Hausa NovelsYar Zaman Wanka Hausa Novel

Yar Zaman Wanka 10

Sponsored Links

️1️⃣0️⃣

Last page

Wannan littafin kuɗi ne 300
Za a tura ta wannan accaunt ɗin Fa’iza Abubakar 0020281885 Unity bank shaidar biya ta wannan no 09030283375 Ƴan Niger su tuntuɓi wannan no +22785885134

 

“`MALAM“`

Sai da aka yi sallar isha’i sannan ya shigo gidan dan tuwansa ma ƙofar gidan aka kai masa inda suke cin abinci shi da abokansa. Cikin gidan ya nufo bayan almajirai sun shigo masa da tabarma da butarsa cikin gidan dan dama yanzu basu da wasu yara a gidan sai almajirai. Duk an aurar da matan suna gidajensu haka ma mazan babu wani ƙaramin yaro yanzu. Sallama ya rinƙa kwalawa daga tsakar gidan Tasalla da ke cikin ɗakinta ta amsa masa dan yanzu dakyar ta daure ta ci tuwo kaɗan shi ma dan tana jin yunwa na neman kwantar da ita shi ne ta daure ta ci, amma ko tuwon ta ɗauka za ta sa a baki sai ta ji wani ƙululun takaici a zuciyarta dan tana tunanin Inna Azumi na can birni tana asuwaki da kaza.

Malam kuwa turakarsa ya sanya kai bayan ya ƙwalawa Tasalla kira kyawawa guda uku, haka ta tashi ta nufi ɗakin nasa tana kitsa yadda za ta yi kisisinar da zai barta zuwa birni dan ko sau ɗaya ne dai a rayuwarta ya kamata ta je birni ko da kuwa kwa Inna Azumi za ta tsireta idan ta je. Da sallama t shiga ɗakin ya amsa mata tana shiga ya ce.

“Wai ni Tasalla me yake damunki ne, ya za a yi ki bar ɗakin nan babu garwashi kin san dai ja fi so a kawu wuta ɗaki kafin in shigo gida ɗakin ya ɗau ɗimi” Ya faɗa yana kallonta.

Shiru Tasalla ta yi dan ita gabaɗaya ma yau ta manta da zancen kaiwa wutar ɗakin na Malam.

“Wallahi Malam sha’afa na yi ka san yau da gobe sai Allah”

“To sai ki je ki ɗakko yanzu idan baki kashe wutar ba in kuma kin kashe sai ki hura ko dai ki tafi maƙota ki samo” Ya faɗa yana ajiye hiraminsa da ya cire.

” A’a ban kashe ba ma dai cire itacen ne kawai amma akwai garwashi bari in ɗakko maka” Ta faɗa tana ɗaukan ƙaton kaskon wutar Malam ɗin.

Sai da ta ciko shi da garwashi sannan ta dawo ɗakin ta maida ƙofar ta rufe dan dama al’adar Malam ce daga isha’i ta yi yake shigowa gida ya rufe sai kuma gobe in Allah ya sa ana raye. Sai da ya yi shirin kwanciya ya kwanta amma Tasalla tana gaban kaskon nan tana kara hannayenta a jiki tana jin ɗumin wutar.

“Wai kam Tasalla yau duk wani iri nake ganinki ko baki so Azumi ta tafi ba?”

“kai, kai kai, Malam bar faɗa dan Allah, ni da ƴar uwata Azumi abokiyar zamana mai zai sanya na ƙi son tafiyarta”

“Yau ɗin kuma Azumi ce ƴar uwarki Tasalla ko dai kin yi makuwa ne?”.

“Ras nake wallahi, dama ai an ce zo mu zauna zo mu saɓa, amma ai ina ƙaunar Azumi”

Zaune Malam ya tashi da sauri yana ƙarewa Tasalla kallo dan bai taɓa jin hakan ba daga bakinta ko a mafarki.

