziya ba zaku iya rasani so ku tayani Addu’a kawai Ina son ta fiyeda tunanin ka nasan you will always support my back. “Of cos brother Insha Allah.

Karfe goma suka isa unguwar su, Wanda mommy Saida taci gaba da fada “kunje ghetto Area ko nasani saiya jamun kai, ka wuce kayi wanka kazo kuci Abinci kaima wuce ka watsa wainnan kayan dustbin kafin ka dawo falon nan kajini ko? Wucewa yayi cikin sanyin jiki ya tafi dakin shi Yana mai jin bakin cikin halin na momyn shi, kasa fitowa yayi saboda rashin jin dadin Abun, shima khaleel kasa cin komai yayi ya kalli momyn dake kan korafi “mommy why please? Ki yi hakuri Ki daina fada akan abunda dole za ayi. “Yes za ayi Amma ni Balkisu bazan bari ya cakuda min iri da na talakawa ba mu zuba tunda dangin ubanku sun nuna sunfini iko akan shi ni kuma zan nuna musu sai naso komai ketafiya mu zuba nida su.
“Momy ji nake kamar in koma bangkok kawai domin bazan iya tsayawa inga d’an uwa na a damuwa ba, please Ki barshi ya samu natsuwa mana. “Khaleel, kana ganin uwa zataki d’an tane? Ina son Ahmed kamar yanda nake sonka saidai bazan iya kawar da idona akan kwashi kwaram din da zai debo min ba.
Mikewa yayi kawai cikin fushi yabar mata Abincin yayi dakin yayan nashi, a kwance yake Yana tunani, dafashi yayi, dagowa yayi tareda rungume Khaleel din, “brother am worried, bansan irin zaman da zamuyi da Naziya a gidan nan ba, bana so injefa Y’ar mutane a damuwa bayan an bani amanar ta. Bubbuga bayan shi yayi “karka damu Ina nan zan taimaka maka ba Abunda zai samu baby doll dinka. Yafada cikeda dariyar tsokana domin ya kwantar da hankalin d’an uwan nashi,
Shigowa tayi dauke da tray tana fara’a domin taga Alamar Idan tayi sake yaran nata zasu juya mata baya akan zancen Auren nan, Wanda bazata taba Yarda da hakan ba,

“Toh yaran momy ga Abincin nakawo muku ni na damu kuci, kashin awaki, ta ajiye a tsakiyar gadon tareda jansu da hira kamar zata mayarda su ciki, tuni suka ware suka kwashi deshes din, tana cewa “bayan rasuwar mahaifin ku nayi iya bakin kokari na ganin bakuyi maraici ba, Alhamdulillahi yau dukan ku kunkai matasa Abun Alfahari a wurina, forgive your mother Ahmed na dauki buri mai girma akan ku naso nice zanyi maku zabin matan da suka dace daku Amma ka watsa mun duk shirina Ahmed. “Am sorry momy, kuma nayi miki Alkwarin zaki samu Naziya a duk yanda kikeso bazakiyi dakin sani ba yarinyace mai tarbiya da kin Amince da tuni nakawo miki ita ma kingan ta. “Aa tunda ansa rana ai lokacin zaizo don haka basai ka kawo taba, bakomai zan cika burina akan khaleel. “No mommy khaleel ma yanada tashi zabin ai, yafada Yana kashe mai ido, “no no no bana sonta Yaya please meye haka she is my mate fa tare muka kammala karatu why zaka ce Ina sonta ita keso na ni banga Y’ar da zanso ba har yanzu’
Wani irin dadi mommy taji ganin khaleel bazai juyuba a wurin mace tunda ita keso shi bayaso ai irinta takeso, “wow Auta na wacece wannan yarinyar? “Mommy Y’ar gidan minister kudin Nigeria ce, “what? Tafada tana dafe kirji, “Y’ar gidan mai nasara kake fada? Oh my god khaleel, ta rungume shi, that’s my son, ka kawomin ita kaji kace tazo inganta Amma ka gama wanke min zuciya d’an nan. Tafada tana mikewa bari inkira Auntyn ku infada mata tafara shirya mana babbar harka ta Fita tana danna kiran kanwar tata mai ra’ayi irin nata. Binta sukayi da kallo suna mugun mamakin halin na mommy, sai kace wadda bata jiku da kudi ba, kullum she is hungry for more, kallon Ahmed yayi da fuskar tausayi yace “why zaka fada mata Yaya kasan am not ready, kuma yanzu tunda taji bazata taba bari insha ruwa in Ajiye cup ba. “Is OK fauzy love you a lot kuma meye laifinta nasan tun lokacin da kuke tare, ya isa haka ka Amince bayan nawa kawai a daure min kai, do you know, Ina mafarkin ganin Auren ka? Ina so inyi witnessing Auren ka inga jinin ka. “Hhh oh come on Yaya kamar wani tsoho na barin wasiyya please tare zamu cika gidan nan da yara, “who know Khaleel? Allah kadai yasan me zai faru gobe, kasan cewa nan gaba kaine zaka rike gidan nan? “Why Yaya? Indai har kana nan bazan taba daukar girma ba saidai in tafiya zakayi dole in rike kana dawowa zanbaka komai domin ka shagwaba ni tuntasowa ta Abu daya nasani shine in saka master card dina inciri duk Abunda nake so ba tareda antanbaye ni me nayi dasu ba, Yaya nasan kudin da daddy yabari bawai haihuwa sukeyi da kansu ba kaine kakara habaka su har suka kai haka kaine jigon gidan nan bazan taba iya Abinda kakeyi ba…… “Shhhhhh zakayi Idan bana nan fiye ma da Wanda zanyi saboda I believe kai jarumi ne kafini iya tafiyar da Rayuwa. “Enough of this discussion kana sani a damuwa. “OK now kakira fauzy kafara bata kulawa domin tunda zancen yaje kunnen mommy ba fashi, yafada Yana dariya,.

