Hausa NovelsNamijin Zuma Hausa Novel

Namijin Zuma 45

Sponsored Links

45…..

*Munada group na kara sani ga matan aure a kan zaman auratayya, and Sex styles, ETC, Sannan zamu koyar da yadda zaki hada magungunanki na mata masu tsafta da kanku a gidajenku, sannan Muna tallata hajarmu ta magungunan mata a ciki, kama daga kan maganin niimah zuwa maganin mallaka, zamu fara lecture a group din Daya ga watan August zamuyi lecture na 3days days, karku bari a baku labari, 3K ne rijister din shiga groups din, matan aure ku hanzarta, zaurawa ku hanzarta, yammata masu Shirin Aure ku hanzarta, uwar gida karki bari amarya tarigaki shiga wannan group din,sannan zakuyi mana tambayoyi ta PC in wata matsalarce daku cikin sirri zamu warware muku abinda ya shige muku duhu. Chart me up only chart pls Banda call 08137747267*

Wani irin mummunan bugu zuciyar nabeelah tayi, seda d’anda ke cikinta ya motsa, Daman kwanan Nan tana yawanjin motsin SOSAI, wasu lokutan har kasa bacci takeyi, ba halin ta kwanta yadda taso, ga nauyin cikin tanaji har cikin kafafuwanta,tako ina cikin ya cika Kuma yasa mata nauyi kafafuwanta duk sun fara tasawa, dukda Bata shiga watan haihuwarta ba,. “Nashiga uku!” nabeelah ta fadi tana sakkowa daga gadon ta a zabure, abinda se a hnkli take sakkowa sbda nauyin ciki Amma yau itace ta sakko da karfi, daga ita se riga mara nauyi doguwa har kasa, yanzu Sam batasan riga me nauyi sbda jin zafi gareta sosai… Ganin yadda ta gigice ta fita hayyacinta, ta tallabo kasan cikinta sbda azababben motsin da yakeyi kmr ze ballo mata mara ya fito sbda tashin hnkli da firgici. “Ki kwantar da hankalinki mommy, ba Wani Abu insha Allahu, in kikasa hijjabi bame gane akwai ciki jikinji insha Allahu…” Aunty hafsat ta fado mata cikin kwantar da hankali. Nabeelah tayi narai-narai da fuska na zallar tashin hankali, ta kasa motsin kirki, ji kake fatt fatt zuciyarta na bugu, ganin batada niyyar motsawa duk tabi ta daburce, aunty Hafsat ta bude drawer ta dubo mata hijjabi zumbulele, ta Mika mata,ta amsa ta saka kalar purple ne dark sosai, har kasan kafafuwanta hijjabin ya kai.. Nabeelah ta kallah uban tulun Cikin nata ta dago ta kalli Aunty hafsat tace “Ana gani kou?” ta fadi Kmr zata fashe da kuka, aunty Hafsat dake kare mata kallo ta girgiza Kai tace “Ba’a gani sosai,,Cikin naki ne tabar kallah yayi girma kamar ba Cikin farko ba, Amma ki dinga wasa da hannunki a Cikin hijjabi , kiyita innalillahi wa’inna ilaihirrajun,insha Allahu Khairan Aunty nabeelah,,,” Nabeelah da zuciyarta keta tsananta bugu tana sauraran Aunty Hafsat ne Kawai Amma gani takeyi kmr dole a gane da ciki jikinta, ga face dinta ma duk ta kumbura. Karasawa tayi drawer dinta Cikin hanzari, ta dakko zani ta daure Cikin sosai wai yadda ze koma ya rage fitowa, Amma Sam ko gezau. Aunty Hafsat ta zaro ido tace “Kai ! Meyasa Zaki tamke cikinki har haka? Wannan aise ki kashe babyn, gaskiya ki kwance mommy, Wlhi bazan iya da haukar Aeezad ba in kika kashe masa baby, ai kwara ko wanne tashin hankali a kan nasa, ni Wlhi nafi tsoronsa a kn hajiya mommy, dande ita nata abun makircine da Kuma ta bayan gida za a biyo maka,,,ki kwance Kawai mommy Addu’ah ta kauda komai, wlhi ubangiji ya gama mana komi, shi muka roka Kuma ze rufa mana asiri…” Aunty Hafsat ta karasa wata zufa na karyo mata goshi dukda uban Sanyin AC dake falon Amma zufa takeyi sbda tunanin irin masifar dake gaba in Hajiya mommy da na’eema suka fahimci cikinnan na jikin nabeelah na Aeezad ne. Aunty Nabeelah data kama Nishi yayinda takeji kmr zatayi amai har bayanta ya dauki zafi sbda daure Cikin da tayi, ji tayi tana neman shidewa Cikin hanzari ta kwance zanin sbda itama bazata jureba, ta canza Wani hijjabi dayafi wannan na jikinta