“Allah sarki ashe akwai ranar da Allah zai nuna min irin hakan nan ɗaya tana yabon ƴar uwarta ku da bakwa jituwa ko da wasa tun daga girmanku har tsufanku amma kuna faɗa sai gashi yau komai zai zama tarihi”

“Yoa ai ka san duk irin makaman yaƙin da mutum ya ɗauka idan ya ajiye nasa kaima ajiyewa kake, wai ɗazu baka ga shigowar Tsahare gidan nan ba?”

“Ni kwa na ga shigowarta dan har gaisawa mun yi”

“Wayyo ashe sai haƙata ba za ta cimma ruwa ba ashe sun gaisa ta faɗa masa me ke tafe da ita” Ta faɗa a zuciyarta a fili kuma ta ce.

“Ashe ma ta faɗa maka saƙon”

“Wane saƙo ai gaisawa kawai muka yi da yake da mutane sai kawai ta shigo ciki”

Wata ɓoyayyar ajiyae zuciya ta sauke jin bata faɗa masa ba dan hakan zai bata dama ta sheƙa ƙaryarta son ranta.

“Saƙon meye?”

“Malam kenan” Ta faɗa tana ɗan sunkuyar da kai alamar tana jin nauyinsa da kunyarsa..

“Dan Allah ki faɗa min Tasallata daga ke ba ƙari”

“Yo na nawa kuma an ce da gwauro ya iyali, Azumin kuma fa da ka ƙaromin ko ka ɗauka na manta to ai in maye ya manta uwar ɗa ba zai yu ta manta ba”

“Ni ba na son tone-tone kawai ki faɗa min ko da na ƙaro Azumi ma ai kece babba kuma matsayinki da ban yake a wurina”

Wani irin washe baki Tasalla ta yi daɗi fal ranta masoyinta a yabe ta tare da jaddada yadda take a wurinsa.

“Dama Azumi ce ta baiwa ɗan machine ɗin saƙo ya je gidan Tsahare ya faɗa mata ta je birni sunan jikarta Sadiya, kuma ta zo har gida ta faɗa min mu tafi tare a sha shagali” Ta faɗa tana kallonsa.

Wani irin kallon mamaki yake mata wanda har ya so ya bata tsoro.

“Haba Malam kamar an faɗa maka wani mugun abu”

“Yo ba gwara mugun abu ba da wannan kk ma in ce meye marabar dambe da faɗa, Azumin da za ta tafi ya kuka kwashe da ke a ɗakin nan nawa, me yasa bata gayyaceki ba da bakinta sai bayan ta tafi za ta bada saƙo?”

“Malam kenan kai baka san sauyi ya kan zuwa wa mutuɓ lokaci guda ba, ina ga bayan tafiyarta ta ga dacewar hakan”

“Ko jikina kunne ne ai ba zan yarda ba cewa Azumi za ta gayyaceki sunan jikarta ba”

“To ai gashi nan yanzu ka gani ta aiko har gida ka san dai ba zan zauna in shirga ƙarya ba dan kawai ina so in je birni” Ta faɗa tana sanya hannu ta share hawayen kissar da ta ƙwaƙwulo.

Hakan ya sanya jimkinsa yin sanyi, ya ce.

“Ban ƙi taki ba Tasalla kawai dai abin ne da mamaki wai kiɗa a gidan makoki, amma tun da har ta faɗa babu dalilin da zai sanya na hanaki zuwa ai hakan kamar kawo gyara ne a zamantakewar ku Allah nuna mana”

Wani daɗi ne ya baibaye Tasalla har tana rasa inda za ta sa ranta dan daɗi, cikin murna ta yi kan Malam ta ƙamƙameshi tana ta dariya.

 

“Wayyo kin cukuikuye min wuyan riga Tasalla duk kin shaƙe min wuya, yashe rabon duniya da ayyaraye”

“Wallahi Malam duk daɗi ne ya cika min ciki”

“Daɗin daidaituwarki da sobar zamanki?”

“Daɗin zuwa birni dai” Ta faɗa a ranta a fili kuma ta ce.

