Dalibina Hausa NovelHausa Novels

Dalibina 55-56

Sponsored Links

Littafina na kudine sister please in kina son karantawa 300regular vip 600 via
2378022567
Aisha Mohammed
Zeinith bnk

Dan girman Allah karki karanta min littafi in Baki biya ba

5️⃣5️⃣⏏️5️⃣6️⃣

Bismillahir Rahmanir Rahim

Tace”kin Gama shiryawar ga mijinki ya turo a kaiki gidanki jibi zai dawo

Yace”eh na Gama

Yar aiki ta fitar da akwatinta zuwa mota Saida taje ta sallami general ya Bata makudan kudade tare da Mata nasiha a gurguje Dan shima sauri yake tafiya zaiyi

Godiya tayi sosai sanan ta fito wani soja ya kaita gidanta

Ta tarar da yan aiki guda biyu a falo ta tsaya tana kallon gidan komai ya birgeta lami Yar aikinta tace”hajiya akwai abinda za ayi Miki ne?”

Wani kuka ne ya kwace Mata lami ta rude tace”hajiya Dan Allah kiyi hakuri in har na fad’a abinda be Miki Dadi ba”

Girgiza Kai kawai tayi tace”tafi Zan Nike ki”

Jikin lami yayi sanyi tace”toh hajiya “ta kicin ta fita dan a boysq suke zama kuka sosai miss Fatima ta Sha Wai a ce duk girman gidan nan nata ne hamdala takeyiwa ubangiji daya kawo Mata wanan ranan a lokacin da batayi zato ba ta dade zaune a falo sanan ta mike ta hau sama tana bin ko wani d’aki da kallo har fadawa take a gadajen ko wani d’aki kamar wata yariya zuwa 4pn ta shiga kicin ta girka indomie lafiyayya ta zauna ta ci tana cikin wanke kayan data Bata sai ga lami ta shigo tace”hajiya da kin barshi zanyi”

Ta dubeta fuskarta da walwala tace”no karki damu kunci abinci?”

Lami tace”eh akwai kayan abinci a bagaren mu”

Tace”ok jeki ki huta in Ina bukatar services d’inki Zan kiraki”

Lami tace”tou hajiya “tana gamawa ta haura sama ta kwanta a bedroom dinta bacci me nauyi ya d’auketa Bata tashi ba sai 6:30 toilet taje tayi alwala ta fito ta zauna tana jira a tada sallah dan duk sai taji gidan is bored for her

Tana idar da sallah ta jawo wayarta ta gan tarin missedcalls dinsa dana khadeejaht shi ta Fara Kira sun dade suna waya suna gamawa ta Kira khadeejaht

Washe gari’ Baki Yan danginsu suke ta zuwa dadin Abu mummy nata turo da abinci Amma still Saida tayi girki da ita da lami da talatu

Yau kwanarta biyu da tarewa a gidan yau Kuma hydar zai dawo

Tun safe suke aiki da su talatu an kwashe su bedsheet ta zuba wasu a kobwani d’aki

Ko Ina kamshi ke tashi anyi girki kala uku ciki harda sakwara

Khadeejaht tace”toh ki kwantar da hankalinki mana”

Ta dubi khadeejaht tana goga turare a jiki Daman gashi anci ado cikin Riga da skirt na lace ga dauri ya zauna tace”bazaki Gane ba yaufa shine ranan farko da zamu kasance dashi I want everything to be perfect ”

Khadeejaht tace”ai ko komai yayi ni Zan tafi be kamata ya dawo ya sameni anan ba”

Godiya tayiwa khadeejaht sosai ta Rakata tana dawowa ya kirata ya sauka

Tace”ko na taho airport ne na daukeka”

Yace”nah general ya turo driver ”

Tace”ok”lami ta Kira tace”lami gidan na kamshi inda ya kamata kuwa ko mu Kara turare ne?”

Lami tace”ah’ah hajiya ai sai ya hau Masa Kai”

Tace”ku fad’a min gaskiya nayi kyau kuwa?”

Lami tace”sosai ma hajiya Baki ganki bane Kamar balarabiya ”

Tace”da gaske”

Su lami Suka kalli juna da talatu sukayi murmushi

Saida ya Fara biyawa gida ya tattara muhimman abubuwansa ya tafi ganin mummy”

Bàyan sun gaisa tace”yau dai za ayi daru”

Yace”mummy na shiryawa yakin”

Tace”Allah ya bada sa_a

Yace”Amin “saina kiraki ”

Tace”yauwa keep me updated ”

Yana fitowa ya shige mota Dan dama a shirye yake cikin wani off white shadda dinkin zamani sai kamshi yake

Tana Jin shigowar motorcin ta mike su lami Suka fita ta kofar kicin suna murmushi hajiyarsu

Bude kofa tayi tana kallonsu ta gan hydar ya fito tana ta sa Ido ta gan aliyu sai ta gan bashi

Ta Kai minti biyu ta zubawa inda yake tsaye Ido sai kawai tayi tsaki ta koma ciki Dan ta Gama yarda hydar d’an uwasu aliyune

Juyawa Baya tayi Dan taji haushi da ba aliyu bane ta d’au waya ta bawa kofa baya tana Kiran aliyu sai taji waya na ringing a bayanta tana kokarin juyowa taji an rungumeta an

Afuwan please uzurine ya rikeni

Maman Nur

Back to top button