girma, suka nufo kofar fita a dakin zuciyar nabeelah kmr zata fito fili sbda tsabar bugu,.. Riko mata hannu aunty Hafsat tayi bayan sun iso kofar ficewa dakin cikin muryar kwantar da hankali tace “Mommy ki kwantar da hankalinki Dan Allah, ba abinda ze faru, Ina jiyo heart beat dinki in kika nuna tashin hankali za a gane, ki kwantar da hankalin ki dan Allah, ba asan tashin hankali game ciki da Aeezad na nan komi zezo da sauki, ki nutsu pls, kinji…” Aunty Nabeelah ta daga mata Kai alamar toh, amma batajin zata iya kwantar da hankalinta. aunty Hafsat ce ta bude dakin ta fara fitowa nabeelah na biye da ita a baya se wasa take da hannunta Cikin hijjabinta… Hajiya mommy dake zaune kan kujerar 3str ta daura kafa daya kan daya, hand bag dinta na side, se faman karkad’a kafa takeyi tana jijjiga kmr me iskokai, sanye take da jallabiya pink ta yane kanta da dankwalin abayar, hajiya mommy ba mummuna bace, daman normal tanada kyau Kuma ga kyawun hutu, sede bata da hanci, dande akwai gyara ne sosai, Amma tafi na’eema kyau nesa ba kusa ba, Kawai de na’eema tafita yarinta ne a jiki,. Aunty hafsat ta karasa ta zauna kasa, hajiya mommy nata binta da Wani Wawan kallo tace “Kinje kin dade daga kirawomin tsohuwar guzuma, Kai kace na aiki bawa garinsu, Kai yaran yanzu basu da tarbiya Sam Se kayi mgna a gaya maka mgna,,,ni inba ma kaddara ba me zanzo nayi a gidanki,…” Aunty Hafsat ta tabe baki daman ita Sam jininsu be hadu da hajiya mommy ba,tin sadda ta taba zaman gidan kafin tayi aure…. Kan nabeelah na kasa ta karaso ta zauna kasa nesa da hajiya mommy tinda ta shigo falon hajiya mommy ke kallonta, gani take Kmr nabeelah ce Kmr ba ita ba, itade taga tayi wata uwar kiba ne a lokaci kankani, kallon da take mata ya kara sa Nabeelah jin bugun zuciya, murya kasa kasa tace “Ina kwana hajiya mommy….” Ba tare da hajiya mommy ta amsa ba sbda mamaki Daya sake rufeta jin sabon muryar nabeelah dataji sak Cikin mamaki ta kalli Aunty hafsat tace “Hafsat Wannan Kuma yayar nabeelah ce tazo ko kanwarta ce” aunty Hafsat ta kalli Aunty nabeelah wadda kejin Kmr ta mutu Dan tashin hnkli. “Kmrya? Aunty nabeelah ce Hajiya mommy…” Hajiya mommy ta kara bude idanuwanta sosai a kan aunty nabeelah Baki sake tace “Yauni naga ikon Allah? Wannan shine Yar Aiki tafi me gida, itace tayi kiba haka nabeelah de dana sani tsohuwar kilaki, an jima ba’ayi Aure ba mazan waje sun gama cinki sun bar banza,,,a haka Zaki mutu ba aure, sede ki dawwama a bauta kina aikatau kina ciyar da uwarki,,Maza sun gama zurfafa gindin,” aunty Hafsat taji zafin kalaman hajiya momny, a bangaren nabeelah ma taji zafi sosai, Amma sede ta saba da mafiyyin hakan da tana gidanta. Hajiya mommy ta tabe baki, ta jinjina Kai se kallon Nabeelah takeyi tana dawowa ta kalli Aunty Hafsat, tsayar da idanuwanta tayi a kan aunty Hafsat kana tace “Ke Kam kinyi asara Hafsa, yanzu kina gani Wannan kaskantacciyar tayi Wannan kibar..,,aaahhhh gaskiya lefinki ne, taya Zaki bama me aiki sake har haka, harma ki barta tadinga ci tana koshi har tayi kiba, aikin bauta tazoyi ko kuma cin abinci? Ahhh lallai , gashi daman Maza sun riga sun gama fafiketa, ko Ina ya bude a jikinta, duk Wani sassa kullalle mazan waje sun bude sun wangale, Allah wadaran naka ya lalace, uhm Allah de yasa ba mijin Hafsat bane ke cin gindin naki,danke Wannan daga ganinki k’arya ce ke, duk wanda kika samu wangale masa zakiyi yaci, yooo Daman meke baroku daga kasarku inba karuwanci ba, se Kuma in tsautsayi ya fada kun aurarma wata asararriya miji ku mallakesa, shegu Yan dangin asiri , dakun samu namiji nan da nan dakun kaishi gun teacher an wanke muku gindii kunzo kun bashi ya shanye, ku kwace miji ku kwace dangin miji, a haka dai ke zaki mutu ba aure….”