“Wallahi kuwa Malam zama lafiya ai ya fi zama ɗan sarki”
“Allah ƙara haɗa kawunanku”

“Amin Malam”

Haka suka kwanta Tasalla ko baccin kirki bata yi ba tana ta tsara yadda komai zai kasance Allah-Allah take gari ya waye ta je ta san ƙaryar da za ta yiwa Tsahare dan ta tafi da ita ranar sunan.

Da gari ya waye Tasalla bayan ta gama komai ta tafi gidan Tsahare ta same ta tana tuyar ƙosan siyarwa nan suka gaisa ta faɗa mata abin da ke tafe da ita kan cewa Malam ya tilasta mata zuwa sunan Sadiya dan a samu maslaha tsakaninsu, duk da Tsahare ta yi mamakin amma sai ta ce mata babu koɓai Allah ya nuna mana ranar, tun da dai ta san da kuɗinta za ta yi kuɗin mota kuma sauran diramar ta sha kallo tsakaninta da Azumi dan ta san ba za a kwashe ƙalaw ba muddin Azumi ta ga Tasalla a gidan sunan da ba ta gayyaceta ba dan lo lokacin bikin Sadiyar cewa ta yi babu inda Tasalla za ta je bare kuma suna.Haka ta baro gidan Tsahare ranta fari ƙal.

Wannna kenan.

 

 

“`MAMA“`

Da asuba bayan sun idar da sallah sun yi azkar sai Ashrof ta shiga gyara gidan da yake yanzu bata zuwa makaranta sai islamiya da yake ta kammala secondry school kuma bata cigaba ba da karatu da yake ƙa’idar babansu ce tun kan ya rasu cewar babu wacce za ta cigaba da karatun sai dai in ta yi aure ta cigaba a ɗakin mijinta. Ko Sadiya ma tana kamamala secondry school aka mata aure. Bayan ta kammala komai suka karya ta yi wanka ta shirya sai Mama ta ce ta bari sai kamar ƙarfe tara sai ta tafi dan kar ta yi musu sakko.

 

“`Hajiya“`

Tana idar da sallah ita ma ta shiga hada hadar gyara gidanta da yake wuni biyu kennan bata zauna ba dan haka gidan yana buƙatar gyara sosai dan haka ta shiga gyarawa a ranta tana ta tunanin yadda Imran da Inna suka kwana ko ya aka ƙarshe.

 

“`INNA“`

Rawar sanyi ta fara tamkar wacce masassara ta yiwa mugun kamu, ta shiga wani irin tashin hankali da ya sanya ta kasa gane ina mafitarsa take, so take ta je ta buga ƙofar tare da roƙon Imran ya fiddota dan ta san matsawar ta ƙara wasu lokuta tare da Hassan a ɗakin to tabbas babu abin da zai hana ta suma in ma bata yi gawa ba. A tsaye take amma kuma ƙafafunta sai rawa suke kallon Hassan take da ke kwance kan shawul gaba ɗaya ya gama sawaya daga mutum zuwa miciji kan sa ne kaɗai na mutum amma dai yana a inda aka ajiye shi ko yunƙurin motsawa bai yi ba.

Ganin yadda Hassan ya mata shamaki da zuwa wurin ƙofa hakan ya sanya ta yanke shawarar neman ɗaukin Imran duk da ta san da gayya ya rufe ta amma ya zame mata farilla tusa a masallaci ta nemi ya buɗe ta.

“Imirana, Imirana, dan Allah ka taimaka ka buɗe ni kai ma da ɗan nan ya zame maka dole ka gudu daga ɗakin bare ni ɗorin ɗosano kakar uwarsa” Ta faɗa tana magiya amma shiru kake ji wai malam ya ci shirwa ko motsin Imran ɗin ma bata ji. Amma hakan bai sa ta saduda da neman ɗaukin daga gareshi ba dan haka sai ta ƙara ware murya ta ce.