Fita yayi daga dakin yayan nashi yanajin wani iri “Aure? Gaskiya bai shirya ba infact zaiyi ne saboda yayanshi ya insisting kuma koda baison Abu Idan yayan shi na sonshi dole shima ya soshi, Allah kadai yasan iyakar soyayyar da yake wa d’an uwan nashi, kwanciya yayi a kujera a dakin nashi Yana mai runtse idanun shi, so yake ya tuna komai na fauzy da quality’s dinta just for Ahmed, Amma first thing da yafado mai a rai yasa ya zabura tareda girgiza kai, “no no no why her?
Cikin Sauri ya dauki wayar shi domin ya k’aryata tunanin shi, fauzy ya Kira, kamar mai gadin wayar ta ta dauka jikin ta na rawa “oh my goodness darling you call me? Tafada tareda Sanya kukan farin ciki, tundazu take kiranshi yaki dagawa har wani zazzabi takeji saboda damuwa tana yimai wani irin so mara misali. Tun isowar ta ake tarairayar ta Amma duk natsuwar ta bata tare da ita,
“Yes I call. Yafada Yana gyara zaman shi domin baisan ma mai zaice ba kuma. “Tank you darling for calling, please Ina so inganka kasan is hard for me kwana daya bansaka a idoba I can’t. “Is OK zaki iya zuwa gidan mu gobe yanzu dare yayi. “OK am coming tomorrow tank you darling. Tafada tana buga tsalle tareda rungume filo, tasan yafara damuwa da ita tunda har yake so taje gidan su yanzu, hakurin ta ya fara aiki yanzu. Kwanciya tayi tareda Addu’ar gari yawaye ta ganta agidan su.

 

Gefen Naziya ta shiga gida da takaicin khaleel, domin yaron mugun d’an wulakanci ne, inba wai gizo idanun ta ke mata ba kamar kallon kyama yake mata, bayan duk unguwar su an shaida tsabtar su, duk da suna fama da Almajirai Inna kulu nada kokarin ganin ta tsabtace gidanta sosai,. Kwance take tana juyi shukrah ta matso gefen ta akan Y’ar madai daiciyar katifar tasu, tace “Aunty lafiya? “Hmm bakomai. “Aa Ina kallon yanda kike ta juyi tundazu kinkasa bacci, meke faruwa ne? “Kawai Ina tunanin yanda zan zauna da Ahmed ne tareda kanin shi shukrah dazu sunzo, baida k’irki irin Ahmed ya cika girman kai da nuna shiyayi karatu a kasar waje. “Ni kuwa Aunty kallon Arziki sosai nakeyiwa Yaya Ahmed fa. “No yafada min Yana da ubangida mai kirkine watarana motocin yake zuwa dasu, “nidai Aunty Ina tantama domin ko tsarin jikinshi ya isa ya nuna Yana cikin hutu. “Ni kuma me zakice dani? Tunda kowa kallon Y’ar masu kudi yakemin a school ko in munfita, halitta ce kawai. “Hmm tom kiyi bacci Ki kyale wani kanin shi Bashi zaki Aura ba.