Aunty Hafsat ta kumajin zafi da kalaman da take sukar mommy da ita, ba Kmr ma da take dangan ta ta da zina, zinar ma wai da mijinta, babbar masifar ma data dangan ta ta da shirka, aunty Hafsat bata tabajin ta tsani hajiya mommy ba Kmr yau, ji takeyi inama da yadda xatayi dase ta gayama hajiya mommy kalaman da harta mutu bazata mance dasu ba kilama bakin Cikin kalaman yazama ajalinta ita da yarta, Aunty Hafsat taso ace big hajiya na falon da hajiya mommy baza tayi wannan cin mutuncinba, koda big hajiyar ma ba komi take gareta ba Amma ta tabbatar da tana nan dole ma ta rage Wani abun.Nabeelah de shiru tayi zuciyarta na suya,.
“Aunty Nabeelah ta muku nisan da babu me muryar daze kirata ta iya juyowa,,,” Aunty Hafsat ta fadi hakan a ranta,.hajiya mommy ta kalli dankareren wristwatch din hannunta na zallar zinari, ta karkada kafa, ta kalli Aunty Nabeelah tace ”Kwana biyu karuwancinne ya hanaki kizo duk karshen satin da kk Zuwa kina min aiki? Yar iska, ko karuwancin naki yayi kaurin suna yasa kika dena zuwa gidana? ” Aunty Nabeelah ta girgiza mata Kai alamar a’ah,Hajiya mommy taja kwafa, kana taci gaba dacewa “Yar iska! tin jiya nake kiranki waya kashe har yau waya kashe, ke harkin isa ki kashe waya kina yar aiki kaskantacciya, mara galihu, baki aje ba baki ba d’an daki ajiya ba, to kisani yadda kika sani wahalar zuwa gidannan haka zaki wahala da aikin gidana yau, nace ma
Kar a gyara komi ke Zaki gyara ko Ina a gidannan yau, har sharar tsakar gida yau kece zaki yita, kina karyar bura uba ne, ni nan na fiki tashanci…harni zaki bawa wahala banzar bazara irinki, ke inbadan babban taronnan dazanyi na cikar shagona shekara goma ba, ai baki isa inzo ba, Amma yanzu ma danazo tabbas se jikinki ya gaya miki, yau duk wannan kibar taki ta asara seta zazzage, tashi mu tafi tsinanniya, waya sani ma ko uwarkima zina tayi ta haifeki Yar iska mara uba, dangin karuwai haihuwar ti-ti,,,” ta karashe hadi da mikewa.