“Imirana indai mutuwa kake so in yi billahillazi ba sai ka rufe ni da Hassan a ɗakin nan ba lokaci na ma yana tafe zan mutu ba sai ka haɗani da wannan abun ba”

“Inna in kin ga na buɗeki to tabbas sai kin wanki yaron nan, ya zaki yi ki wanki ɗan uwansa amma shi kiƙi masa wanka, sannan bayan haka ma har ki ce wai shi ɗan ruwa ne bayan kin san baiwa ce Allah ya masa, ba ke ce jiya kika ce kar ake raba kan su ba, tun da har Allah ya halicce su a ciki ɗaya? Amma shi ne ke kika fara nuna musu banbanci, baki san ba a yiwa tagwaye haka ba ransu ɓaci yake”

“Haba Imirana ya za ka faɗi haka da bakin ka, son dai ka sanya Hassan ɗin ya min wani abu, ni ban nuna musu banbanci ba, kuma da kake batun ba a nuna musu banbanci ni dai na san ba a ɓata musu rai in ransu ya ɓaci suna ɓatawa mutane abinci ko ayi ta dafa abinci yaƙi dahuwa amma tun da uwata mai daddawa ta haifeni ban taɓa jin inda aka yiwa ɗan mutum baiwar komawa miciji ba”

“Wai wa ya ce miki miciji ne bayansa ne fa kawai fatar ta miciji”

“Ƙur’ani miciji ne, dan baka ga yadda ya koma ba yanzu wallahi kan sa ne kawai na mutum” Inna ta faɗa idanunta a kan Hassan tana sakin kuka dan sai ta ga girman macijin ya yi yawa.

“Ki wankesa sai na buɗeki”

“Wallahi ba zan wankeshi ba, ta ina zan fara wanka wannan abu himili guda wallahi da in wankesa gwara ya kasheni in san mutuwar shahada na yi, ai da uwaka Amina ce ba za ka rufeta a ɗaki ɗaya da maciji ba”

“To zage ni Inna sai in buɗe miki”

“Ni shegiya in ji ɗan daudu ba zan fara ba ma ina so ka buɗe ni ta ina zan fara zaginka ai ko banza ba zan ce maka ba”

“Gashi kwa kin faɗa kn ce banza”

“Sa’adiyya, Sa’adiyya, dan Allah ki fito daga bayin nan, ima dalili kamar wacce za ta koma budurwa in kin yi zaman ruwan zafin, bayan har ƴaƴa biyu sun keto ta gabanki ba yadda za a yi ki koma kamar da, in kuma wanka kike in ba fatar za ki canja ba dan Allah ki zo ki ga halin da Innarki Azumimi take ciki duk na fita hayyaci na…

“Sadiya fa bata jinki kawai ki min abu ɗaya in buɗe ki ya katse mata magiyar da take yiwa Sadiya.

“Me kake so, ko goyaka ka ce in yi Imirana zan goya ka in dai ka fito dani”

“Kin ji matsalar ai, so nake ki kirani da suna na, na asali wato ki ce IMRAN inda kin faɗa to zan buɗeki”

“I,Imir, Imirana” Ta faɗa dakyar dan ta kasa faɗar yadda yake so.

“IMRAN kawai nake so ki ce”

“Haba wnnnn rashin imani har ina tayaya bakin tsohuwa zai iya faɗar wannan abu ban da ɗaukan alhaki wallahi Imirana duk ranar da na fito za ka san ka min wannan wulaƙanci” Ta faɗa tana rushewa da kuka.

“Sai ki bari sai kin fito ɗin, ke ba matar malam bace ki yi addu,a kawai ki kuɓuta”

“To ai mutum ba ya ƙin ta mutane” Cewar Inna.Jin abin da Imran ya ce sai ta tarki yin addu’ar amma ruɗani ya sa ta manta komai, tunani ta shiga yi can sai kawai ta ji wani karatu ya faɗo mata a baki.

“Alif, am baki, waw, zal, ba, alif, baƙi, lallam, hakuri” Ta faɗa da ɗaɗɗaya kamar yadda ta ji almajiran Malam na biyawa da allo. Imran yana kwance rigingine tsabar dariya yana tunani wai dama matar nan akwai maganinta aka bari ta addabi mutane, dariya yake tun ƙarfi can ya ce.