 

Washe gari Karfe goma tayi mata a gidan su khaleel cikin tangamemiyar motar ta ta yayi, da kanta ta tuko kanta, da taimakon shi ta zo gidan domin unguwar su ba boyayya bace, momy ta zage sai rawar kafa takeyi an shirya mata tarba Kala Kala, cikin adon jan material doguwar Riga dinkin yayi na yayan masu daula, taci gwala gwalai wuya da hannayen ta tana zabga sheki da kamshi. Ta hadu ba sauki domin ta iya caba ado. Tasamu tarba gefen momy, Wanda koda tazo gidan bai tashi baccin safe ba,
Momy sai Ina ta saka Ina ta Ajiye takeyi da ita, sai zare idanun ta takeyi taga inda zai bullo. “Huh khaleel na bacci haryanzu bai tashi ba, kinsan da gajiya a jikin shi.
Shigowar Ahmed ne yasa Momy tace “ka duba d’an uwan ka ko ya tashi ga bakuwar ta iso. Gaisawa sukayi Yana Kara ganin wayewar ta da kudi Wanda yasan ba yanda za ayi Naziya tazo gidan nan saboda shi, banbancin yayan talaka kuma y’an gidan mutunci kenan da kuma ya’yan masu kudi. Yanzu meye Abun burgewa a nan mace ta nuna rawar kafa akan namiji, idanun fauzy ya gama budewa gaskiya and zasuyi kusan sa’a da Khaleel like he said, wucewa yayi Yana daya sanin bashi goyon baya akanta,.
A kwance ya sameshi Yana kallon saman pop, “oh you wake up? So kazo fauzy is here. “You see tunda Asuba mayyar ta tanbayeni address nafada mata don uwar ta a gidan mu zata karya? Dariya Ahmed yayi, “Auzubillahi yada zagi? “That’s why Yaya bana sonta wallahi batada kamun kai Sam ace Karfe goma ta zo wurin saurayi saikace ba iyayen ta a gidan. “Yanzu dai katashi kayi fresh up kafito tana jira mother in law dinta ta bata big welcome. Tashi yayi ya shige bathroom, like Always Saida ya kwashe hour guda kafin ya fito Wanda shirin nashi ma Saida ya kwashi rabin hour cikin guntayen kayan nashi kamar yanda ya saba.
Cikin takun kasaita da shan kamshi ya fito falon, fuskar shi Sam ba fara’a, “ga shinan yaron kirki ya fito. Mommy Tafada tana mikewa tareda taroshi kamar wani kwai jitake kamar ta goyashi saboda so, jikin fauzy na rawa tace “hy darling kamar ta ruga ta rungume shi takeji. “Tashi kuje dakin shi zakufi sakewa bari insa a hado muku breakfast akawo ciki. Cikin sakewa tace “Saidai baby ni ai mommy kin cika min ciki tun zuwana kike duramin ciye ciye, Tafada tana Dariya, “Allah Y’ar nan, to bakomai ai gidan kune nan.
Zama yayi a falon fuskar shi a cakude yace “ke iyayen Ki basa gidane kika fito early morning? Kallon fuskar shi tayi tareda yin murmushi duk da tasan maganar banza yafada mata ranta bai baci ba, “mommy na nan dady na nan kuma sun san inda naje. “Really? Kuma basuyi kokarin hanaki ba? “Why zasu Hanani? Bayan su masu goyon baya na ne akan duk Abinda nakeso kasan cewa sun san komai akan ka dady na a shirye yake da katuro neman Aure na, please khaleel ka cika mun burina I promise zaka sameni yanda kakeso zan share maka damuwar ka duka zanbaka gatan da mata basa iya bawa mazajen su just give me chance.
“OK zanturo tunda mommy ta Amince dake and my brother too yanzu kije gida zanturo. Tsalle ta buga tareda Dane shi ta rungume shi kam” don Allah da gaske zaka tura? Oh my god khaleel zanyi suman dadi yau. Tafada tana share hawaye, ban bare ta yayi a jikin shi ya ce “oh come on a gidan surukai kike fa behave yourself.
“Farin ciki ne yamun yawa baby muje mota indakko wa momy tsarabar ta please, Tafada tana riko hannun shi, jinta takeyi kamar anyi mata bushara da gidan Aljannah……. 🖊

 

 

*Matar Soja*
10/20/21, 7:33 AM – Fiddausi Yunus: 🌻🌻 *AUREN GADO* 🌻🌻

 

*Matar soja ce*

 

Daga marubuciyar
KUSKURE NA
BARIKI AUREN SOJA
MUK’ADDARI
WANAKE AURE
ZANYI BIYAYYA
And now AUREN GADO,

🆓 page

 

Back to top button