Ba karamin zafi Nabeelah taji na kalaman hajiyar mommy ba musamman ma kalmarta ta karshe, seda ta lumshe idanuwanta ta bude, a ranta tana tunanin wai a banza banza ma tana mata wannan zagin ina maga ta fahimci akwai Aure a tsakaninsu da Aeezad mijin yarta, ta tabbatar daga ranar data sani kasheta big hajiya zatayi har lahira,. Ita kanta Aunty Hafsat abun ya mata zafi amma a ranta tasan koda goma ta lalace tafi biyar albarka, balle wannan goman ba lalatacciya bace. Ganin hajiya mommy ta mike yasa aunty nabeelah mikewa, Aunty Hafsat ma ta mike, hajiya mommy ta nufi kofar fita tana fadin “Wuce muje, ki daura tukunyar girki, ammayi wasu girke girken yanzu dai ke Zaki daura wasu , fried rice da jallof rice, se sauran ayyuka…” Nabeelah tace “Toh,,,” a tsorace take gabaki daya, Aunty Hafsat se kallon aunty Nabeelah takeyi Cikin tausayi, tasan yau zata wahala ita da d’an cikinta. Hajiya mommy ta fice a palon, aunty Nabeelah na biye da ita, aunty Hafsat ma ta rakosu har bakin mota.. Bude hand bag hajiya mommy tayi ta zaro kudi dubu daya ta wurgama Nabeelah tana fadin “Kinde san bazan hau mota daya dake ba, kaskantacciya irinki, bana san karnin talauci, ga wannan Kya hau napep ki iso, karki sake in rigaki isa…” Nabeelah ta tsugunna ta dauka,tace “Toh mommy…”aunty Hafsat najin zafin kaskancin nan har cikin ranta, Aunty Nabeelah ta nufa gate aunty Hafsat na kallo tafice ji takeyi kmr ta dakatar da ita daga fita daga gidan, tabbas da Aeezad Na nan da duk hakan bata faru ba, wane mutum,. Driver ya budewa hajiya mommy gidan baya ta shiga yaja motar suka fice a gidan,. aunty Hafsat ta dawo Cikin gidan ta zauna a falo, haka kawai wasu kwallah suka wanke mata idanuwa na zallar tausayin Aunty Nabeelah, ga cikin jikinta, gashi ko Kafin ta fita ti-ti tasamu napep babban aiki ne, zataci tafiya sosai,duk abunnan da akeyi big hajiya bata Sani ba tana can tana baccin asara Kmr kasa.

Da sauri sauri ta ringa tafiya sbda ta isa ti-ti da wuri, ga cikinta se uban motsi yakeyi,tana ta tafiyarta motar hajiya mommy tazo ta wuce fittt,.haka taci gaba da Addu’ah Allah yasa kada hajiya mommy ta rigata isa gida, dukda tasan da wuya hakan. Da sauri sauri ga uban ciki , ba halin tayi gudu da ace babu ciki jikinta da harda gudu zata hada, Amma Ina yanzu ba halin gudu, tafiyarma se a hnkli, ta tallabo kasan cikinta dayayi tsini ta kasa. A haka tayita takawa ta isa ti-ti da kyar, tayi sa’ah tana fitowa titin tasamu napep ta hau bayan ta gaya masa inda ze kaita, ba kowa a napep din, ko ciniki bata tsaya yiba sbda se uban haki takeyi, tana shiga ta jingina bayanta da napep ta kalli kafarta taga harta kuma kumbura ba karamar tafiya tayi ba, Kuma Cikin sauri da takura kai. se nishi takeyi Kawai taji me napep nacewa “Sannu hajiya, dagani kin tafiyu ga juna biyu Kuma jikinki…” Nabeelah ta shiga mamakin ya akayi ya gane akwai juna biyu jikinta, me napep,”ya akayi kasan da ciki jikina?” Nabeelah ta tambayesa Cikin mamaki da tsoro, wai namiji ya gane tanada ciki Ina maga mace, ta tabbatar ko hajiya mommy bata gane yanzu ba dole zata gane nan in taje gidan. Me napep yayi murmushi yace “Ah hajiya ai ciki ba boyeyyen abu bane, tinda na tsaya zan daukeki nagani, inda zaki ba nan zanyi ba amma sbda tausayin Cikin jikinki yasa na daukeki,,,Nima fa inada iyali yarana bakwai nasaba ganin ciki hajiya…” Nabeelah ta sauke ajiyar zuciya ita kadai tasan meke ranta ta kasa cewa komi, kawai se kallon me napep din takeyi, tana jiyo bugun zuciyar babynta a tare da ta-ta zuciyar. Kosawa tayi su isa gidan dame napep din, a kwanar shiga gidan Wani me mota baka Mercedes, yadinga biyo napep din, yazo dai-dai napep din ya zuge glass dinsa kasa, matashine dagani ko Auren fari beyi ba, Kallo daya ta masa ta dauke idanuwanta a kansa, shikam se murmushi yakeyi mata gashi kyakkyawa chocolate color, Amma be Kai Aeezad dinta kyau ba, duk sadda zataga wani namiji ko a film ne Aeezad kawai ke zuwar mata zuciya da idanuwa, data tunasa seta tuna da dadin burarsa in
yana zungura mata ita. Mutunmin yace dame napep din ya tsaya Yanasan mgna da wadda ke Cikin napep din. Me napep na shirin tsayawa tace karya tsaya, dole yabi umarni dukda yaso ya samu kudi sbda yasan inya tsaya dole mutumin ze bashi Wani Abu duba da yadda ya gansa dagani zeyi alheri har me napep yasa ran yasamu ko 5k ce daga gareta
,har suka isa kofar gidan me motar na biye dasu. Nabeelah se mamaki takeyi tana tunanin to koshi bega cikin jikinnata bane yakeso ya tsayar da ita hakan ya tabbatar mata dame napep din nada kallon kwa-kwaf babbar Addu’ar ta Allah yasa ba Maye bane me napep din. Me napep din na tsayawa, tana sauka a napep din me motar ma ya tsaya Yana fadin “Baiwar Allah ni sanki nake da Aure…” Nabeelah ta kalli cikin dake jikinta a cikin hijjabi, tana mamaki ta mikawa me napep din dubu dayar kawai, tafiyar tata batafi ta 700 ba ko a drop ne, wai danma akwai tsadar fuel, Sam ba Wani uban nisa. Nabeelah ta shige gidan da hanzari bayan ta mikawa me napep din kudin se godiya yakeyi ganin ta bashi dubu daya, itade ta shige Nan ta barsu waje shida me napep dayayi tafiyarsa tuni. Me motar Wanda ya jima kofar gidan yana jiran fitowarta kana ya juya ya bar kofar gidan.