“Am, baki,”

Sai Inna ta karɓa da cewa ‘Waw zal”

Ƙaran dariyar Imran kawai Inna ke ji, hakan ya sanya ta fara neman yadda za ta samu mafita dan ta ga bashi da niyyar taimakonta. Idanunta ta mayar inda Hassan ke kwance aikuwa ta yi arba da gabaɗaya ya koma maciji har kan, idanunta ta zaro ta ce.

“Hassan kai ne ka koma haka,duk da hausawa sun ce kaƙi naka duniya ta so shi, ka so shi duniya ta ƙi shi, to yau dai ga ranar, ni dai na ƙika dama ba wani haɗi garemu ba,Allah tsari gatari da saran shuka, uban gyatumarka kawai na haifa, ni ma ban da shishshigi shiga dangin miji da ganamasgo me ya kaini zuwa ZAMAN WANKA, ya Allah ka raba bawa da wahala gwauro a teburin mai shayi” Tana faɗar haka ya fara ja baya har sai da ta ji ta tokare da jikin drower waigen mafaka ta fara amma bata gani ba, idanunta ne suka sauka a ƙasan gado inda ta kwana jiya kawai sai fashewa da kuka ta yi ta ce.

“Ni Azumi na ga takaina, tun da na zo birnin nan nake yin angamo da abubuwa, na yi angamo da mazaƙutar (Al’aura) abokin Imirana, na yi gamo da aljani cikin dare lokacin da ake cewa mahutar bawa amma haka na kwana a tsakanin katakwaye, sauron duniyar nan ya gama cinye min ƙauri, ga riga a jiƙe duk sanyin nan amma rigar tana naniƙe dani da lema da komai haka na jure na kwanta, yanzu hallaw daga garin Allah ya waye a rufe ni da miciji a ɗaki” Ta faɗa tana jin haushin kan ta da bata fito daga ɗakin ba lokacin da Imran ya karɓi Hassan.

Da sauri ta nufi akwatunan Sadiya da aka musu ɗaya kan ɗaya, guda huɗu ne, hakan ya sa ta hau kan su amma tana iya hango jelar Hassan na kaɗawa tana motsi, da sauri ta diro daga kan akwatuna ta taka gado, ta buɗe drower step ɗin wardrobe ɗin ta kalla ta ce.

“In ka ji mutum na cewa ba zan iya ba to bai kama shi bane, ƙafafunta ta ɗora a kan step ɗin cikin drower ta ƙanƙanme a haka ta yi matakala da step ɗin sai gata ta haye saman drower can saman ta hau kan ta na gab da silin.

“Taimakona ɗaya da Allah ya yi lokacin sanyi ne da ace zafi ake fanka a kunne ai da an yi gudun gara an tadda zago, da fil fanka za ta ɗauke min kai” Ta faɗa tana kallon ƙasa inda Hassan yake har lokacin yana nan a micijinsa.

Sai da ta ji ta zaune dandam, ta sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi ta ce.

“Allah raba bawa da wahala, na san dai komin nisan dare gari zai waye, amma ban da dai matar mutum kabarinsa babu yadda za a yi Halima ta auri wannan yaron marar imani” Ta faɗa tana rafka uban tagumi.

Ƙaran buɗe ƙofar bayi ne ya sanya Imran daina dariyar da yake ya tashi zaune sa sauri ya koma kan kujera ya zauna ya ɗauki Husaini ya riƙe dan ba ya so ko Sadiya ta san gashin ƙumar da zai ke yiwa Inna a gidan dan ya san ko ba komai kakarta ce kuma ba za ta ji daɗi ba.

 

Da sallama Sadiya ta shigo falon, amsa mata Imran ya yi mamaki ta yi da ta ganshi ɗam a zaune fuskarsa fes da alamar yana cikin nishaɗi, mamaki take yi daga jiya zuwa yau Imran ya sauya ya zama mai yawan fara’a kumai magana ba ta masa wahala yanzu, danganta hakan ta yi da ƙaruwar da aka samu.

“Ina Innar?” Tambaya tana kallonsa.

“Tana ciki Hassan take yiwa wanka”

“Ikon Allah shi ne har da rufo ƙofa” Ta faɗa tana sanya hannunta ta tura ƙofar, ashe kafin ta shigo falon Imran ya buɗe mukullin da ya sanya, dan haka ƙofar kawai ta tura ta shiga. Inna da ke saman drower tana jin duk abin da suke cewa, a ranta ta ce

“Lallai Imirana ya cika maƙaryaci, kuma maƙetaci wallahi yau duk abin da za a yi sai na yi jarumta na yi ta maza na rama abin da ya mini” Ta faɗa tana jijjiga kai.

Sadiya da ta shigo idanunta suka sauka a kan Hassan da ke kwance a siffar miciji ya fasa kai kamar zai sara, idanu ta zaro cikin kiɗima ta fara waiwayen inda za da ga Inna dan bata ganta ba kuma tana tunanin kar dai saran Innar ya yi.

“Sa’adiyya kin ganni nan” Inna ta faɗa cikin raɗa-raɗa, ta shaƙe murya kamar wanda aka riƙe mata maƙoshi sai da ta faɗa sai biyu sannan Sadiya ta tsinkayo muryarta ɗaga idanu ta yi ta sauke su a kan Inna da ke kan drower ɗare-ɗare kamar biri ya samu saman bashiya.

“Inna” Ta faɗa tana kallon Innar yadda ta yi wani wujiga-wujiga ta yi sharkaf da gumi kamar wacce ta fito daga filin restiling, sai ka ce ba sanyi ake ba. Amma kuma sai ta ga Inna tana sanya hannu a baki alamar ta yi shiru mamaki ya kama Sadiya sai kuma ta yi tunanin tsabar tsoro ne ya sanya Inna bata so a ɓuga magana saboda micijin, tana ƙoƙarin juyawa ta kira Imran ya zo ya ga abin al’ajabi dan ta lura da yanayinsa bai san abinda ke faruwa ba dan cewa ya yi Innar wanka take yiwa Hassan. Inna ta gani ta ƙanƙame drower ta sanyo ƙafarta cikin drower ta ya fara taka step ɗin drower da ke drower a buɗe take kawai sai gani ta yi Inna ta dirƙo a kan gado da ta faɗo gadon ma har da wata adungure ta yi alkafira sannna ta sauke idanunta a kan micijin nan wani yawu ta haɗiye midik amma duk da hakan bata karaya ba a kan abin da ta yi niyyar yiwa Imran.

Tsaye ta miƙe a kan gadon sai da ta saita yadda za ta tsallake micijin sai kawai ta yi wani tsalle sai gata ta tsallake miciji ta zo kusa da Sadiya da ke bakin ƙofa, tana zuwa bata yi wata -wata ba ta riƙe Sadiya ta ce mata a kunnenta

“Ƙwalawa Imran kira ki ce ya ajiye Husaini ya zo amma kar ki faɗa masa Hassan ya zama maciji dan kar ya razana” Inna ta faɗawa Sadiya hakan cikin raɗa a kunne. Sadiya kuwa da bata gane menene ba sai ta shiga kiran Imran da cewa ya ajiye Husaini sai da ya yi dariya sosai sannan ta taso dan shi duk tunaninsa fatar miciji Inna ke yiwa rangwangwan ɗin wannan.