Nabeelah na Shiga cikin gidan ta tsaya ta saita kanta sosai a gate din farko ta kara gyara hijjabinta, kana ta nufa cikin gidan se gaisawa sukeyi da masu gadi wadanda da kyar suka ganeta sbda kibar da tayi. Tana isowa packing space taga motar Hajiya mommy seda gabanta ya fadi yau tasan zatasha wulakanci sosai,. Haka jiki a sanyaye ta nufa part din Hajiya mommy bakinta dauke da sallama, ta isa palonta bayan an mata iso se Addu’ah takeyi a ranta kada a gane cikin jikinta. A palon ta tadda naeema zaune ta saki uban jiki, Hajiya mommy ma zaune se faman karkada kafa takeyi Daman jiran isowar nabeelah takeyi, se manyan aminanta guda biyu hajiya naja’atu da hajiya samira, sauran basu karaso ba tukunna, yau babban sha’ani za ayi na cikar babban shagon hajiya mommy shekara goma da budewa. Sai Karfe shida na yamma za a fara. Na’eema da kyar ta iya gane nabeelah wadda ta zube kasan ta fara gaida kowa dake palon harda naeema, wadda keta kallanta tana yatsina fuska kmr taga zawo, Nan da Nan ta hade Rai kmr taga mutuwa, gabaki daya se taji ta Kuma tsanar Nabeelah fin ada ta rasa dalilin hakan, ko amsa gaisuwarta batayi ba. Hajiya mommy ta rufeta da masifa da zagi da tozarci na rashin karasowar da batayi ba da wuri har ta bari ta rigata karasowa. Seda hajiya naja’atu ta bata hkri kana ta sassauta.Nabeelah tabata hkri ta mata banza, ta mike ta nufi hanyar kitchen hajiya mommy tace”Baraka zata nuna miki komi, kar Wanda yasa Miki hannu ke zakiyi duk aikin musammanma girkin Kuma inaso abincina yayi dadih…” Nabeelah ta juyo tace toh Cikin ladabi. Ta nufa kitchen jiki na rawa, ta tadda masu Aiki suka gaggaisa duk nutsuwarta bata jikinta tunani takeyi ta yaya zatayi wannan uban aikin gata da uban hijjabi jikinta. Bata tsaya bata lokaci ba,ta fita kitchen din waje, ta hada wutar itace, tin a nan se nishi kawai takeyi tana motsa kafa da kyar, gashi ba d’an tayi sbda tace kar wanda ya tayata a barta tayi ita kadai, kaf kawayenta sunasan abincin nabeelah shiyasa take zuwa duk satin ta girka in zatayi taro da kawayen nata. Haka ta hada wutar ba karamin wahala tasha ba ga wutar damuna azabar wahala ce da ita,seda tasha fama wutar kafin ta kama, ga hayaki idanuwanta sukayi red sosai, haka ta daure, ta dakko tukunya lamba ashirin ta daura kan wutar , da kyar ta dauko tukunyar, fried rice ta fara daurawa, kana ta sake kunna wata wutar ta daura jallof rice, tana Aikin tana gumi Gashi ba sauri Sbda a takure take ga nauyin cikin ga nauyin hijjabi duk ta gaji kafin aje ko ina,. Inna sadiya dake gefe tana yanka salad Se sannu take mata ba kowa a gurin duk masu aikin sun kama gabansu zuwa nasu ayyukan, Nabeelah ta amsa da yawah. Innah sadiya dayace daga masu dafa abinci a gidan, kawai Taya Nabeelah takeyi yankan salad din ganin ayyukan sun mata yawa,sannan se kallanta takeyi ganin Kmr tanada ciki,DUk yadda Nabeelah ta kaiga fama da hijjabi seda inna sadiya ta gane akwai ciki jikinta abinka da babbar mace, mamaki inna sadiya tashigayi kan yaushe nabeelah tayi aure basu Sani ba?” Haka kawai inna sadiya se taji tausan Nabeelah, ta tashi kawai tasa mata hannu a Aikin, Nabeelah tace ta barshi, inna sadiya tace “Bari in tayaki ba komi insha Allahu…” Aiko Nabeelah taji dadih, Nan inna tasa mata hannu har suka gama Hajiya mommy bata leko ba tana can falon tana fama da baki wanda keta danno kai, tini gida ya cika da mata taf,. Nabeelah da innah suka kammala komi suka gyara kitchen, Nabeelah ta nufa gyaran gidan