Yana dai dai shigowa ɗakin Inna ta riƙe hannun Sadiya gam, yana gama shigowa ɗakin kafin idanunsa su kai kan Hassan Inna ta ja Sadiya ta shammaceshi sun fita daga ɗakin, suna fita ta banke ƙofar ta cire mukullin ta sanya a aljihun ɗan tofinta (Siket ɗin da ake ɗinkawa tsoffi suka sanyawa cikin kayan jikinsu) Ta ja zip ɗin ta zige hakan ya yi dai dai da saukar idanun Imran a kan danƙareran miciji da ya fasa kai yana ciccira ido. Wani uban juyawa ya yi tare da yin kukan kura zai gudu yana taɓa ƙofa a jita a rufe. Sadiya kuwa da bata gane abin da Inna ta yi ba sai ta shiga tambayarta dalili nan Inna ta kwashe komai ta faɗa mata.

“Saboda Imirana ya raina ni dan rashin Imani har da cewa in ke addu’a tun da ni matar Malam ce, yo ɗiyar nan ina ma na tuno da wata addu’a kawai dai na ji ina karanto alif, am baki ,waw zal, yo banda ruɗewa da gigicewa ina waɗannan baƙaƴe zansu zama addu’a kai Allah raba bawa da wahala, ji yadda na koma yau ne kika shiga wanka amma azabar da na sha wallahi kamar wata na yi a cikin ɗakin, yadda kika san a cikin rijiyar macizai aka saka ni haka na tsinci kaina cikin fargaba amma Imirana bai tausaya min ba bai dubi tsufana ba ai yau ko sama da ƙasa za su haɗe sai ya ɗanɗani abin da na ɗanɗana dan wallahi ba zan buɗe ba gwara ma ki ja bakin ki ki yi shiru ki toshe kunnuwanki dan ba magiyarki ba zan ji”.

“Sadiya miciji ne fa, Sadiya da ke za a haɗa baki a sanya ni a ɗaki a rufe da miciji”

“Babu mai buɗe ka sai ka masa wanka tas ka shirya shi, ni ma da yake ɗan jikata muka zauna bare kai da ka yi fush ya fito duniya” Inna ta faɗa tana zaunawa a kan kujera Sadiya kuw sai magiya take Inna ta bada mukulli ko ta buɗeshi amma taƙi.

Kuka Imran ya saki ganin micijin ya fara gangarowa daga kan shawul ɗin kamar ma wajensa zai zo. Ya dadage cikin ihu da ɗaga murya yana kuka ya ce.

“Inna dan Allah ki min rai wallahi ban san ya zama miciji ba da na buɗeki duk tunani na a yadda yake a haka yake”.

“Sai ka lissafo min sunayen limaman da suka yi limanci a masallacin makka da madina tun daga wanda suka fara har zuwa na yanzu”

“Haba Inna ya za a yi in iya wannan aiki”

“Ni kuwa ka ce sai na faɗi sunanka ba wanda nake faɗa ba bayan ni ma ba iya na yi ba.

Sai da ya shafe sama da awa guda a ɗakin nan yana kuka da magiya amma Inna bata buɗe ba, sai da ta ga Sadiya na kuka sannan ta haƙura ta buɗe tana buɗewa ta ga Imran a jingine a jikin bango ya yi sharkaf da gumi har da fitsari ma ya yi a wurin, ga macijin ya fasa masa kai a daf a daf suke da shi.

“Imran haka kake manne da bango kamar wani ƙadangare” Inna ta faɗa tana dariya, da gudu ya miƙe har yana neman hankaɗe Inna da ke bakin ƙofa, Inna ta juya ta bishi tana dariya har lokacin yana share hawaye dan bai taɓa shiga mawuyacin hali irin haka ba.

“Imran ka ganka kamar wanda ya fito daga rijiyar maciji”

Banza ya mata , Sadiya kuwa ta ɗanta take ɗakin ta nufa tana zuwa cikin jin tausayin Hassan ɗin ta sanya hannu ta ɗan dungureshi, cikin tsoro dan ta san ko zai cutar da kowa ita ya ɗaga mata ƙafa ko dan kasancewarta mahaifiya a wajensa.Tana dungurinsa kuwa ya kanannaɗe jikinsa sai kuwa ya koma jariri tare da tsallara uban kuka, da sauri ta miƙa hannu ta ɗaukesa tana jijjigashi, ta zauna tana share hawaye ta sanya shi a nono tinɓir da shi ko wando babu da Inna ta masa tsirara za ta masa wanka.

Inna ce fa shigo ganin tana bashi nono ta kama haɓa ta ce

“Lallai uwa da ɗa sai Allah yanzu nono kike baiwa miciji Halima”

“Haba Inna dan yana zama miciji sai na hana shi nono bayan na san ɗan mutum ne, kakarmu ta wajen uwa ta taɓa bamu labarin wacce ta haifi ɗaya mutum ɗaya miciji, kuma ta taɓa cewa wata maƙociyarta ta haifi yan biyu in aka kwamtarsu idan aka zo ɗaukansu sai a ga wani ya zama miciji kuma ta ce da za ave za a cillar da su to sao su koma mutum kuma za a ga sun ji ciwo”
Taɓe baki Inna ta yi ta ce

“Sai ki ajiyewa Amina ko Rakiya in sun zo su masa wankan. Ta faɗa tana fitowa daga ɗakin, tana fita tsakar gida suka yi ido huɗu da Imran yana wani muzurai.

Haka dai Ashrof ta zo ta girka abinci da yin ayyukan gidan, Hajiya ma ta zo Mama kuma sai yamma ta zo. Ƴan uwa da abokan arziƙi da maƙota suka ringa shigowa suna yin barka.

 

“`DARE“`

Kowa ya yi bacci amma Inna idanunta biyu dan gani take kamar aljanin nan ma jiya zai kawo mata ziyara, haka ta matse fitsarinta, can cikin dare ta tashi Sadiya ta ce su yi macanjan bargo ita dai Sadiya bata ce komai ba, dan bata son rikicin Inna kuma ga bacci a idanunta, Inna kuwa ta yi haka ne dan idan aljani ya zo nemanta sai ya ga bargonta a jikin Sadiya wataƙila ba zai yiwa Sadiya komai ba dan ita ƴar gidan ce, ca haka bacci ya yi awon gaba da Inna, da goronta da ta ɓalgata ta gama taunewa ma bata haɗiye ba.

“`IMRAN“`

Gabaɗaya ya kasa bacci burinsa kawai ya ji shi a jikin Sadiya, zuwa can ya yanke shawarar zuwa ya shiga bargon Sadiya ya ɗan sanyata a jikinsa ko ya rage zafi tun da Inna nauyin bacci gareta. Cikin sanɗa ya shigo ɗakin, da wayarsa ya haska ya gansu suna ta bacci, haka ya kashe wayar ya ajiye akan mudubi yana mamakin yau Inna bata munshari. Bargon Sadiya ya ɗaga a hankali ya shige ciki, ya sanya hannu ya rungumota jikinsa, dan bai san Inna bace kawai ya yi amfani da bargo ne dan bai san sun yi canjan bargo ba, bakinsa ya sanya ya haɗe da na Inna da bai san ita bace Inna kuma jin an ruƙunƙumeta da ta falka sai ta yi zaton aljani ne hakan ya sanya ta fara kiciniyar ƙwatar kan ta, Imran bai ankara ba ya ji wani goro a bakinsa mai uban ɗaci, da sauri ya ɗauke bakinsa yana zaro idanu Inna sakin uban ihu ta yi da ta tashi zaune wanda ihun nata ya sanya Sadiya miƙewa zaune , Imran kuwa gefen gado ya samu wani ɗan sukurutu ya laɓe dan ya ana yau ko sama da ƙasa za ta haɗe ba zai fidsa kan sa ba ga goron da ya gogo garin yin kiss ya haɗe masa baki…

 

To fa readers dandandan dan dan dan dan, ga akuya ga kura dan jin yadda za ta kaya ki siya ki karanta dan nishaɗinki ki sha walwala da dariyarki, labarin ZAMAN WANKA yanzu aka fara.

Ku nuna soyayyarku ga marubuciya mmn afrah ta hanyar siyan littafin mai zaman wanka ngd

Dan ƙarin bayani
09030283375

Back to top button