ita kadai da kyar, take aikin Amma haka seda ta gyara ko Ina,Hajiya mommy tace har tsakar gida ta share, Aiko haka ta share tsakar gidan da kyar, ranar de haka Nan ta wuni tsaye, se aikin azaba takeyi, Nan gidan akasha party , Hall taso tayi abubuwanta Amma Alhaji sunusi ya dinga rokonta kartaje hall da kyar ta yadda,. DUk cukowar gidan babu Dan uwan Hajiya mommy sede bare, bata gayyaci Yan uwanta ba, ko uwarta bata gayyataba, Sbda batasan azo a zubda mata mutumci a cikin manyan mutane, kawai Sbda su talakawa ne, kar suzo su addabi masu kudi da Karnin talauci, acewarta, ita fa Sam ba Wani zuwa ma gidansu takeyi ba, tinda ta auri Alhaji sunusi kimanin shekaru goma Sha biyar bata je gidan iyayensa sau hudu ba, se Alhaji sunusi yayi ta lallashi take zuwa, ko tunawa tayi da yadda gidansu yake da muni da Karnin talauci se taji tashin zuciya,in kaga an Kai Wani Abu Arziki gidansu to daga Alhaji sunusi ne Amma ita kan Ina bata taba aika musu dakomiba, hana karya de sadda ubanta ya kwanta ciwo rai hannun Allah ta aika musu da kudi dubu hamsin, Amma ita ko zuwa batayi ba, sede ta kirasa ta gaidasa sama-sama, harga Allah tinda ta shigo daula bata fatan zuwa cikin karnin talauci,. Sannan bata bawa Wani nata fuskar zuwa nata gidan ba,abinka da uwa, uwarta ta taba zuwa sbda ta ganta kawai, tabi ta hade rai,batade furta abaki ba, sede ta nuna a fuskarta daga ranar Mamanta bata Kuma zuwa ba, sede tanata binta da Adduar shiriya, sbda zuwanta gidan ta fuskanci se yadda tayi da mijin Kuma tasan aikin asiri ne kawai,ita da kanta uwar ta-ta tasan yarta bata da hali,. A wata shekara gidansu ya ruguje, seda Alhaji sunusi yase musu gida Amma ita sede ta bisu da Allah kyauta,ubanta kullum cikin tsine mata yakeyi, danma uwar na tausarsa, ita Sam bazata iya tsine mata ba sede ta bita da Addu’ah kawai. Hajiya Rafi’ah zatama kawayenta hidimar 5m sbda a fita kunya harkar girma da isa, ita a dole ga matar me kudi, ta baza gwala-gwalai a wuya da hannu ayita isa, Amma bazata iyama uwarta da ubanta hidimar 100k ba, duk kusancinta da kawaye bata taba nuna musu gidan su ba sede tace iyayenta sun rasu. har karfe sha-biyu na dare Nabeelah na tsaye da sauran masu Aikin sbda mutane dayawa Nan gidan zasu kwana domin gobe ma akwai wata walimar Za a kira masu kida’ a rakashe,. ba Wanda ya Kai Nabeelah aiki a gidan kaf jikinta ciwo yakeyi sallolin tama seda gaske tasamu tayi sbda aiki, a zaune tayi sallolinta,. Tana Aiki da daddaren tana gyangyadi, Wani mugun bacci tadingaji Wanda bata tabajin irinsa ba, kaf ilahirin jikinta ciwo yakeyi har Wani zazzabi ma ke neman rufeta, Motsin cikinta ma ya ragu, ko abincin kirki bata sawa cikinta ba sede ruwana Sanyi taketasha se ayaba data gani a kitchen taci Sbda duk cikin abincin gidan ba Wanda zata iya ci, jikinta yayi rawa harya gaji, babyn cikinta tin Yana mugun motsi, yazo ya denayi sede tana jiyo motsinsa Dan kadan-kadan.tanata Aiki tana tunanin Aeezad tasan Yana can Yana haukan kiranta, Gashi wayarta kashe take, tasan Yana can ze addabi aunty Hafsat da uban kira,. Basu suka kwanta ba ranar se karfe biyu da Rabi na dare Nabeelah tayi gyangyadi yafi Sau talatin, suna shiga dakinsu na masu aiki, Nabeelah ta kwanta ko wankan batayi ba duk uban gajiyar dake tattare da ita, haka ta kwana da yunwa cikinta ko motsin kirki beyi, sbda rashin abinci, ita har ynzu ta kasa cin komi sede abubuwan da takeci tin su take iya ci, ko kamshin abinci bataso sede dauriya kawai,.

A gidan Aunty Hafsat kuwa, big hajiya na tashi ta tambayi Aunty Hafsat Ina nabeelah sbda tashiga daki bata ganta ba time din Aunty Hafsat na kitchen. Nan Aunty Hafsat ta sanar da big Hajiya kaf abinda ya faru. Aifa nan big hajiya ta dora masifa da bala’i tace meyasa aunty Hafsat bata tasota ba ta nunawa Hajiya mommy iyakarta. Aunty Hafsat ce tadinga bata hakuri kawai ganin big hajiya zata dawo kanta da masifar da bala’in,big hajiya ta rikice tadinga masifar, ta fita zataje gidan Hajiya mommy da kyar aunty Hafsat ta rikota tana bata baki, tadawo da ita falon suka zauna big hajiya de ranar ko abinci ta kasa ci se ruwan masifa takeyi knr yawun bakinta ze kare gashi tayi-tayi Aunty Hafsat ta tashi ta kaita gidan mommy taki sbda inta kaita seta lalata komi gashi abun kan Nabeelah ze dawo, duk fadan da big Hajiya keyi sbda cikin jikin nabeelah takeyi ita tsoronta kar aje a mata asara gashi tasawa ranta wannan cikin na jikin Nabeelah, a kullum se tayi Addu’ah Allah yasa Yan uku ne. Har dare nabeelah bata dawo ba, ga fadan big hajiya ga uban kira Aeezad na mata, sede ta masa karya tace kawai bacci Nabeelah ketayi yau sbda in ciki ya kusa shiga watansa bacci mace keyi sosai…” Itace karyar da Aunty Hafsat tayima Aeezad, Aeezad yace okay Amma badan hnklinsa ya kwanta ba daren ranar de gaza bacci Yayi sbda beji abar kaunarsa ba da Kuma ajiyar cikinsa dake jikinta. Big hajiya kanta duk mugun baccinta batayi bacci ba ranar, aunty Hafsat ma dake part din baban Noor gaza bacci tayi zuciyarta na kan tunanin ya nabeelah take da cikin jikinta? Jikinta ma kawai bata yakeyi asiri ya tonu. Seda baban Noor ya tambayeta meya hanata bacci tace masa ciwon kaine kawai. Daren ranar a bangaren Aeezad Da aunty Hafsat da big Hajiya bacci sede barawo, shi Aeezad Kam duk kwarewar satar bacci beyi galaba a kansa ba.

Manage ba editing.

 

This book is 1k 08101626484.
NAMIJIN ZUMA

Back to top button